< KwabaseGalathiya 2 >

1 Emva kwalokho sekwedlule iminyaka elitshumi lane ngenyukela futhi eJerusalema kanye loBarnabasi, ngathatha loTitosi futhi;
Bayan shekara goma sha huɗu sai na sāke haurawa zuwa Urushalima, a wannan lokaci na tafi tare da Barnabas. Na kuma ɗauki Titus muka tafi tare.
2 ngasengisenyuka ngesambulelo, ngasengibalandisela ivangeli engilitshumayela phakathi kwabezizwe, kodwa ngasese kulabo ababelodumo, hlezi mhlawumbe ngigijimele kumbe ngagijimela ize.
Na tafi ne bisa ga wani wahayi. Da na kai can, sai na bayyana musu bisharar da nake wa’azi a cikin Al’ummai. Na yi haka a keɓance a gaban waɗanda suke shugabanni, don tsoro kada gudun da nake yi, ko kuwa na riga na yi, yă zama a banza.
3 Kodwa ngitsho uTitosi owayelami, engumGriki, kacindezelwanga ukuthi asokwe;
Amma ko Titus ma da yake tare da ni, ba a ce dole sai ya yi kaciya ba, ko da yake shi mutumin Al’ummai ne.
4 njalo ngenxa yabazalwane bamanga abangeniswa ngensitha, abangena ngokunyenya ukuze bahlole ukukhululeka kwethu esilakho kuKristu Jesu, ukuze basenze izigqili;
Wannan zancen kaciya ya taso domin waɗansu’yan’uwan ƙarya sun shiga cikinmu domin su yi leƙe a kan’yancin da muke da shi a cikin Kiristi Yesu, su kuma mai da mu bayi.
5 esingabathobelanga ngokuzehlisa ngitsho okwehola, ukuze iqiniso levangeli lime njalo kini.
Ba mu kuwa ba su zarafi ba ko kaɗan, don gaskiyar bishara ta ci gaba da kasance tare da ku.
6 Kodwa kulabo okuthiwa bayilutho (loba babeyini kakutsho lutho kimi; uNkulunkulu kemukeli isimo somuntu) ngoba labo ababedunyisiwe kabangelekelelanga ngalutho;
Game da waɗanda aka ɗauka a dā a kan su wani abu ne, ko wane ne su, duk ɗaya ne a wurina; gama Allah ba ya nuna bambanci, ina dai gaya muku waɗannan da suke wani abu ne a dā, ba su ƙara mini kome ba.
7 kodwa kokuphambeneyo, bebona ukuthi ngaphiwa ivangeli lokungasoki, njengoPetro elokusoka,
A maimakon haka, sun ga cewa an danƙa mini hakkin wa’azin bishara ga Al’ummai, kamar yadda aka danƙa wa Bitrus ga Yahudawa.
8 ngoba owenza ngamandla kuPetro kubuphostoli bokusoka, wenza ngamandla lakimi kwabezizwe,
Gama Allah wanda ya yi aiki a cikin hidimar Bitrus a matsayin manzo ga Yahudawa, haka ma ya yi aiki a cikin hidimata a matsayin manzo ga Al’ummai.
9 bathi besazi umusa engiwuphiweyo, oJakobe loKefasi loJohane, abadume bezinsika, banika mina loBarnabasi isandla sokunene sobudlelwano, ukuze thina siye kwabezizwe, bona-ke ekusokweni;
Yaƙub, Bitrus da Yohanna waɗanda suke fitattun ginshiƙai, sun karɓe ni da Barnabas da hannu biyu biyu sa’ad da suka gane alherin da aka ba ni. Suka kuma yarda cewa ya kamata mu tafi wajen Al’ummai, su kuwa su tafi wajen Yahudawa.
10 kuphela ukuze sikhumbule abayanga, into le lami engangikhuthalele ukuyenza.
Abin da dai suka roƙa shi ne ya kamata mu riƙa tuna da matalauta, abin nan da nake marmarin yi.
11 Kodwa kwathi uPetro efika eAntiyoki, ngamelana laye ebusweni, ngoba wayefanele asolwe.
Sa’ad da Bitrus ya zo Antiyok, na tsawata masa ido da ido don laifinsa a fili yake.
