< UGenesisi 25 >

1 UAbrahama wasebuya wathatha umfazi, lebizo lakhe linguKetura.
Ibrahim ya auro wata mace, mai suna Ketura.
2 Wasemzalela uZimrani loJokishani loMedani loMidiyani loIshibaki loShuwa.
Ta haifa masa Zimran, Yokshan, Medan, Midiyan, Ishbak da Shuwa.
3 UJokishani wasezala uShebha loDedani. Lamadodana kaDedani ayengamaAshuri lamaLetushi lamaLewumi.
Yokshan shi ne mahaifin Sheba da Dedan. Zuriyar Dedan su ne mutanen Ashur, da mutanen Letush, da kuma mutanen Lewummin.
4 Njalo amadodana kaMidiyani ayengoEfa loEferi loHanoki loAbida loElidaha. Wonke la ngamadodana kaKetura.
’Ya’yan Midiyan maza su ne, Efa, Efer, Hanok, Abida, da kuma Elda’a. Dukan waɗannan zuriyar Ketura ce.
5 UAbrahama wasemupha uIsaka konke ayelakho.
Ibrahim ya bar wa Ishaku kome da ya mallaka.
6 Kodwa kumadodana abafazi abancane uAbrahama ayelabo uAbrahama wanika izipho; wawasusa kuIsaka indodana yakhe, esaphila, wawathuma empumalanga elizweni lempumalanga.
Amma yayinda Ibrahim yake da rai, ya ba wa’ya’yan ƙwarƙwaransa maza kyautai, ya kuma sallame su daga ɗansa Ishaku zuwa ƙasashen gabas.
7 Lalezi zinsuku zeminyaka yempilo kaAbrahama ayiphilayo, iminyaka elikhulu lamatshumi ayisikhombisa lanhlanu.
Duka-duka, Ibrahim ya yi shekara ɗari da saba’in da biyar.
8 UAbrahama wasephela, wafa eseluphele kuhle emdala enele, wabuthelwa ezizweni zakibo.
Sa’an nan Ibrahim ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu da kyakkyawar tsufa, tsoho da kuma shekaru masu yawa; aka kuma tara shi ga mutanensa.
9 UIsaka loIshmayeli amadodana akhe basebemngcwaba obhalwini lweMakaphela, esiqintini sikaEfroni indodana kaZohari umHethi, esiqondene leMamre,
’Ya’yansa maza kuwa Ishaku da Ishmayel suka binne shi cikin kogon Makfela, kusa da Mamre, a cikin filin Efron ɗan Zohar mutumin Hitti,
10 isiqinti uAbrahama asithenga emadodaneni akaHethi; lapho uAbrahama wangcwatshwa loSara umkakhe.
filin da Ibrahim ya saya daga Hittiyawa. A nan aka binne Ibrahim tare da matarsa Saratu.
11 Kwasekusithi emva kokufa kukaAbrahama, uNkulunkulu wambusisa uIsaka indodana yakhe; uIsaka wasehlala emthonjeni iLahayi-Royi.
Bayan rasuwar Ibrahim, Allah ya albarkaci ɗansa Ishaku wanda a lokacin yana zama kusa da Beyer-Lahai-Royi.
12 Lalezi yizizukulwana zikaIshmayeli indodana kaAbrahama, uHagari umGibhithekazi, incekukazi kaSara, amzalela uAbrahama.
Waɗannan su ne zuriyar Ishmayel ɗan Ibrahim, wanda Hagar mutuniyar Masar, baranyar Saratu, ta haifa wa Ibrahim.
13 Lala ngamabizo amadodana kaIshmayeli ngamabizo awo njengokuzalwa kwawo; izibulo likaIshmayeli nguNebayothi, loKedari loAdibeli loMibisama
Ga jerin sunayen’ya’yan Ishmayel maza bisa ga haihuwarsu, Nebayiwot ɗan farin Ishmayel, Kedar, Adbeyel, Mibsam,
14 loMishima loDuma loMasa,
Mishma, Duma, Massa,
15 uHadadi loTema, uJeturi, uNafishi loKedema;
Hadad, Tema, Yetur, Nafish da Kedema.
16 la ngamadodana kaIshmayeli, njalo la ngamabizo awo ngemizana yawo langezinqaba zawo, iziphathamandla ezilitshumi lambili ngezizwe zawo.
Waɗannan su ne’ya’yan Ishmayel maza, waɗanda kuma suke sunayen kabilu goma sha biyu masu mulki bisa ga wuraren zamansu da sansaninsu.
17 Njalo le yiminyaka yempilo kaIshmayeli, iminyaka elikhulu lamatshumi amathathu lesikhombisa; wasephela, wafa, wabuthelwa ebantwini bakibo.
Duka-duka Ishmayel ya yi shekara ɗari da talatin da bakwai; sai ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa.
18 Basebehlala kusukela eHavila kusiya eShuri ephambi kweGibhithe, ekuhambeni usiya eAsiriya; wahlala phambi kobuso babafowabo bonke.
Zuriyarsa sun zauna tsakanin Hawila ne da Shur, wanda yake kusa da gabashin iyakar Masar wajen Asshur. Sun yi zaman rikici da dukan sauran’yan’uwansu.
