< UHezekheli 44 >

1 Wasengibuyisela ngendlela yesango lendawo engcwele engaphandle, elikhangele ngasempumalanga, elalivalekile.
Sai mutumin ya komo da ni zuwa ƙofar waje na wuri mai tsarki, wadda take fuskantar gabas, tana kuwa a rufe.
2 INkosi yasisithi kimi: Lelisango lizahlala livaliwe, kaliyikuvulwa, kakulamuntu ozangena ngalo; ngoba iNkosi, uNkulunkulu kaIsrayeli, ingene ngalo, ngakho lizakuba livalekile.
Ubangiji ya ce mini, “Wannan ƙofar za tă kasance a rufe. Ba za a buɗe ta ba; ba wanda zai shiga ta wurinta. Za tă kasance a rufe domin Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya shiga ta wurinta.
3 Libe ngelesiphathamandla; isiphathamandla, sona sizahlala kilo, ukuthi sidle isinkwa phambi kweNkosi. Ngendlela yekhulusi lesango sizangena, langendlela yalo sizaphuma.
Sarki kansa ne kaɗai zai zauna a hanyar shiga don yă ci a gaban Ubangiji. Zai shiga ta hanyar shirayin hanyar shiga yă kuma fita a wannan hanya.”
4 Wasengiletha ngendlela yesango lenyakatho ngaphambi kwendlu. Ngasengibona, khangela-ke, inkazimulo yeNkosi yagcwalisa indlu yeNkosi; ngasengisithi mbo ngobuso bami.
Sa’an nan mutumin ya kawo ni ta hanyar ƙofar arewa zuwa gaban haikali. Na duba na kuma ga ɗaukakar Ubangiji tana cika haikalin Ubangiji, sai na fāɗi rubda ciki.
5 INkosi yasisithi kimi: Ndodana yomuntu, beka inhliziyo yakho, ubone ngamehlo akho, uzwe ngendlebe zakho, konke engizakutshela khona mayelana lezimiso zonke zendlu yeNkosi, lemilayo yayo yonke; ubeke inhliziyo yakho kuyo indawo yokungena yendlu, lazo zonke izindawo zokuphuma zendawo engcwele.
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, ka lura sosai, ka saurara sosai ka kuma mai da hankali ga kome da na faɗa maka game da dukan ƙa’idodi game da haikalin Ubangiji. Ka lura sosai da ƙofar shigar haikali da kuma dukan ƙofofin wuri mai tsarki.
6 Njalo uzakuthi kubo abavukelayo, kiyo indlu kaIsrayeli: Itsho njalo iNkosi uJehova: Sekwanele kini, ngenxa yazo zonke izinengiso zenu, lina ndlu kaIsrayeli.
Faɗa wa’yan tawayen gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ayyukan banƙyamarku sun isa haka, ya gidan Isra’ila!
7 Ngoba lingenisile abezizwe, abangasokanga ngenhliziyo labangasokanga ngenyama, ukuthi babe sendaweni yami engcwele, ukuyingcolisa, ngitsho indlu yami, lapho linikela isinkwa sami, amafutha, legazi, futhi bephulile isivumelwano sami ngamanyala enu wonke.
Ban da dukan sauran ayyukanku na banƙyama, kun kawo baƙi marasa kaciya a zuciya da jiki a wurina mai tsarki, kun kuma ƙazantar da haikalina yayinda kuke miƙa mini abinci, kitse da kuma jini, kun kuma karya alkawarina.
8 Njalo kaligcinanga umlindo wezinto zami ezingcwele; kodwa lizimisele abagcini bomlindo wami endaweni yami engcwele.
A maimakon yin ayyukanku bisa ga abubuwana masu tsarki, kun sa waɗansu su lura da wurina mai tsarki.
9 Itsho njalo iNkosi uJehova: Kakulamuntu wezizwe, ongasokanga enhliziyweni, kumbe ongasokanga enyameni, ozangena endaweni yami engcwele, kuye wonke owezizwe ophakathi kwabantwana bakoIsrayeli.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba baƙo marar kaciya a zuciya da jiki da zai shiga wurina mai tsarki, kai, har ma da baƙin da suke zama a cikin Isra’ila.
10 Kodwa amaLevi asuka aya khatshana lami, lapho uIsrayeli eduha, aduha esuka kimi elandela izithombe zawo, ngitsho azathwala isiphambeko sawo.
