< UGenesisi 15 >
1 Emva kwalezizinto ilizwi leNkosi leza kuAbrama ngombono, lisithi: Ungesabi Abrama, ngiyisihlangu sakho, umvuzo wakho omkhulu kakhulu.
Bayan wannan, maganar Ubangiji ta zo wa Abram cikin mafarki cewa, “Kada ka ji tsoro, Abram. Ni ne garkuwarka, kuma ladanka zai zama mai girma.”
2 UAbrama wasesithi: Nkosi Jehova, uzangiphani, njengoba lokhe ngingelamntwana, lendlalifa yendlu yami ingoweDamaseko uEliyezeri?
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mene ne za ka ba ni, ganin cewa ba na haihuwa, wanda kuma zai gāji gādon gidana shi ne Eliyezer mutumin Damaskus?”
3 UAbrama wasesithi: Khangela, kimi kawuphanga nzalo; njalo khangela, ozelwe endlini yami uzakuba yindlalifa yami.
Abram ya kuma ce, “Ga shi ba ka ba ni ɗa ba, don haka bawan da aka haifa a gidana ne zai zama magājina.”
4 Khangela-ke ilizwi leNkosi laba kuye lisithi: Lo kayikudla ilifa lakho, kodwa ozaphuma emibilini yakho, yena uzakudla ilifa lakho.
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Wannan mutum ba zai zama magājinka ba, ɗa da yake zuwa daga jikinka ne zai zama magājinka.”
5 Wasemkhuphela phandle wathi: Khangela-ke emazulwini, ubale izinkanyezi uba ungazibala. Wasesithi kuye: Izakuba njalo inzalo yakho.
Sai Ubangiji ya fito da kai shi waje ya ce, “Ka dubi sammai ka kuma ƙirga taurari, in har za ka iya ƙirga su.” Sa’an nan ya ce masa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
6 Wasekholwa eNkosini. Yasimbalela lokhu kube yikulunga.
Abram ya gaskata, Ubangiji kuma ya lasafta shi adalci ga Abram.
7 Yasisithi kuye: NgiyiNkosi, eyakukhupha eUri yamaKhaladiya ukukunika ilizwe leli libe yilifa lakho.
Ubangiji ya kuma ce wa Abram, “Ni ne Ubangiji wanda ya fitar da kai daga Ur na Kaldiyawa, domin in ba ka wannan ƙasa ka mallake ta.”
8 Wasesithi: Nkosi Jehova, ngizakwazi ngani ukuthi lizakuba yilifa lami?
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, yaya zan san cewa zan mallake ta?”
9 Yasisithi kuye: Ngithathela ithokazi elileminyaka emithathu, lesibhuzikazi esileminyaka emithathu, lenqama eleminyaka emithathu, lejuba, lephuphu lenkwilimba.
Saboda haka Allah ya ce masa, “Kawo mini karsana, akuya, da kuma rago kowanne yă kasance shi shekara uku ne, da kurciya da kuma ɗan tattabara.”
10 Wasesisa kuyo zonke lezizinto, wazidabula phakathi, wabeka leyo laleyongxenye yazo ikhangelene lenye; kodwa inyoni kazidabulanga.
Abram ya kawo waɗannan duka a gaban Allah, ya raba kowannensu a tsakiya, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba.
11 Inyoni ezidla inyama zasezisehlela phezu kwezidumbu, uAbrama wasezixotshela khatshana.
Sai tsuntsaye masu cin nama suka sauko a kan gawawwakin, amma Abram ya kore su.
12 Kwasekusithi ilanga selitshona, ubuthongo obukhulu bajuma uAbrama; khangela-ke, uvalo lomnyama omkhulu lwehlela phezu kwakhe.
Yayinda rana tana fāɗuwa, sai Abram ya yi barci mai zurfi, sai wani duhu mai kauri mai kuma bantsoro ya rufe shi.
13 Yasisithi kuAbrama: Yazi lokwazi ukuthi inzalo yakho izakuba yisihambi elizweni elingeyisilo layo, njalo bazabasebenzela, besebebahlupha iminyaka engamakhulu amane.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani tabbatacce cewa shekaru ɗari huɗu, zuriyarka za tă zama baƙi a ƙasar da ba tasu ba, za a mai da su bayi, a kuma wulaƙanta su.
14 Kodwa lesizwe abazasisebenzela ngizasigweba; lemva kwalokho bazaphuma lempahla enengi.
Amma zan hukunta al’ummar da suka yi bauta kamar bayi, daga baya kuma za su fita da mallaka mai yawa.
15 Kodwa wena uzakuya kuboyihlo ngokuthula, uzangcwatshwa ekuluphaleni okuhle.
Amma kai za ka koma wurin kakanninka cikin salama a kuma binne ka da kyakkyawan tsufa.
16 Isizukulwana sesine sizabuya-ke lapha; ngoba isono samaAmori kasikapheleli.
A tsara ta huɗu zuriyarka za tă komo nan, saboda zunubin Amoriyawa bai riga ya cika ba.”
17 Kwasekusithi ilanga selitshonile sekumnyama, khangela-ke, imbawula ethunqayo lesihlanti somlilo esadabula phakathi kwalezozingxenye.
Sa’ad da rana ta fāɗi, aka kuwa yi duhu, sai wata tukunya mai hayaƙi, mai harshen wuta mai ci, ta bayyana, ta kuma wuce tsakanin abubuwan nan da aka tsaga.
18 Ngalolosuku iNkosi yenza isivumelwano loAbrama isithi: Enzalweni yakho nginikele lelilizwe, kusukela emfuleni weGibhithe kuze kube semfuleni omkhulu, umfula iYufrathi,
A wannan rana, Ubangiji ya yi alkawari da Abram ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga kogin Masar zuwa babban kogi, Yuferites ke nan,
19 amaKeni lamaKenizi lamaKadimoni
ƙasar Keniyawa, Kenizziyawa, Kadmoniyawa,
20 lamaHethi lamaPerizi lamaRefa
Hittiyawa, Ferizziyawa, Refahiyawa,
21 lamaAmori lamaKhanani lamaGirigashi lamaJebusi.
Amoriyawa, Kan’aniyawa, Girgashiyawa da kuma Yebusiyawa.”