< UGenesisi 21 >

1 INkosi yasimhambela uSara njengokukhuluma kwayo, njalo iNkosi yenza kuSara njengoba yayitshilo.
Ana nan sai Ubangiji ya nuna wa Saratu alheri kamar yadda ya ce, Ubangiji kuma ya yi wa Saratu abin da ya yi alkawari.
2 USara wasethatha isisu, wamzalela indodana uAbrahama ebudaleni bakhe, ngesikhathi esimisiweyo uNkulunkulu abesitshilo kuye.
Saratu ta yi ciki, ta kuma haifa wa Ibrahim ɗa a tsufansa; a daidai lokacin da Allah ya yi masa alkawari.
3 UAbrahama wasesitha ibizo lendodana yakhe, eyazalelwa yena, uSara amzalela yona, wathi nguIsaka.
Ibrahim ya sa wa ɗan da Saratu ta haifa masa suna Ishaku.
4 UAbrahama wasesoka uIsaka indodana yakhe isilensuku eziyisificaminwembili, njengoba uNkulunkulu wamlaya.
Sa’ad da ɗansa Ishaku ya kai kwana takwas da haihuwa, sai Ibrahim ya yi masa kaciya, kamar yadda Allah ya umarce shi.
5 Njalo uAbrahama wayeleminyaka elikhulu lapho ezalelwa uIsaka indodana yakhe.
Ibrahim yana da shekara ɗari, sa’ad da aka haifa masa ɗansa Ishaku.
6 USara wasesithi: UNkulunkulu ungenzele uhleko, wonke ozwayo uzahleka lami.
Saratu ta ce, “Allah ya sa na yi dariya, kuma duk wanda ya ji game da wannan, zai yi dariya tare da ni.”
7 Wathi futhi: Ngubani obengatsho kuAbrahama ukuthi: USara uzamunyisa abantwana? Ngoba ngimzalele indodana ebudaleni bakhe.
Ta kuma ƙara da cewa, “Dā, wa zai iya ce wa Ibrahim, Saratu za tă yi renon yara? Duk da haka na haifar masa ɗa cikin tsufansa.”
8 Umntwana wakhula, walunyulwa. UAbrahama wasesenza idili elikhulu mhla uIsaka elunyulwa.
Yaron ya yi girma, aka kuma yaye shi, a ranar da aka yaye shi kuwa, Ibrahim ya yi babban biki.
9 USara wasebona indodana kaHagari umGibhithekazi ayeyizalele uAbrahama ikloloda.
Amma Saratu ta ga cewa yaron da Hagar, mutuniyar Masar ta haifa wa Ibrahim yana wa ɗanta Ishaku gori,
10 Ngakho wathi kuAbrahama: Xotsha lesisigqilikazi lendodana yaso; ngoba indodana yalesisigqilikazi kayiyikudla ilifa kanye lendodana yami, kanye loIsaka.
sai ta ce wa Ibrahim, “Ka kori baiwan nan tare da ɗanta, saboda ɗan baiwan nan ba zai taɓa raba gādo da ɗana Ishaku ba.”
11 Lalelilizwi laba libi kakhulu emehlweni kaAbrahama, ngenxa yendodana yakhe.
Al’amarin ya ɓata wa Ibrahim rai sosai domin zancen ya shafi ɗansa.
12 Kodwa uNkulunkulu wathi kuAbrahama: Kakungabi kubi emehlweni akho, ngenxa yomfana langenxa yesigqilikazi sakho; konke uSara azakutsho kuwe, lalela ilizwi lakhe, ngoba kuIsaka inzalo yakho izabizwa.
Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada hankalinka yă tashi game da yaron nan da kuma baiwarka. Ka saurari duk abin da Saratu ta faɗa maka, saboda ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.
13 Kodwa lendodana yesigqilikazi ngizayenza ibe yisizwe, ngoba iyinzalo yakho.
Zan ba ɗan baiwan nan al’umma shi ma, domin shi zuriyarka ne.”
14 Ngakho uAbrahama wavuka ekuseni kakhulu, wathatha isinkwa lesigxingi samanzi, wakunika uHagari, ekubeka emahlombe akhe, lomntwana, wamyekela wahamba. Wasehamba wazula enkangala iBherishebha.
Kashegari da sassafe sai Ibrahim ya ɗauki abinci da salkar ruwa, ya ba wa Hagar. Ya ɗora su a kafaɗunta, sa’an nan ya sallame ta da yaron. Ta kama hanyarta ta kuma yi ta yawo a cikin jejin Beyersheba.
15 Amanzi esephelile esigxingini waphosela umntwana phansi kwesinye sezihlahlakazana.
Sa’ad da ruwan da yake cikin salkan ya ƙare, sai ta ajiye yaron a ƙarƙashin wani ƙaramin itace.
16 Wasehamba wahlala phansi maqondana laye, esuka kuye khatshanyana, okungaba yikutshoka ngedandili; ngoba wathi: Kangingaboni ukufa komntwana. Wahlala maqondana laye, waphakamisa ilizwi lakhe wakhala inyembezi.
Sai ta tafi, ta zauna ɗan nesa da yaron, misalin nisan harbin baka, gama ta yi tunani ta ce, “Ba zan iya kallon yaron yana mutuwa ba.” Da ta zauna nesa da yaron, sai ta fara kuka.
