< UGenesisi 18 >
1 INkosi yasibonakala kuye ema-okhini eMamre, wathi ehlezi emnyango wethente ekutshiseni kosuku,
Ubangiji ya bayyana ga Ibrahim kusa da manyan itatuwan Mamre yayinda yake zaune a mashigin tentinsa da tsakar rana.
2 wasephakamisa amehlo akhe wabona, khangela-ke amadoda amathathu emi phambi kwakhe; esewabonile wagijima ukuwahlangabeza esuka emnyango wethente, wakhothamela emhlabathini,
Da Ibrahim ya ɗaga ido, sai ya ga mutum uku suna tsaye kusa da shi. Sa’ad da ya gan su, sai ya tashi nan da nan daga mashigin tentinsa, ya tarye su, ya rusuna har ƙasa.
3 wasesithi: Nkosi, uba-ke ngithole umusa emehlweni akho, ngicela ungadluli usuke encekwini yakho.
Ya ce, “Ranka yă daɗe, in na sami tagomashi daga gare ku kada ku wuce bawanku.
4 Ake kulethwe amanzi amalutshwana, beseligeza inyawo zenu, liphumule ngaphansi kwesihlahla.
Bari a kawo ruwa ku wanke ƙafafunku, ku huta a ƙarƙashin wannan itace.
5 Ngizaletha-ke ucezu lwesinkwa, beseliqinisa inhliziyo yenu, beselisedlula, ngoba yikho ledlule encekwini yenu. Asesithi: Ngokunjalo yenza njengokutsho kwakho.
Bari in samo muku wani abu ku ci don ku wartsake, sa’an nan ku ci gaba da tafiyarku; da yake kun biyo wurin bawanku.” Suka ce, “To, sai ka yi abin da ka ce.”
6 UAbrahama wasephangisa esiya ethenteni kuSara, wasesithi: Phangisa! Amaseya amathathu empuphu ecolekileyo! Xova, wenze amaqebelengwana.
Saboda haka Ibrahim ya ruga zuwa wurin Saratu a cikin tenti ya ce, “Yi sauri, ki shirya mudu uku na gari mai laushi, ki cuɗa shi, ki yi burodi.”
7 UAbrahama wasegijimela enkomeni, wathatha ithole elibuthakathaka njalo elihle, walinika ijaha; laphangisa ukulilungisa.
Sa’an nan Ibrahim ya yi gudu zuwa garkensa, ya zaɓi ɗan maraƙi ya ba wa bawansa, bawansa kuma ya yi sauri ya gyara shi.
8 Wasethatha amasi lochago, lethole abelilungisile, wakubeka phambi kwawo; wema eduze lawo ngaphansi kwesihlahla, asesidla.
Sa’an nan Ibrahim ya ɗauko dambu da madara da naman ɗan maraƙin da aka gyara, ya kawo a gabansu. Yayinda suke ci, ya tsaya a gindin itace kusa da su.
9 Asesithi kuye: Ungaphi uSara umkakho? Wasesithi: Khangela, ethenteni.
Sai suka ce masa, “Ina Saratu matarka?” Ibrahim ya ce, “Tana can cikin tenti.”
10 Yasisithi: Isibili ngizabuya kuwe ngalesisikhathi sempilo; khangela, uSara umkakho uzakuba lendodana. USara wakuzwa esemnyango wethente elalingemva kwayo.
Sa’an nan ɗayansu ya ce, “Lalle zan komo wurinka war haka shekara mai zuwa. Saratu matarka kuwa za tă haifi ɗa.” Saratu kuwa tana a bayansu tana ji daga mashigin tenti.
11 UAbrahama loSara basebebadala sebelensuku ezinengi; kwasekuphelile kuSara okwendlela yabafazi.
Ibrahim da Saratu dai sun riga sun tsufa sosai. Saratu kuma ta wuce shekarun haihuwa.
