< UHezekheli 37 >

1 Isandla seNkosi sasiphezu kwami, sangikhupha ngoMoya weNkosi, sangibeka phakathi kwesihotsha esasigcwele amathambo.
Hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma fitar da ni ta wurin Ruhun Ubangiji ya sa ni a tsakiyar kwarin; yana cike da ƙasusuwa.
2 Yangidlulisa kuwo ngibhoda inhlangothi zonke; khangela-ke, ayemanengi kakhulu ebusweni besihotsha, njalo khangela, ayomile kakhulu.
Ya sa na kai na komo a ciki, na kuma ga ƙasusuwa masu girma da yawa a ƙasar kwarin, ƙasusuwan da suka bushe ƙwarai.
3 Yasisithi kimi: Ndodana yomuntu, amathambo la angaphila yini? Ngasengisithi: Nkosi Jehova, nguwe owaziyo.
Sai ya tambaye ni cewa, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa za su iya rayu?” Ni kuwa na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai kaɗai ka sani.”
4 Yasisithi kimi: Profetha phezu kwalamathambo, uthi kiwo: Lina mathambo omileyo, zwanini ilizwi leNkosi.
Sai ya ce mini, “Ka yi wa waɗannan ƙasusuwa annabci ka ce musu, ‘Busassun ƙasusuwa, ku ji maganar Ubangiji!
5 Itsho njalo iNkosi uJehova kula amathambo: Khangelani, ngizakwenza umoya ungene kini, liphile.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce wa waɗannan ƙasusuwa. Zan sa numfashi ya shiga muku, za ku kuwa rayu.
6 Ngibeke imisipha phezu kwenu, ngivuselele inyama phezu kwenu, ngilembese ngesikhumba, ngifake umoya kini, liphile. Khona lizakwazi ukuthi ngiyiNkosi.
Zan harhaɗa muku jijiyoyi in sa muku tsoka in kuma rufe ku da fata; zan sa numfashi a cikinku, za ku kuwa rayu. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
7 Ngasengiprofetha njengokulaywa kwami; kwasekusiba lomsindo ngisaprofetha, khangela-ke ukunyikinyeka, amathambo asesondelelana, ithambo kuthambo lalo.
Saboda haka sai na yi annabci yadda aka umarce ni. Da nake annabcin, sai aka ji motsi, ƙarar girgiza, sai ƙasusuwan suka harhaɗu, ƙashi ya haɗu da ƙashi.
8 Ngasengibona, khangela-ke, kwakulemisipha phezu kwawo, yavela inyama, lesikhumba sawasibekela ngaphezulu; kodwa kwakungelamoya kiwo.
Na duba, sai ga jijiyoyi da nama suka bayyana a kansu fata kuma ta rufe su, amma ba numfashi a cikinsu.
9 Yasisithi kimi: Profetha emoyeni, profetha ndodana yomuntu, uthi emoyeni: Itsho njalo iNkosi uJehova: Woza uvela emimoyeni emine, wena moya, uphefumulele kulaba ababuleweyo ukuze baphile.
Sa’an nan ya ce mini, “Ka yi annabci wa numfashi; ka yi annabci, ɗan mutum, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka fito daga kusurwoyi huɗu, ya numfashi, ka kuma numfasa cikin waɗannan matattu, don su rayu.’”
10 Ngasengiprofetha njengalokho yayingilayile; umoya wasungena kiwo, aphila, ema ngenyawo zawo, ibutho elikhulu kakhulukazi.
Saboda haka na yi annabci yadda aka umarce ni, sai numfashi ya shiga musu; suka rayu suka kuma miƙe tsaye a ƙafafunsu babbar runduna ce ƙwarai.
11 Yasisithi kimi: Ndodana yomuntu, la amathambo ayindlu yonke kaIsrayeli. Khangela, bathi: Amathambo ethu omile, lethemba lethu libhubhile, siqunyiwe ngokwethu.
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa su ne dukan gidan Isra’ila. Suna cewa, ‘Ƙasusuwanmu sun bushe, sa zuciyarmu duk ya tafi; an share mu ƙaf.’
12 Ngakho profetha uthi kubo: Itsho njalo iNkosi uJehova: Khangelani, ngizavula amangcwaba enu, ngilikhuphule emangcwabeni enu, lina bantu bami, ngilise elizweni lakoIsrayeli.
Saboda haka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ya mutanena, zan buɗe kaburburanku in fitar da ku daga cikinsu; zan mai da ku ƙasar Isra’ila.
13 Khona lizakwazi ukuthi ngiyiNkosi, lapho ngivula amangcwaba enu, ngilikhuphule emangcwabeni enu, lina bantu bami.
Sa’an nan ku, mutanena, za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na buɗe kaburburanku na fitar da ku daga cikinsu.
14 Besengifaka umoya wami kini, liphile, besengilibeka elizweni lenu; khona lizakwazi ukuthi mina Nkosi ngikhulumile, ngakwenza, itsho iNkosi.
Zan sa Ruhuna a cikinku za ku kuwa rayu, zan kuma zaunar da ku a ƙasarku. Sa’an nan za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata, in ji Ubangiji.’”