17 UNkulunkulu wasesizwa ilizwi lomfana. Yasimemeza ingilosi kaNkulunkulu kuHagari isemazulwini, yathi kuye: Ulani, Hagari? Ungesabi, ngoba uNkulunkulu ulizwile ilizwi lomfana lapho akhona.
Allah kuwa ya ji yaron yana kuka, sai mala’ikan Allah ya kira Hagar daga sama ya ce mata, “Mene ne damuwarki, Hagar? Kada ki ji tsoro, Allah ya ji yaron yana kuka yayinda yake kwance a can.
18 Sukuma, uphakamise umfana, umbambe ngesandla sakho; ngoba ngizamenza abe yisizwe esikhulu.
Ki ɗaga yaron ki riƙe shi a hannu, gama zan mai da shi al’umma mai girma.”
19 UNkulunkulu wasevula amehlo akhe, njalo wabona umthombo wamanzi; wahamba, wagcwalisa isigxingi ngamanzi, wamnathisa umfana.
Sa’an nan Allah ya buɗe idanunta ta ga wata rijiyar ruwa. Don haka sai ta tafi ta cika salkan da ruwa, ta kuma ba wa yaron ruwa ya sha.
20 Njalo uNkulunkulu waba lomfana, wakhula, wahlala enkangala, waba ngumtshoki.
Allah ya kasance da yaron, yayinda yake girma. Ya yi zama a jeji, ya kuma zama maharbi.
21 Wahlala enkangala iParani; unina wasemthathela umfazi elizweni leGibhithe.
Yayinda yake zama a Jejin Faran, sai mahaifiyarsa ta samo masa mata daga Masar.
22 Kwasekusithi ngalesosikhathi uAbhimeleki loFikoli, induna yebutho yakhe, wakhuluma kuAbrahama wathi: UNkulunkulu ulawe kukho konke okwenzayo.
A lokacin nan Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka zo suka ce wa Ibrahim, “Allah yana tare da kai a ko mene ne kake yi.
23 Ngakho-ke funga kimi lapha ngoNkulunkulu ukuthi kawuyikungikhohlisa mina kumbe indodana yami kumbe izizukulwana zami; njengomusa engikwenzele wona, yenza kimi, lelizweni ohlala kilo njengowemzini.
Yanzu ka rantse mini a nan a gaban Allah cewa, ba za ka yaudare ni ko’ya’yana ko kuma zuriyata ba. Ka nuna mini alheri, kai da ƙasar da kake zama baƙunci kamar yadda na nuna maka.”
24 UAbrahama wasesithi: Mina ngizafunga.
Ibrahim ya ce, “Na rantse.”
25 Kodwa uAbrahama wamsola uAbhimeleki ngenxa yomthombo wamanzi ebeziwuphangile izinceku zikaAbhimeleki.
Sa’an nan Ibrahim ya kawo kuka ga Abimelek game da rijiyar ruwan da bayin Abimelek suka ƙwace.
26 UAbhimeleki wasesithi: Angazi owenze le into; njalo lawe kawungitshelanga, futhi lami kangizwanga ngakho, ngaphandle kwalamuhla.
Sai Abimelek ya ce, “Ban san wanda ya yi wannan ba. Ba ka faɗa mini ba, ban kuwa taɓa ji ba, sai yau.”
27 UAbrahama wasethatha izimvu lenkomo, wazinika uAbhimeleki; njalo bobabili benza isivumelwano.
Sai Ibrahim ya kawo tumaki da shanu ya ba wa Abimelek, sai su biyun suka yi yarjejjeniya.
28 UAbrahama wabeka amawundlukazi omhlambi ayisikhombisa wodwa.
Ibrahim ya ware’yan raguna bakwai daga cikin garke,
29 UAbhimeleki wasesithi kuAbrahama: Ayini lapha lamawundlukazi ayisikhombisa owabeke wodwa?
sai Abimelek ya ce wa Ibrahim, “Mene ne ma’anar’yan raguna bakwai da ka keɓe?”
30 Wasesithi: Ngoba uzakwemukela esandleni sami amawundlukazi ayisikhombisa, ukuze abe yibufakazi kimi bokuthi lumthombo ngiwugebhile.
Ibrahim ya amsa ya ce, “Ka karɓi waɗannan’yan tumaki bakwai daga hannuna a matsayin shaida cewa ni ne na haƙa wannan rijiya.”
31 Ngakho wabiza leyondawo ngokuthi yiBherishebha, ngoba lapho bafunga bobabili.
Saboda haka aka kira wurin Beyersheba, domin a nan ne su biyun suka yi rantsuwa.
32 Ngakho benza isivumelwano eBherishebha. UAbhimeleki wasesukuma, loFikoli induna yebutho lakhe, babuyela elizweni lamaFilisti.
Bayan da aka yi yarjejjeniya a Beyersheba, sai Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka koma ƙasar Filistiyawa.
33 Wasehlanyela isihlahla setamarisiki eBherishebha wabiza khona ibizo leNkosi, uNkulunkulu olaphakade.
Sai Ibrahim ya shuka itacen tsamiya a Beyersheba, a can kuma ya kira bisa sunan Ubangiji, Allah Madawwami.
34 UAbrahama wasehlala njengowezizwe elizweni lamaFilisti insuku ezinengi.
Ibrahim kuwa ya zauna a ƙasar Filistiyawa na dogon lokaci.

< UGenesisi 21 >