< UHezekheli 13 >
1 Ilizwi leNkosi laselifika kimi lisithi:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Ndodana yomuntu, profetha umelene labaprofethi bakoIsrayeli abaprofethayo, utsho kubo abaprofetha okwenhliziyo yabo: Zwanini ilizwi leNkosi.
“Ɗan mutum, yi annabci a kan annabawan Isra’ila waɗanda suke annabci yanzu. Ka faɗa wa waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji!
3 Itsho njalo iNkosi uJehova: Maye kubaprofethi abayizithutha, abalandela umoya wabo, abangabonanga lutho!
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake faɗa, Kaiton wawaye annabawan da suke bin ruhunsu kuma ba su ga kome ba!
4 Israyeli, abaprofethi bakho banjengamakhanka emanxiweni.
Annabawanki, ya Isra’ila, suna kama da diloli a kufai.
5 Kalenyukelanga ezikhexeni, kumbe libiyele indlu kaIsrayeli uthango ukuze ime empini ngosuku lweNkosi.
Ba ku haura don ku rushe katanga don ku gyara gidan Isra’ila saboda ya tsaya daram a yaƙi a ranar Ubangiji ba.
6 Babone okuyize, lokuvumisa kwamanga, abathi: INkosi ithi; kanti iNkosi ingabathumanga; bathemba ekuqinisweni kwelizwi.
Wahayoyinsu ƙarya ne suna yin dubansu na ƙarya ne. Sukan ce, Ubangiji ya furta, alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba; duk da haka sukan sa zuciya ga cikawar maganarsu.
7 Kalibonanga yini umbono oyize njalo likhulume ukuvumisa okungamanga yini? Kanti lithi: INkosi ithi; kodwa mina ngingakhulumanga.
Ba ku ga wahayin ƙarya kuka kuma faɗa yin duban ƙarya sa’ad da kuka ce, “Ubangiji ya furta,” ko da yake bai yi magana ba?
8 Ngakho itsho njalo iNkosi uJehova: Ngoba likhulume okuyize, labona amanga, ngakho, khangelani, ngimelene lani, itsho iNkosi uJehova.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa saboda maganganunku na ƙarya da wahayinku na ƙarya, ina gāba da ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Njalo isandla sami sizakuba phezu kwabaprofethi ababona okuyize, labavumisa amanga; kabayikuba senhlanganweni yabantu bami, futhi kabayikubhalwa embhalweni wendlu yakoIsrayeli, futhi kabayikungena elizweni lakoIsrayeli; njalo lizakwazi ukuthi ngiyiNkosi uJehova.
Hannuna zai yi gāba da annabawan da suke ganin wahayin ƙarya suna kuma yin duban ƙarya. Ba za su kasance cikin taron mutanena ba, ba kuwa za a rubuta su a littafin gidan Isra’ila ba, ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
10 Ngoba, yebo ngoba beduhise abantu bami, besithi: Ukuthula; khona kungelakuthula; kwathi omunye wakha umduli ongaqinanga, khangela-ke, abanye bawubhada ngodaka olungalunganga.
“‘Domin sun ɓad da mutanena, suna cewa, “Salama,” sa’ad da ba salama, kuma saboda, sa’ad da ana gina katanga marar ƙarfi, sukan shafe ta da farar ƙasa,
11 Tshono kulabo abawubhada ngekalaga ukuthi uzakuwa. Kuzakuba khona izulu elikhukhulayo; lawe, matshe amakhulu esiqhotho, uzakuwa, lomoya wesiphepho uwuqhekeze.
saboda haka ka faɗa wa waɗanda suka shafe da farar ƙasa cewa za tă fāɗi. Ruwan sama zai sauko da rigyawa, zan kuma aika da ƙanƙara, kuma babbar iska za tă ɓarke.
12 Khangela-ke, nxa umduli usuwile, kakuyikutshiwo yini kini ukuthi: Lungaphi udaka elalibhade ngalo?
Sa’ad da katangar ta fāɗi, mutane ba za su tambaye ku ba cewa, “Ina shafen farar ƙasar da kuka yi mata?”
13 Ngakho itsho njalo iNkosi uJehova: Ngizawuqhekeza ngomoya wesiphepho ekuthukutheleni kwami, kube khona izulu elikhukhulayo ngolaka lwami, lamatshe esiqhotho ngentukuthelo yami ukuwuqeda.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a cikin hasalata zan saki babbar iska, kuma cikin fushina zan tura ƙanƙara kuma rigyawan ruwan sama zai sauko da fushin hallaka.