15 Ilizwi leNkosi lafika kimi futhi lisithi:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
16 Wena-ke ndodana yomuntu, zithathele intonga eyodwa, ubhale phezu kwayo uthi: EkaJuda, leyabantwana bakaIsrayeli abangane bakhe; ubusuthatha enye intonga, ubhale phezu kwayo uthi: EkaJosefa, intonga kaEfrayimi, layo yonke indlu kaIsrayeli abangane bakhe.
“Ɗan mutum, ka ɗauki sanda ka rubuta a kansa, ‘Na Yahuda da Isra’ilawan da suke tare da shi.’ Sa’an nan ka ɗauki wani sanda, ka rubuta a kansa, ‘Sandan Efraim, na Yusuf da dukan gidan Isra’ilan da suke tare da shi.’
17 Ubusuzisondeza, enye kwenye kuwe, zibe yintonga eyodwa; njalo zizakuba ngeyodwa esandleni sakho.
Ka haɗa su su zama sanda guda saboda su kasance ɗaya a hannunka.
18 Lalapho abantwana babantu bakini bekhuluma kuwe besithi: Kawuyikusitshela yini ukuthi lezi ziyini kuwe?
“In mutanen ƙasarka suka tambaye ka cewa, ‘Ba za ka faɗa mana abin da kake nufi da wannan ba?’
19 Tshono kubo: Itsho njalo iNkosi uJehova: Khangela, ngizathatha intonga kaJosefa, esesandleni sikaEfrayimi, lezizwe zakoIsrayeli abangane bakhe, ngizibeke kuyo, kuyo intonga kaJuda, ngizenze zibe yintonga eyodwa, zibe ngeyodwa esandleni sami.
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, Zan ɗauki sandan Yusuf, wanda yake a hannun Efraim, da na kabilan Isra’ilawan da suke tare da shi, in haɗa shi da sandan Yahuda, in mai da su sanda guda, za su kuwa zama ɗaya a hannuna.’
20 Njalo izintonga obhale kizo zizakuba sesandleni sakho phambi kwamehlo abo.
Ka riƙe sandunan da ka yi rubutun a gabansu
21 Ubususithi kubo: Itsho njalo iNkosi uJehova: Khangelani, ngizathatha abantwana bakoIsrayeli phakathi kwezizwe, abaye kizo, ngibabuthe inhlangothi zonke, ngibalethe elizweni labo;
ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan fitar da Isra’ilawa daga al’ummai inda suka tafi. Zan tattara su daga dukan kewaye in komo da su ƙasarsu.
22 ngibenze babe yisizwe esisodwa elizweni phezu kwezintaba zakoIsrayeli; njalo inkosi eyodwa izakuba yinkosi yabo bonke; njalo kabasayikuba yizizwe ezimbili, kabasayikwehlukaniswa babe yimibuso emibili futhi.
Zan mai da su al’umma ɗaya a cikin ƙasar, a kan duwatsun Isra’ila. Za a kasance da sarki guda a kan dukansu ba za su ƙara zama al’ummai biyu ko su rabu su zama masarautai biyu ba.
23 Kabasayikuzingcolisa ngezithombe zabo, langamanyala abo, langasiphi seziphambeko zabo; kodwa ngizabasindisa baphume kuzo zonke indawo zabo zokuhlala, abona kizo, ngibahlambulule. Ngalokho bazakuba ngabantu bami, lami ngibe nguNkulunkulu wabo.
Ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumaka da mugayen siffofi ko kuma da wani daga laifofinsu ba, gama zan cece su daga dukan zunubinsu na ridda, zan kuma tsarkake su. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu.
24 Njalo inceku yami uDavida izakuba yinkosi phezu kwabo; labo bonke bazakuba lomalusi munye; futhi bazahamba kuzahlulelo zami, bagcine izimiso zami, bazenze.
“‘Bawana Dawuda zai zama sarki a kansu, dukansu kuwa za su kasance da makiyayi guda. Za su bi dokokina su kuma kiyaye ƙa’idodina.
25 Bahlale elizweni engalinika inceku yami uJakobe, ababehlala kulo oyihlo, yebo, bazahlala kulo, bona, labantwana babo, labantwana babantwana babo, kuze kube phakade. Futhi uDavida inceku yami uzakuba yisiphathamandla sabo kuze kube phakade.
Za su zauna a ƙasar da na ba wa bawana Yaƙub, ƙasar da kakanninsu suka zauna. Su da’ya’yansu da’ya’ya’ya’yansu za su zauna a can har abada, kuma Dawuda bawana zai zama sarkinsu har abada.
26 Futhi ngizakwenza isivumelwano sokuthula labo; sizakuba yisivumelwano esilaphakade labo; ngibamise, ngibandise, ngibeke indawo yami engcwele phakathi kwabo kuze kube phakade.
Zan yi alkawarin salama da su; zai zama madawwamin alkawari. Zan kafa su in ƙara yawansu, zan kuma sa wuri mai tsarkina a cikinsu har abada.
27 Ithabhanekele lami lalo lizakuba kubo, njalo ngizakuba nguNkulunkulu wabo, labo bazakuba ngabantu bami.
Mazaunina zai kasance da su; zan kuwa zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
28 Lezizwe zizakwazi ukuthi mina Nkosi ngenza uIsrayeli abe ngcwele, nxa indawo yami engcwele izakuba phakathi kwabo kuze kube phakade.
Sa’an nan al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji na mai da Isra’ila mai tsarki, sa’ad da wuri mai tsarkina yana a cikinsu har abada.’”

< UHezekheli 37 >