12 USara wasehlekela ngaphakathi, esithi: Sengigugile, ngingaba lenjabulo, lenkosi yami isindala yini?
Saboda haka Saratu ta yi dariya da ta yi tunani a zuci tana cewa, “Bayan ƙarfina ya ƙare, maigidana kuma ya tsufa, yanzu zan sami wannan jin daɗi?”
13 INkosi yasisithi kuAbrahama: Kungani uSara ehleka, esithi: Isibili lami ngizazala mina sengimdala yini?
Sai Ubangiji ya ce wa Ibrahim, “Me ya ba Saratu dariya har da ta ce, ‘Har zan iya haifi ɗa duk ta tsufata yanzu?’
14 Kukhona into enzima kakhulu eNkosini yini? Ngesikhathi esimisiweyo ngizabuya kuwe, ngalesisikhathi sempilo, njalo uSara uzakuba lendodana.
Akwai abin zai gagari Ubangiji? Zan komo wurinka a ƙayyadadden lokacin nan shekara mai zuwa kuma Saratu za tă haifi ɗa.”
15 USara wasephika esithi: Kangihlekanga, ngoba wayesesaba. Kodwa wathi: Hatshi, ngoba uhlekile.
Saratu ta ji tsoro, don haka sai ta yi ƙarya ta ce, “Ban yi dariya ba.” Ya ce, “A’a, kin yi dariya.”
16 Amadoda asesukuma esuka lapho akhangela phansi eSodoma; uAbrahama wasehamba lawo ewaphelekezela.
Sai mutanen suka tashi suka nufi Sodom, Ibrahim kuwa ya yi musu rakiya, ya yi bankwana da su.
17 INkosi yasisithi: Mina ngingamfihlela uAbrahama yini engikwenzayo?
Sai Ubangiji ya ce, “Zan ɓoye wa Ibrahim abin da nake shirin yi?
18 Ngoba isibili uAbrahama uzakuba yisizwe esikhulu esilamandla; lazo zonke izizwe zomhlaba zizabusiswa kuye.
Lalle Ibrahim zai zama al’umma mai girma da kuma mai iko, kuma ta wurinsa dukan al’umman duniya za su sami albarka.
19 Ngoba ngimazile, ukuze alaye abantwana bakhe lendlu yakhe emva kwakhe, besebegcina indlela yeNkosi ukuze benze ukulunga lokwahlulela, ukuze iNkosi imehlisele uAbrahama lokho ekutshoyo ngaye.
Saboda na zaɓe shi don yă umarci’ya’yansa da iyalinsa a bayansa su kiyaye hanyoyin Ubangiji, ta wurin yin abin da yake daidai da kuma yin adalci, domin Ubangiji ya aikata abin da ya yi wa Ibrahim alkawari.”
20 INkosi yasisithi: Ngoba isikhalo seSodoma leGomora sikhulu, langoba isono sabo sinzima kakhulu,
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kuka a kan Sodom da Gomorra ta yi yawa, zunubinsu kuma ya yi muni sosai,
21 ngizakwehla-ke besengibona ukuthi njengokwesikhalo sayo esesifike kimi, benzile ngokupheleleyo; kodwa uba kungenjalo ngizakwazi.
zan gangara in ga ko abin da suka yi ya yi muni kamar yadda kukan ya zo gare ni, zan bincike.”
22 Amadoda esefulathele lapho, asesiya eSodoma; kodwa uAbrahama wayelokhu emile phambi kweNkosi.
Sai mutanen suka juya suka nufi wajen Sodom amma Ibrahim ya ci gaba da kasance a gaban Ubangiji.
23 UAbrahama wasesondela, wathi: Kambe uzambhubhisa lolungileyo kanye lomubi?
Sai Ibrahim ya matso wurinsa ya ce, “Za ka hallaka masu adalci tare da masu mugunta?
24 Mhlawumbe kukhona abalungileyo abangamatshumi amahlanu phakathi komuzi; kambe uzabhubhisa ungaxoleli indawo ngenxa yabalungileyo abangamatshumi amahlanu abakuwo?