19 Lalezi yizizukulwana zikaIsaka indodana kaAbrahama; uAbrahama wazala uIsaka.
Waɗannan su ne zuriyar Ishaku ɗan Ibrahim. Ibrahim ya haifi Ishaku,
20 UIsaka wayeseleminyaka engamatshumi amane mhla ethatha uRebeka, indodakazi kaBethuweli umSiriya wePadani-Arama, udadewabo kaLabani umSiriya, ukuba ngumkakhe.
Ishaku yana da shekara arba’in sa’ad da ya auri Rebeka’yar Betuwel, mutumin Aram, daga Faddan Aram,’yar’uwar Laban mutumin Aram.
21 UIsaka wasemncengela umkakhe eNkosini, ngoba wayeyinyumba; iNkosi yasincengeka ngaye, kwaze kwathi uRebeka umkakhe wathatha isisu.
Ishaku ya yi addu’a ga Ubangiji a madadin matarsa, saboda ba ta haihuwa. Ubangiji ya amsa addu’arsa, matarsa Rebeka kuwa ta yi ciki.
22 Abantwana babebindana-ke ngaphakathi kwakhe; wasesithi: Uba kunjalo, kungani nginje? Wasesiyabuza iNkosi.
Jariran suka kama kokawa da juna a cikinta, sai ta ce, “Me ya sa wannan yake faruwa da ni?” Saboda haka ta tafi don ta nemi nufin Ubangiji.
23 INkosi yasisithi kuye: Izizwe ezimbili zisesizalweni sakho, izizwe ezimbili zizakwehlukana emibilini yakho. Njalo esinye isizwe sizakuba lamandla kulesinye isizwe, futhi omkhulu uzakhonza omncinyane.
Ubangiji ya ce mata, “Al’ummai biyu suna a cikin mahaifarki mutum biyu da za ki haifa, za su rabu da juna, ɗayan zai fi ɗayan ƙarfi, babban kuma zai bauta wa ƙaramin.”
24 Kwathi sezigcwalisekile insuku zakhe zokubeletha, khangela-ke, amaphahla esiswini sakhe.
Da lokaci ya yi da za tă haihu, sai ga’yan biyu maza a mahaifarta.
25 Kwasekuphuma owokuqala ebomvana, yena wonke enjengesembatho soboya; ngakho bamutha ibizo lakhe bathi nguEsawu.
Wanda ya fara fita ja ne, dukan jikinsa kuwa kamar riga mai gashi. Don haka aka sa masa suna Isuwa.
26 Njalo emva kwalokho kwaphuma umfowabo, lesandla sakhe sibambelele esithendeni sikaEsawu; basebebiza ibizo lakhe uJakobe. LoIsaka wayeleminyaka engamatshumi ayisithupha ekuzalweni kwabo.
Bayan wannan, ɗan’uwansa ya fito, da hannunsa yana riƙe da ɗiɗɗigen Isuwa; don haka aka sa masa suna Yaƙub. Ishaku yana da shekara sittin, lokacin da Rebeka ta haife su.
27 Abafana basebekhula; uEsawu wasesiba ngumzingeli ohlakaniphileyo, umuntu weganga; loJakobe umuntu obekekileyo ehlala emathenteni.
Yaran suka yi girma, Isuwa kuwa ya zama riƙaƙƙen maharbi, mutumin jeji, yayinda Yaƙub, shiru-shiru ne mai son zama a tentuna.
28 Njalo uIsaka wayemthanda uEsawu ngoba wadla inyama yenyamazana yakhe; kodwa uRebeka wathanda uJakobe.
Ishaku, mai son ci naman jeji, ya ƙaunaci Isuwa, amma Rebeka ta ƙaunaci Yaƙub.
29 Kwathi uJakobe esephekile ukudla okuphekiweyo, kwasekufika uEsawu evela egangeni, ekhathele.
Wata rana sa’ad da Yaƙub yana dafa fate. Isuwa ya shigo daga jeji, da yunwa sosai.
30 UEsawu wasesithi kuJakobe: Ake ungivumele ngiginye kokubomvu lokho okubomvu, ngoba ngikhathele. Ngalokhu babiza ibizo lakhe ngokuthi uEdoma.
Ya ce wa Yaƙub, “Ina roƙonka, ka ɗan ɗiba mini faten nan! Ina fama da yunwa!” (Shi ya sa aka kira shi Edom.)
31 UJakobe wasesithi: Ngithengisela lamuhla ilungelo lobuzibulo bakho.
Yaƙub ya amsa ya ce, “Ka fara sayar mini da matsayinka na ɗan fari tukuna.”
32 UEsawu wasesithi: Khangela, sengizakufa; njalo liyini kimi ilungelo lobuzibulo?
Isuwa ya ce, “Duba, ina gab da mutuwa, me matsayina na ɗan fari zai yi mini?”
33 UJakobe wasesithi: Funga kimi lamuhla. Wasefunga kuye, wathengisa ilungelo lobuzibulo bakhe kuJakobe.
Amma Yaƙub ya ce, “Ka rantse mini tukuna.” Don haka ya rantse masa, ya sayar da matsayinsa na ɗan fari ga Yaƙub.
34 UJakobe wasenika uEsawu isinkwa lokudla okuphekiweyo kwamalentili; wasesidla wanatha, wasukuma wahamba; ngalokho uEsawu wadelela ilungelo lobuzibulo bakhe.
Sa’an nan Yaƙub ya ba wa Isuwa burodi da ɗan miyan lansir. Ya ci, ya sha, sa’an nan ya tashi ya tafi. Ta haka Isuwa ya yi banza da matsayinsa na ɗan fari.

< UGenesisi 25 >