12 Ngoba bengakafiki abathile abavela kuJakobe, wayesidla labezizwe; kodwa kuthe sebefikile, wamonyuka wazehlukanisa, esesaba abokusoka.
Kafin waɗansu mutane su zo daga wurin Yaƙub, yakan ci abinci tare da Al’ummai. Amma da suka iso, sai ya fara janyewa, ya kuma ware kansa daga wajen Al’ummai domin yana tsoron waɗanda suke ƙungiyar masu kaciya.
13 Lamanye futhi amaJuda azenzisa kanye laye, kwaze kwathi loBarnabasi wathatheka ngokuzenzisa kwawo.
Sauran Yahudawa suka haɗa kai da shi a munafuncinsa har Barnabas ma ya bauɗe.
14 Kodwa kuthe sengibonile ukuthi kabahambi ngokuqonda eqinisweni levangeli, ngathi kuPetro phambi kwabo bonke: Uba wena ungumJuda, uphila ngokwabezizwe njalo kungeyisikho ngokwamaJuda, ubacindezelelani abezizwe ukuthi baphile ngokwamaJuda?
Da na ga cewa ba sa yin daidai da gaskiyar bishara, sai na ce wa Bitrus a gabansu duka, “Kai mutumin Yahuda ne, duk da haka kana rayuwa kamar Ba’al’umme ba kamar mutumin Yahuda ba. To, yaya aka yi, kana tilasta Al’ummai su bi al’adun Yahudawa?
15 Thina singamaJuda ngemvelo, njalo kasisizo izoni ezivela kwabezizwe,
“Mu da muke Yahudawa ta wurin haihuwa ba Al’ummai masu zunubi ba,
16 sisazi ukuthi umuntu kalungisiswa ngemisebenzi yomlayo, kodwa ngokholo lukaJesu Kristu, lathi sakholwa kuKristu Jesu, ukuze silungisiswe ngokholo lukaKristu, njalo kungeyisikho ngemisebenzi yomlayo; ngoba ngemisebenzi yomlayo kakuyikulungisiswa nyama.
mun san cewa mutum ba ya samun kuɓuta ta wurin kiyaye Doka, sai dai ta wurin bangaskiya cikin Kiristi Yesu. Saboda haka, mu ma, muka sa bangaskiyarmu cikin Kiristi Yesu don mu sami kuɓuta ta wurin bangaskiya cikin Kiristi ba ta wurin kiyaye Doka ba, domin ba wanda zai kuɓuta ta wurin bin Doka.
17 Kodwa uba thina, esidinga ukulungisiswa kuKristu, lathi uqobo sificwe siyizoni, ngakho uKristu uyisisebenzi sesono yini? Phinde!
“In kuwa ya zama muna so mu sami zaman marasa laifi a gaban Allah ta wurin dogara ga Kiristi, sa’an nan an same mu mu kanmu ma masu zunubi ne, ashe, ko wannan zai nuna Kiristi yana ƙarfafa zunubi ke nan? A’a, ko kusa!
18 Ngoba uba ngibuye ngakhe izinto engizidilizileyo, ngitshengisa ukuthi ngingophambekayo.
In na sāke gina abin da na rushe, na zama mai karyar Doka ke nan.
19 Ngoba ngomlayo mina ngafa kuwo umlayo, ukuze ngiphile kuNkulunkulu.
“Gama ta wurin Doka na mutu ga Doka saboda in rayu ga Allah.
20 Ngibethelwe kanye loKristu, kodwa ngiyaphila; kakuseyimi-ke, kodwa uKristu uphila kimi; kodwa lokhu engikuphila khathesi enyameni ngikuphila ekholweni lweNdodana kaNkulunkulu eyangithandayo njalo yazinikelela mina.
An gicciye ni tare da Kiristi. Yanzu ba ni ne nake raye ba, Kiristi ne yake raye a cikina. Rayuwar da nake yi a jiki, ina rayuwa ce ta wurin bangaskiya cikin Ɗan Allah, wanda ya ƙaunace ni ya kuma ba da kansa domina.
21 Kangiwutshayi ize umusa kaNkulunkulu; ngoba uba ukulunga kusiya ngomlayo, ngakho uKristu wafela ize.
Ba na ajiyar alherin Allah a gefe, gama da a ce ana samun adalci ta wurin Doka, ai, da Kiristi ya mutu a banza ke nan!”

< KwabaseGalathiya 2 >