< UHezekheli 34 >

1 Ilizwi leNkosi laselifika kimi lisithi:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Ndodana yomuntu, profetha umelene labelusi bakoIsrayeli, profetha uthi kubo: Itsho njalo iNkosi uJehova kubelusi: Maye kubelusi bakoIsrayeli abazelusayo bona! Abelusi bebengayikuzelusa izimvu yini?
“Ɗan mutum, ka yi annabci a kan makiyayan Isra’ila; ka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton makiyayan Isra’ila waɗanda suke kula da kansu ne kawai! Ashe, bai kamata makiyaya ne su lura da tumaki ba?
3 Lidla amanono, lizigqokise ngoboya, lihlabe ezinonileyo, umhlambi kaliwelusi.
Kuna cin kitsensu, kuna yi wa kanku tufafi da gashinsu, kukan yanka turkakkun, amma ba ku yi kiwon tumakin ba.
4 Ezibuthakathaka kaliziqinisanga, lezigulayo kalizelaphanga, lezephukileyo kalizibophanga, lebezixotshiwe kalizibuyisanga, lebezilahlekile kalizidinganga; kodwa ngamandla langesihluku lizibusile.
Ba ku ƙarfafa marasa ƙarfi ba, ko ku warkar da marasa lafiya ko ku ɗaura waɗanda suka ji rauni. Ba ku dawo da waɗanda suka yi makuwa ko ku nemi waɗanda suka ɓace ba. Amma sai kuka mallake su ƙarfi da yaji.
5 Ngokunjalo zahlakazeka ngoba kungelamelusi; zaba yikudla kuzo zonke izilo zeganga, lapho zihlakazekile.
Saboda haka suka warwatse domin babu makiyayi, kuma da suka warwatsu sai suka zama abincin namun jeji.
6 Izimvu zami zazulazula kuzo zonke izintaba, laphezu kwalo lonke uqaqa oluphakemeyo; yebo umhlambi wami wawuhlakazeke phezu kobuso bonke bomhlaba, njalo kungekho ozidingayo, kungekho ozibhudulayo.
Tumakina suna ta yawo a kan dukan duwatsu da kuma kowane tudu. Sun watsu a dukan duniya, kuma ba wanda ya neme su.
7 Ngakho, lina belusi, zwanini ilizwi leNkosi.
“‘Saboda haka, ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
8 Kuphila kwami, itsho iNkosi uJehova, isibili, ngoba umhlambi wami usube yimpango, lomhlambi wami usube yikudla kwaso sonke isilo seganga, ngoba kungelamelusi, labelusi bami bengazidinganga izimvu zami, kodwa abelusi bezelusile bona, bengazelusanga izimvu zami;
Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin tumaki sun rasa makiyayi ta haka aka washe su suka kuma zama abincin dukan namun jeji, kuma domin makiyayana ba su nemi tumakina ba amma suka kula da kansu a maimakon tumakina,
9 ngakho, lina belusi, zwanini ilizwi leNkosi.
saboda haka, ya ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
10 Itsho njalo iNkosi uJehova: Khangela, ngimelane labelusi, ngizabiza umhlambi wami esandleni sabo, ngibenze bayekele ukwelusa umhlambi, ukuthi abelusi bangabuyi bazeluse bona; ngiwophule umhlambi wami emlonyeni wabo, ukuze ungabi yikudla kwabo.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da makiyaya kuma zan nemi hakkin tumakina daga gare su. Zan hana su yin kiwon tumakin don kada makiyayan su ƙara yin kiwon kansu. Zan ƙwace tumakina daga bakunansu, ba kuwa za su ƙara zama abincinsu.
11 Ngoba itsho njalo iNkosi uJehova: Khangela, mina, ngitsho mina ngizafuna izimvu zami, ngizidinge.
“‘Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan nemi tumakina.
12 Njengomalusi edinga umhlambi wakhe ngosuku ephakathi kwezimvu zakhe ezihlakazekileyo, ngokunjalo ngizadinga izimvu zami, ngizophule kuzo zonke izindawo lapho ezihlakazekele khona ngosuku lweyezi lolomnyama.
Kamar yadda makiyayi yakan lura da tumakinsa da suka watse sa’ad da yake tare da su, haka zan lura da tumakina. Zan cece su daga dukan wuraren da aka watsar da su a ranar gizagizai da baƙin duhu.
13 Ngizazikhupha ebantwini, ngizibuthe emazweni, ngizise elizweni lazo, ngizeluse phezu kwezintaba zakoIsrayeli ngasemifuleni lakuzo zonke indawo zokuhlala zelizwe.
Zan dawo da su daga al’ummai in kuma tattara su daga ƙasashe, zan kuma kawo su cikin ƙasarsu. Zan yi kiwonsu a kan duwatsun Isra’ila, a maɓulɓulai da kuma cikin wuraren zamansu a ƙasar.
14 Ngizazelusa edlelweni elivundileyo, lesibaya sazo sizakuba sezintabeni eziphakemeyo zakoIsrayeli. Zizalala lapho esibayeni esihle, zidle edlelweni elihle ezintabeni zakoIsrayeli.
Zan kula da su a wurin kiwo mai kyau, kuma ƙwanƙolin duwatsun Isra’ila ne zai zama wurin kiwonsu. Za su kwanta a wurin kiwo mai kyau, a can kuma za su yi kiwo a wurin kiwo mai kyau a kan duwatsun Isra’ila.
15 Mina ngizawelusa umhlambi wami, mina ngiwulalise phansi, itsho iNkosi uJehova.
Ni kaina zan lura da tumakina in kuma sa su kwanta, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
16 Ngizadinga ezilahlekileyo, ngibuyise ezixotshiweyo, ngibophe ezephukileyo, ngiqinise ezigulayo; kodwa ezinonileyo leziqinileyo ngizazibhubhisa, ngizeluse ngesahlulelo.