14 Ngokunjalo ngizadiliza umduli eliwubhade ngekalaga, ngiwuwisele emhlabathini, ukuze kwembuleke isisekelo sawo, uwe; njalo lizaqedwa phakathi kwawo; njalo lizakwazi ukuthi ngiyiNkosi.
Zan rushe katangar da kuka shafe da farar ƙasa zan baje ta har ƙasa saboda tushenta zai tsaya tsirara. Sa’ad da ta fāɗi, za a hallaka ku a cikinta; kuma za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Ngokunjalo ngizaphelelisa ulaka lwami emdulini laphezu kwalabo abawubhade ngekalaga, besengisithi kini: Umduli kawusekho, lalabo abawubhadayo kabakho;
Ta haka zan aukar wa katangar da hasalata da kuma a kan waɗanda suka yi shafenta da farar ƙasa. Zan ce muku, “Katangar ta fāɗi haka kuma mutanen da suka shafe ta da farar ƙasa,
16 okutsho abaprofethi bakoIsrayeli abaprofetha ngeJerusalema, labayibonela umbono wokuthula, kanti kungelakuthula, itsho iNkosi uJehova.
waɗannan annabawan Isra’ila waɗanda suka yi annabci wa Urushalima suka kuma ga mata wahayin salama sa’ad da ba salama, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”’
17 Wena-ke ndodana yomuntu, misa ubuso bakho bumelene lamadodakazi abantu bakho, abaprofetha okuvela enhliziyweni yabo, uprofethe umelene labo.
“To, ɗan mutum, ka kafa idonka a kan’yan matan mutanenka waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu. Yi annabci a kansu
18 Ubususithi: Itsho njalo iNkosi uJehova: Maye kwabesifazana abathungela izigqizo kuzo zonke izihlakala, abenza izimbombozo ezinde phezu kwekhanda labo bonke ubude, ukuze bazingele imiphefumulo! Lizazingela imiphefumulo yabantu bami yini, njalo lizazigcinela imiphefumulo iphila yini?
ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton matan da suke ɗinka kambuna a hannuwansu suna kuma yin gyale masu tsawo dabam-dabam wa kawunansu don su farauci mutane. Za ku farauci rayukan mutanena ku bar naku?
19 Futhi lizangingcolisa yini phakathi kwabantu bami ngenxa yezandla ezigcwele ibhali, langenxa yezincezu zezinkwa, ukuthi libulale imiphefumulo ebingayikufa, lokuthi ligcine iphila imiphefumulo ebingayikuphila, ngokuqamba amanga kwenu ebantwini bami abalalela amanga?
Kun jawo mini kunya a cikin mutanena don a tafa muku sha’ir da ɗan dunƙulen burodi. Ta wurin yin ƙarya wa mutanena, waɗanda suke jin ƙarairayi, kuka kashe waɗanda bai kamata su mutu ba kuka bar waɗanda ya kamata su mutu.
20 Ngalokho itsho njalo iNkosi uJehova: Khangelani, ngimelene lezigqizo zenu, elizingela ngazo lapho imiphefumulo liyenza iphaphe; ngizaziqamula engalweni zenu, ngiyekele imiphefumulo ihambe, ngitsho imiphefumulo eliyizingelayo liyenza iphaphe.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kambunanku waɗanda kuke farautar mutane da su kamar tsuntsaye don haka zan kuma tsintsinke su daga hannuwanku; zan’yantar da mutanen da kuka farauto kamar tsuntsaye.
21 Lezimbombozo zenu ezinde ngizazidabula, ngophule abantu bami esandleni senu, ukuthi bengasayikuba sesandleni senu ukuba yimpango; njalo lizakwazi ukuthi ngiyiNkosi.
Zan kyakketa gyalenku in ceci mutanena daga hannuwanku, ba za su kuma ƙara zama ganima a hannunku ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji
22 Ngoba lidanisile inhliziyo yolungileyo ngamanga, engingamdabukisanga mina, langoba laqinisa izandla zomubi ukuze angaphenduki endleleni yakhe embi, ukumgcina ephila.
Domin kun karya zuciyar masu adalci da ƙarairayinku, sa’ad da na fitar da su babu damuwa, kuma domin kun ƙarfafa mugaye kada su juye daga mugayen hanyoyinsu su ceci rayukansu,
23 Ngakho kalisayikubona okuyize njalo kaliyikuvumisa okuvunyiswayo; ngoba ngizakophula abantu bami esandleni senu; beselisazi ukuthi ngiyiNkosi.
saboda haka ba za ku ƙara ganin wahayin ƙarya ba, ko ku yi duba. Zan ceci mutanena daga hannuwanku. A sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”