< UHezekheli 38 >

1 Ilizwi leNkosi laselifika kimi lisithi:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Ndodana yomuntu, misa ubuso bakho bumelene loGogi, ilizwe likaMagogi, isiphathamandla esiyinhloko yeMesheki leThubhali, uprofethe umelene laye,
“Ɗan mutum, ka fuskanci Gog, na ƙasar Magog, babban sarkin Meshek da Tubal; ka yi annabci a kansa
3 uthi: Itsho njalo iNkosi uJehova: Khangela, ngimelene lawe, wena Gogi isiphathamandla esiyinhloko yeMesheki leThubhali.
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
4 Njalo ngizakuphendula, ngifake izingwegwe emihlathini yakho, ngikukhuphe wena lebutho lakho lonke, amabhiza labagadi bamabhiza, bonke begqoke bephelele, ixuku elikhulu elilomhawu lesihlangu, bonke bephethe izinkemba.
Zan juyar da kai, in sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in fitar da kai tare da dukan sojojinka, dawakanka, mahayan dawakanka saye da makamai, da kuma jama’a mai girma masu riƙe da garkuwoyi manya da ƙanana, dukansu da takuba a zāre.
5 IPerisiya, iEthiyophiya, lePuti ilabo; bonke belesihlangu lengowane.
Farisa, Kush da Fut za su kasance tare da su, duka riƙe da garkuwoyi da hulunan kwano,
6 IGomeri lamaviyo ayo wonke, indlu kaTogarima ezinhlangothini zenyakatho, lamaviyo ayo wonke; abantu abanengi kanye lawe.
haka ma Gomer da dukan sojojinsa, da Bet Togarma daga can arewa tare da dukan sojojinsa, al’ummai masu yawa tare da kai.
7 Lunga, uzilungisele, wena lexuku lakho lonke elibuthene kuwe, ube ngumgcini wabo.
“‘Ka shirya; ka kintsa, kai da dukan jama’arka da suka taru kewaye da kai, ka kuma zama mai ba su umarni.
8 Emva kwensuku ezinengi uzahanjelwa; ekucineni kweminyaka uzakuza elizweni elabuyiswa enkembeni, elabuthwa ezizweni ezinengi, ngasezintabeni zakoIsrayeli, ezaziyincithakalo njalonjalo. Kodwa selikhutshwe emazweni, njalo bazahlala bevikelekile bonke.
Bayan kwanaki masu yawa za a kira ka. A shekaru masu zuwa za ka kai hari a ƙasar da ta farfaɗo daga yaƙi, wadda aka tattara mutanenta daga al’ummai masu yawa zuwa duwatsun Isra’ila, dā kango ne sosai. An fitar da su daga al’ummai, yanzu kuwa dukansu suna zama lafiya.
9 Khona uzakwenyuka, uze njengesiphepho, ube njengeyezi lokusibekela umhlaba, wena, lawo wonke amaviyo akho, labantu abanengi kanye lawe.
Kai da dukan sojojinka da kuma al’ummai masu yawa da suke tare da kai za ku haura, kuna cin gaba kamar hadari; za ku zama kamar girgijen da yake rufewa ƙasa.
10 Itsho njalo iNkosi uJehova: Kuzakuthi-ke ngalolosuku kuvele izinto enhliziyweni yakho, unakane icebo elibi,
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, tunani zai shiga cikin zuciyarka za ka kuma ƙirƙiro muguwar dabara.
11 uthi: Ngizakwenyukela elizweni lemizi engabiyelwanga; ngizakuya kwabalokuthula, abahlezi bevikelekile, bonke behlezi bengelamduli, bengelamgoqo lezivalo,
Za ka ce, “Zan kai hari wa ƙasar da ƙauyukanta ba su da katanga; zan fāɗa wa mutanen da suke zamansu kurum cikin salama, dukansu suna zama babu katanga babu ƙofofi ko ƙyamare.
12 ukuphanga impango, lokubamba okubanjiweyo; ukuphendulela isandla sakho phezu kwezindawo ezingamanxiwa esezihlalwa, laphezu kwabantu ababuthwe ezizweni, abazuze izifuyo lempahla, abahlala enkabeni yelizwe.
Zan washe in kwashe ganima in kuma juye hannuna gāba da kufai da aka sāke zaunar da mutanen da aka tattara daga al’ummai, masu yawan shanu da kayayyaki, masu zama a tsakiyar ƙasa.”
13 IShebha, leDedani, labathengiselani beTarshishi, lazo zonke izilwane zayo ezintsha, kuzakuthi kuwe: Ufike yini ukuzaphanga impango? Ixuku lakho ulibuthanisele ukubamba okubanjiweyo yini, ukususa isiliva legolide, ukuthatha izifuyo lempahla, ukuphanga impango enkulu yini?