Zan nemi ɓatattuna in kuma dawo da waɗanda suka yi makuwa. Zan ɗaura raunin waɗanda suka ji ciwo in kuma ƙarfafa marasa ƙarfi, amma zan hallaka ƙarfafa da kuma masu ƙiba. Zan yi kiwo tumaki da adalci.
17 Lina-ke, mhlambi wami, itsho njalo iNkosi uJehova: Khangela, ngizakwahlulela phakathi kwemvu lemvu, phakathi kwezinqama lezimpongo.
“‘Game da ku, tumakina, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya, da tsakanin raguna da awaki.
18 Kuyinto encane kini yini ukuthi lidle edlelweni elihle, linyathelele phansi ngenyawo zenu insali yamadlelo enu, lokuthi linathe amanzi acengekileyo, kodwa lidunge aseleyo ngenyawo zenu?
Bai isa ba a ce kun yi kiwo a wuri mai kyau? Sai kun tattake sauran wurin kiwonku da ƙafafunku tukuna? Bai isa ba a ce kun sha ruwa mai tsabta? Sai kun kuma gurɓata sauran da ƙafafunku?
19 Kodwa umhlambi wami udla lokhu elikunyathele ngenyawo zenu, wanatha lokho elikudunge ngenyawo zenu.
Dole ne tumakina su ci abin da kuka tattake su kuma sha abin da kuka gurɓata da ƙafafunku?
20 Ngakho itsho njalo iNkosi uJehova kuzo: Khangelani, mina, ngitsho mina ngizakwahlulela phakathi kwezimvu ezinonileyo lezimvu ezicakileyo.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce musu, duba, ni kaina zan hukunta tsakanin turkakkun tumaki da ramammun tumaki.
21 Ngoba lisunduza ngomhlubulo langehlombe, lihlabe zonke ezigulayo ngezimpondo zenu, lize lizihlakazele ngaphandle;
Domin kun tunkuɗe marasa ƙarfi da kafaɗunku, kun kuma tunkuye su da ƙahoninku sai da suka gudu,
22 ngakho ngizasindisa umhlambi wami, njalo kawusayikuba yimpango; ngahlulele phakathi kwemvu lemvu.
zan cece tumakina ba za su ƙara zama ganima ba. Zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya.
23 Ngimise umelusi oyedwa phezu kwazo, azeluse, inceku yami uDavida; yena uzazelusa, yena abe ngumelusi wazo.
Zan sa musu makiyaya guda, bawana Dawuda, zai kuwa lura da su; zai kula da su ya kuma zama makiyayinsu.
24 Mina-ke Nkosi ngizakuba nguNkulunkulu wazo, lenceku yami uDavida ibe yisiphathamandla phakathi kwazo. Mina Nkosi ngikhulumile.
Ni Ubangiji zan zama Allahnsu, bawana kuma Dawuda zai zama yerima a cikinsu. Ni Ubangiji na faɗa.
25 Njalo ngizakwenza lazo isivumelwano sokuthula, ngenze izilo ezimbi ziphele elizweni; njalo zizahlala zivikelekile enkangala, zilale emahlathini.
“‘Zan yi alkawarin salama da su in kuma kawar wa ƙasar da namun jeji domin su zauna a hamada su kuma kwana a kurmi lafiya lau.
26 Futhi ngizakwenza zona lezindawo ezihanqe uqaqa lwami kube yisibusiso; ngenze umkhizo wehle ngesikhathi sawo, kuzakuba lemikhizo yesibusiso.
Zan albarkace su in kuma sa tuduna kewaye da su. Zan zubo yayyafi a lokacinsa; za a kasance da yayyafin albarka.
27 Lesihlahla sasendle sizathela izithelo zaso, lomhlaba uveze isivuno sawo; njalo zizakuba ngezivikelekileyo elizweni lazo, zazi ukuthi ngiyiNkosi, nxa sengephule izikeyi zejogwe lazo, ngizophule esandleni salabo abazisebenzisayo.
Itatuwan gona za su ba da’ya’yansu, ƙasa kuma za tă ba da amfaninta; mutane za su zauna lafiya a ƙasarsu. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na karya karkiyarsu, na cece su daga hannun waɗanda suka bautar da su.
28 Njalo kazisayikuba yimpango yabezizwe, njalo izilo zelizwe kazisayikuzidla; kodwa zizahlala zivikelekile, njalo kakukho okungazethusa.
Ba za su ƙara zama ganimar al’ummai ba, ba kuwa namun jeji za su cinye su ba. Za su zauna lafiya, kuma babu wani da zai sa su ji tsoro.
29 Njalo ngizazivusela isilimo esilebizo njalo kazisayikususwa yindlala elizweni, kazisayikuthwala ihlazo labezizwe.
Zan tanada musu ƙasar da aka sani don hatsinta, ba za su kuma ƙara zama abin da yunwa za tă fara musu a ƙasa ba ko su sha zargin sauran al’ummai.
30 Ngalokho zizakwazi ukuthi mina Nkosi, uNkulunkulu wazo, ngilazo, lokuthi zona, indlu kaIsrayeli, zingabantu bami, itsho iNkosi uJehova.
Sa’an nan za su san cewa ni, Ubangiji Allahnsu, ina tare da su kuma cewa su, gidan Isra’ila, mutanena ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
31 Lina-ke, mhlambi wami, mhlambi wedlelo lami, lingabantu; mina nginguNkulunkulu wenu, itsho iNkosi uJehova.
Ku tumakina, tumakin wurin kiwona, mutanena ne, ni kuwa Allahnku ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”

< UHezekheli 34 >