“‘Lawiyawan da suka yi nesa da ni sa’ad da Isra’ila suka kauce da kuma waɗanda suka karkata daga gare ni suka bi gumakansu, dole su ɗauki alhakin zunubinsu.
11 Kube kanti azakuba yizikhonzi endaweni yami engcwele, belobubonisi bamasango endlu, njalo ekhonza endlini; wona azahlaba umnikelo wokutshiswa lomhlatshelo owenzelwa abantu, wona ame phambi kwabo ukuze abakhonze.
Za su iya yin hidima a wurina mai tsarki, suna lura da ƙofofin haikali suna kuma hidima a cikinsu; za su iya yankan hadayun ƙonawa da sadaka don mutane su kuma tsaya a gaban mutane su yi musu hidima.
12 Ngenxa yokuthi bebakhonze phambi kwezithombe zabo, baba yisikhubekiso sesiphambeko kuyo indlu yakoIsrayeli, ngalokho ngiphakamise isandla sami ngimelene labo, itsho iNkosi uJehova, ukuthi bazathwala isiphambeko sabo.
Amma domin sun yi musu hidima a gaban gumakansu suka sa gidan Isra’ila ya yi zunubi, saboda haka na ɗaga hannu na rantse cewa dole su ɗauki alhakin zunubinsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
13 Njalo kabayikusondela kimi, ukuze bangisebenzele njengabapristi, loba basondele lakuziphi izinto zami ezingcwele, endaweni eyingcwelengcwele; kodwa bazathwala ihlazo labo, lamanyala abo abawenzileyo.
Ba za su yi kusa don su yi hidima kamar firistoci ko su zo kusa da abubuwana masu tsarki ko hadayuna mafi tsarki ba; dole su sha kunya saboda ayyukansu na banƙyama.
14 Kodwa ngizabenza abagcini bomlindo wendlu, kuwo wonke umsebenzi wayo, lakukho konke okuzakwenziwa kiyo.
Duk da haka zan sa su su lura da ayyukan haikali da kuma dukan ayyukan da za a yi a cikinsa.
15 Kodwa abapristi abangamaLevi, amadodana kaZadoki, abagcina umlindo wendawo yami engcwele lapho abantwana bakoIsrayeli beduha besuka kimi, bona bazasondela kimi ukungikhonza, beme phambi kwami ukunikela kimi amahwahwa legazi, itsho iNkosi uJehova.
“‘Amma firistoci, waɗanda suke Lawiyawa kuma zuriyar Zadok waɗanda suka yi aminci ta wurin yin ayyukansu a wurina mai tsarki sa’ad da Isra’ilawa suka kauce daga gare ni, su ne za su zo kusa don hidima a gabana; za su tsaya a gabana don miƙa hadayun kitse da jini, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
16 Bona bazangena endaweni yami engcwele, bona basondele etafuleni lami ukungikhonza, bagcine umlindo wami.
Su ne kaɗai za su shiga wurina mai tsarki; su ne kaɗai za su zo kusa da teburina don yin hidima a gabana su kuma yi hidimata.
17 Kuzakuthi-ke lapho bengena emasangweni eguma elingaphakathi, bagqoke izembatho zelembu elicolekileyo, kodwa uboya bezimvu kabuyikuza phezu kwabo, besakhonza emasangweni eguma elingaphakathi, langaphakathi.
“‘Sa’ad da suka shiga ƙofofin fili na can ciki, dole su sa tufafin lilin; kada su sa wani rigar da aka yi da ulu yayinda suke hidima a ƙofofin fili na can ciki da cikin haikali.
18 Kuzakuba lamaqhiye elembu elicolekileyo emakhanda abo, labokabhudula bangaphansi belembu elicolekileyo babe enkalweni zabo, bangabhinci ngokuginqisayo.
Za su naɗa rawunan lilin a kawunansu, su kuma sa wandunan lilin. Kada su sa wani abin da zai sa su yi zuffa.
19 Lalapho bephumela egumeni elingaphandle, ngitsho egumeni elingaphandle besiya ebantwini, bazakhulula izembatho zabo abakhonza ngazo, bazibeke emakamelweni angcwele, bagqoke ezinye izigqoko, njalo kabayikungcwelisa abantu ngezembatho zabo.
Sa’ad da suka fita daga haikali zuwa fili na waje inda mutane suke, sai su tuɓe rigunan da suka yi hidima da su su bar su a tsarkakan ɗakuna, su sa waɗansu riguna, don kada su tsarkake mutane ta wurin rigunansu.