Me zai faru in akwai mutum hamshin masu adalci a cikin birnin? Ashe, za ka hallaka shi, ba za ka cece wurin saboda mutane hamsin nan masu adalcin da suke a cikinsa ba?
25 Kakube khatshana lawe ukwenza into enjalo, ukubulala olungileyo kanye lomubi lokuthi olungileyo abe njengomubi; kakube khatshana lawe; umahluleli womhlaba wonke kayikwenza ukulunga yini?
Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba, ka kashe masu adalci tare da masu mugunta, ka ɗauka masu adalci da masu mugunta daidai? Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba! Mai hukuncin dukan duniya ba zai aikata gaskiya ba?”
26 INkosi yasisithi: Uba ngithola eSodoma abalungileyo abangamatshumi amahlanu phakathi komuzi, ngizaxolela yonke indawo ngenxa yabo.
Ubangiji ce, “In na sami mutum hamshin masu adalci a cikin birnin Sodom, zan bar dukan birnin saboda su.”
27 UAbrahama wasephendula wathi: Khangela-ke, ngizimisele ukukhuluma eNkosini, lanxa ngiluthuli lomlotha.
Sai Ibrahim ya ƙara cewa, “Yanzu da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, ko da yake ni ba kome ba ne illa turɓaya da toka,
28 Mhlawumbe kuzasweleka abahlanu kubo abalungileyo abangamatshumi amahlanu; uzabhubhisa umuzi wonke ngenxa yabahlanu yini? Yasisithi: Kangiyikuwubhubhisa uba ngithola khona abangamatshumi amane lanhlanu.
in yawan masu adalci sun kāsa hamshin da mutum biyar fa? Za ka hallaka dukan birnin saboda rashin mutum biyar ɗin?” Ya ce, “In na sami mutum arba’in da biyar a wurin, ba zan hallaka shi ba.”
29 Waseqhubeka elokhu ekhuluma kuyo wathi: Mhlawumbe kuzatholwa khona abangamatshumi amane. Yasisithi: Kangiyikukwenza ngenxa yabangamatshumi amane.
Ya sāke cewa, “In mutum arba’in kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda mutum arba’in ɗin, ba zan aikata ba.”
30 Wasesithi: Ngicela iNkosi ingathukutheli lapho ngikhuluma. Mhlawumbe kuzatholwa khona abangamatshumi amathathu. Yasisithi: Kangiyikukwenza uba ngithola khona abangamatshumi amathathu.
Sai ya ce, “Kada Ubangiji ya yi fushi, amma bari in ƙara magana. A ce mutum talatin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Ba zan aikata ba, in na sami mutum talatin a can.”
31 Wasesithi: Khangela-ke, ngizimisele ukukhuluma eNkosini; mhlawumbe kuzatholwa khona abangamatshumi amabili. Yasisithi: Kangiyikuwubhubhisa ngenxa yabangamatshumi amabili.
Ibrahim ya ce, “Yanzu fa da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, in ashirin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda ashirin ɗin, ba zan hallaka shi ba.”
32 Wasesithi: Ngicela iNkosi ingathukutheli, ngizakhuluma khathesi kuphela; mhlawumbe kuzatholwa khona abalitshumi. Yasisithi: Kangiyikuwubhubhisa ngenxa yabalitshumi.
Sa’an nan Ibrahim ya ce, “Kada Ubangiji yă yi fushi, amma bari in ƙara magana sau ɗaya tak. In aka sami mutum goma kaɗai a can fa?” Ubangiji ya ce, “Saboda goma nan, ba zan hallaka shi ba.”
33 INkosi yasihamba isiqedile ukukhuluma kuAbrahama; uAbrahama wasebuyela endaweni yakhe.
Sa’ad da Ubangiji ya gama magana da Ibrahim, ya tafi, Ibrahim kuma ya koma gida.