Sheba da Dedan da’yan kasuwar Tarshish da dukan ƙauyukanta za su ce maka, “Ka zo ka kwashe ganima ne? Ka tattara jama’arka don ka yi waso, ka kuma kwashe azurfa da zinariya, ka kwashe shanu da kayayyaki ka kuma ƙwace ganima mai yawa?”’
14 Ngakho, profetha, ndodana yomuntu, uthi kuGogi: Itsho njalo iNkosi uJehova: Ngalolosuku, mhla abantu bami uIsrayeli behlezi ngokuvikeleka, kawuyikukwazi yini?
“Saboda haka ɗan mutum, ka yi annabci ka ce wa Gog, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, sa’ad da mutanena Isra’ila suna zaman lafiya, ba za ka sani ba?
15 Khona uzakuza uvele endaweni yakho, ezinhlangothini zenyakatho, wena, labantu abanengi kanye lawe, bonke begade amabhiza, ixuku elikhulu, lebutho elilamandla.
Za ka zo daga wurinka a can arewa, kai da al’ummai masu yawa tare da kai, dukansu suna hawan dawakai, jama’a mai yawa, babbar runduna.
16 Njalo uzakwenyuka umelane labantu bami uIsrayeli, njengeyezi elisibekela umhlaba. Kuzakwenzeka ekucineni kwezinsuku, ngikuse umelane lelizwe lami, ukuze izizwe zingazi, lapho ngizangcweliswa kuwe, wena Gogi, phambi kwamehlo azo.
Za ka ci gaba a kan mutanena Isra’ila kamar yadda girgijen yakan rufe ƙasa. A kwanaki masu zuwa, ya Gog, zan kawo ka, ka yi yaƙi da ƙasata, domin al’ummai su san ni sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinka a gabansu.
17 Itsho njalo iNkosi uJehova: Unguwe yini engakhuluma ngaye ensukwini zasendulo ngesandla sezinceku zami abaprofethi bakoIsrayeli, abaprofetha ngalezonsuku okweminyaka eminengi ukuthi ngizakuletha umelane labo?
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba kai ba ne na yi magana da kai a kwanakin dā ta wurin bayina annabawan Isra’ila? A lokacin sun yi annabci shekaru masu yawa cewa zan kawo ka, ka yaƙe su.
18 Kuzakuthi-ke ngalolosuku mhla uGogi ezakuza ukumelana lelizwe lakoIsrayeli, itsho iNkosi uJehova, ulaka lwami luvuke ebusweni bami.
Ga abin da zai faru a ranar. Sa’ad da Gog ya fāɗa wa ƙasar Isra’ila, fushina mai zafi zai ƙuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
19 Ngoba ebukhweleni bami lemlilweni wolaka lwami ngathi: Isibili ngalolosuku kuzakuba khona ukuzamazama okukhulu elizweni lakoIsrayeli.
Cikin kishina da hasalata mai zafi zan furta cewa a wannan lokaci za a yi babbar girgizar ƙasa a ƙasar Isra’ila.
20 Ukuze kuthuthumele ebukhoneni bami izinhlanzi zolwandle, lenyoni zamazulu, lenyamazana zeganga, lazo zonke izinto ezihuquzelayo, ezihuquzela emhlabathini, labo bonke abantu abasebusweni bomhlaba, lezintaba zizawiselwa phansi, lamawa azawela phansi, lawo wonke umduli uwele emhlabathini.
Kifin teku, tsuntsayen sarari, namun jeji, kowace halitta mai rarrafe da kuma dukan mutane a duniya za su yi rawar jiki a gabana. Za a tumɓuke duwatsu, a ragargaza tsaunuka, kuma kowane bango zai fāɗi ƙasa.
21 Njalo ngizabiza inkemba imelane laye kuzo zonke izintaba zami, itsho iNkosi uJehova; inkemba yalowo lalowomuntu izamelana lomfowabo.
Zan kira takobi a kan Gog a dukan duwatsuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Kowane takobin mutum zai yi gāba da ɗan’uwansa.
22 Futhi ngizamehlulela ngomatshayabhuqe wesifo langegazi; nginise phezu kwakhe, laphezu kwamaxuku akhe, laphezu kwezizwe ezinengi ezilaye, izulu elikhukhulayo, lamatshe esiqhotho, umlilo, lesolufa.
Zan yi hukunci a kansa da annoba da kuma zub da jini; zan yi ruwa mai yawa da ƙanƙara da kibiritu mai cin wuta a kansa da a kan sojojinsa da kuma a kan al’ummai masu yawa da suke tare da shi.
23 Ngalokho ngizazikhulisa ngizingcwelise, ngaziwe phambi kwamehlo ezizwe ezinengi; khona bazakwazi ukuthi ngiyiNkosi.
Ta haka zan nuna girmana da kuma tsarkina, zan sanar da kaina a gaban al’ummai masu yawa. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’

< UHezekheli 38 >