20 Futhi kabayikuphuca amakhanda abo, kabayikuvumela izihluthu zenwele zikhule zibe zinde; bazagela lokugela amakhanda abo.
“‘Ba za su aske kawunansu ko su bar gashin kansu ya yi tsayi ba, amma sai su sausaye gashin kansu.
21 Futhi kabayikunatha iwayini, ngulowo lalowompristi, ekungeneni kwabo egumeni elingaphakathi.
Kada firist ya sha ruwan inabi sa’ad da zai shiga fili na can ciki.
22 Njalo kabayikuzithathela umfelokazi kumbe olahliweyo babe ngabafazi, kodwa bazathatha izintombi ezimsulwa zenzalo yendlu yakoIsrayeli, loba umfelokazi ongumfelokazi wompristi.
Kada su auri gwauruwa ko macen da aka sāke; za su auri budurwai ne kaɗai na Isra’ilawa ko gwaurayen firistoci.
23 Njalo bazafundisa abantu bami umehluko phakathi kokungcwele lokungangcwele, babazise umehluko phakathi kokungcolileyo lokuhlambulukileyo.
Za su koyar da mutanena bambanci tsakanin tsarki da rashin tsarki su kuma nuna musu yadda za su bambanta marar tsarki da mai tsarki.
24 Lekuphikisaneni bona bazakuma ekwahluleleni, bahlulele ngokwezahlulelo zami. Bagcine imilayo yami lezimiso zami kiyo yonke imikhosi yami emisiweyo, bangcwelise amasabatha ami.
“‘A duk wani rashin jituwa, firistoci za su zama alƙalai su kuma yanke magana bisa ga farillaina. Za su kiyaye dokokina da ƙa’idodina a dukan ƙayyadaddun bukukkuwana, su kuma kiyaye Asabbataina da tsarki.
25 Njalo kabayikuza emuntwini ofileyo ukuzingcolisa; kodwa ngoyise, kumbe ngonina, kumbe ngendodana, kumbe ngendodakazi, ngomfowabo, kumbe ngodadewabo ongeyisuye wendoda, bangazingcolisa.
“‘Firist ba zai ƙazantar da kansa ta wurin zuwa kusa da gawa ba; amma, in gawar mahaifinsa ko mahaifiyarsa, ko ɗansa ko’yarsa, ko ɗan’uwansa ko’yar’uwarsa ce, to, ba zai ƙazantar da kansa ba.
26 Langemva kokuhlanjululwa kwakhe bazambalela insuku eziyisikhombisa.
Bayan ya tsarkaka, dole yă jira har kwana bakwai.
27 Langosuku azangena ngalo endaweni engcwele, egumeni elingaphakathi, ukuyakhonza endaweni engcwele, uzanikela umnikelo wakhe wesono, itsho iNkosi uJehova.
A ranar da ya shiga fili na can ciki na wuri mai tsarki don hidima a wuri mai tsarki, zai miƙa hadaya don zunubi saboda kansa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
28 Lokhu kuzakuba yilifa kubo; ngiyilifa labo; njalo kaliyikubanika imfuyo koIsrayeli; mina ngiyinzuzo yabo.
“‘Ni ne kaɗai zan zama abin gādon da firistoci za su kasance da shi. Kada ka ba su wani mallaka a Isra’ila; zan zama mallakarsu.
29 Bona bazakudla umnikelo wokudla, lomnikelo wesono, lomnikelo wecala, lakho konke okwehlukanisiweyo koIsrayeli kuzakuba ngokwabo.
Za su ci hadaya ta gari, hadaya don zunubi da hadaya don laifi; da kuma kowane keɓaɓɓen abu a Isra’ila da za a ba wa Ubangiji zai zama nasu.
30 Lokuqala kwazo zonke izithelo zokuqala zakho konke, lawo wonke umnikelo wakho konke, kuyo yonke iminikelo yenu, kuzakuba ngokwabapristi; lokuqala kwenhlama yenu likunike umpristi, ukuhlalisa isibusiso phezu kwendlu yakho.
Mafi kyau na nunan farinku da kuma dukan kyautanku na musamman za su zama na firistoci. Za ku ba su rabo na fari na ɓarzajjen hatsinku saboda albarka ta kasance a gidanku.
31 Abapristi kabayikudla loba kuyini okuzifeleyo, loba okudatshuliweyo, okwenyoni kumbe okwenyamazana.
Firistoci ba za su ci mushen tsuntsu ko na dabba ba, ba kuwa za su ci waɗanda namun jeji suka kashe ba.

< UHezekheli 44 >