< UHezekheli 12 >
1 Ilizwi leNkosi lafika futhi kimi lisithi:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
2 Ndodana yomuntu, uhlala phakathi kwendlu evukelayo, abalamehlo okubona, kodwa bengaboni, balendlebe zokuzwa, kodwa bengezwa; ngoba bayindlu evukelayo.
ɗan mutum, kana zama a cikin mutane masu tawaye, Suna da idanun gani amma ba sa gani, suna da kunnuwan ji amma ba sa ji, gama’yan tawaye ne.
3 Ngakho, wena ndodana yomuntu, zenzele impahla yokuthunjwa, usuke emini phambi kwamehlo abo, usuke endaweni yakho uye kwenye indawo phambi kwamehlo abo. Mhlawumbe bazabona lanxa beyindlu evukelayo.
“Saboda haka ɗan mutum, ka tattara kayanka don zuwa zaman bauta, ka tashi da rana suna gani ka ƙaura a inda kake zuwa wani wuri. Mai yiwuwa za su gane, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
4 Ubusukhupha impahla yakho emini phambi kwamehlo abo njengempahla yokuthunjwa; wena-ke uzaphuma ntambama phambi kwamehlo abo njengabaphuma besiya ekuthunjweni.
Da rana, yayinda suke kallo, ka fid da kayanka da ka tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma, yayinda suke kallo, ka fita kamar yadda mutane masu tafiyar zaman bauta sukan yi.
5 Uzibhobozele umduli phambi kwamehlo abo, uyikhuphe kiwo.
Yayinda suke kallo, ka huda katanga ka fitar da kayanka daga ciki.
6 Phambi kwamehlo abo uzayithwala emahlombe, uyikhiphe emnyameni, ugubuzele ubuso bakho ukuze ungaboni umhlabathi; ngoba ngikubeke waba yisibonakaliso kuyo indlu yakoIsrayeli.
Ka sa su a kafaɗarka yayinda suke kallo ka kuma fitar da su da dare. Ka rufe fuskarka don kada ka ga ƙasar, gama na mai da kai alama ga gidan Isra’ila.”
7 Ngasengisenza ngokunjalo njengokulaywa kwami: Ngakhupha impahla yami emini, njengempahla yokuthunjwa; kwathi kusihlwa ngazibhobozela umduli ngesandla, ngayikhupha emnyameni ngayithwala emahlombe phambi kwamehlo abo.
Sai na yi kamar yadda aka umarce ni. Da rana na fitar da kayana da na tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma na huda katanga da hannuwana. Na kwashe kayana da dare, na ɗauke su a kafaɗuna yayinda suke kallo.
8 Ekuseni ilizwi leNkosi laselifika kimi lisithi:
Da safe maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
9 Ndodana yomuntu, kayitshongo yini kuwe indlu kaIsrayeli, indlu evukelayo, ukuthi: Wenzani?
“Ɗan mutum, gidan’yan tawayen nan na Isra’ila ba su tambaye ka, ‘Me kake yi ba?’
10 Tshono kubo: Itsho njalo iNkosi uJehova: Lo umthwalo umayelana lesiphathamandla eJerusalema, layo yonke indlu kaIsrayeli ephakathi kwabo.
“Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan abin da Allah ya yi magana a kai ya shafi sarki a Urushalima da kuma dukan gidan Isra’ila waɗanda suke a can.’
11 Wothi: Ngiyisibonakaliso senu; njengoba ngenzile, kuzakwenziwa njalo kubo, bazakuya ekuthunjweni ngokuthunjwa.
Ka ce musu, ‘Ni alama ne a gare ku.’ “Kamar yadda na yi, haka za a yi da su. Za a kai su zaman bauta kamar kamammu.
12 Njalo isiphathamandla esiphakathi kwabo sizayithwala emahlombe emnyameni, siphume; bazabhoboza umduli ukuze bakhuphe ngawo; sizagubuzela ubuso baso, ukuze singaboni umhlabathi ngamehlo.
“Sarkin da yake a cikinsu zai ɗauki kayansa ya saɓa a kafaɗarsa da dare ya tafi, za a huda masa rami a katanga ya fita. Zai rufe fuskarsa don kada yă ga ƙasar.
13 Njalo ngizakwendlala imbule lami phezu kwaso, ukuthi sibanjwe emgibeni wami; ngisilethe eBhabhiloni, ilizwe lamaKhaladiya; kanti kasiyikulibona, loba sizafela khona.
Zan shimfiɗa masa ragata, za a kuwa kama shi da tarkona; zan kawo shi Babiloniya, ƙasar Kaldiyawa, amma ba zai gan ta ba, a can kuwa zai mutu.
14 Labo bonke abasihanqileyo ukuba lusizo lwaso lalo lonke ibutho laso ngizabahlakazela kuwo wonke umoya; ngihwatshe inkemba emva kwabo.
Zan warwatsa dukan waɗanda suke kewaye da shi a dukan fuskokin iska, ma’aikatansa da dukan rundunoninsa, zan fafare su da takobin da aka zāre.
15 Khona bazakwazi ukuthi ngiyiNkosi nxa ngibahlakazela ezizweni, ngibachithachithela emazweni.
“Za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na watsar da su a cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe.
16 Kodwa ngizatshiya amadoda amalutshwana kubo asuke enkembeni, endlaleni, lakumatshayabhuqe wesifo, ukuze balandise ngawo wonke amanyala abo phakathi kwezizwe abazafika kizo; njalo bazakwazi ukuthi ngiyiNkosi.
Amma zan bar kaɗan daga cikinsu su tsere wa takobi, yunwa da annoba, saboda a cikin al’umman da suka tafi su furta dukan ayyukansu masu banƙyama. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
17 Ilizwi leNkosi lafika kimi futhi lisithi:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 Ndodana yomuntu, dlana isinkwa sakho ngokuqhaqhazela, unathe amanzi akho ngokuthuthumela langokukhathazeka.
“Ɗan mutum, ka yi rawar jiki yayinda kake cin abincinka, ka kuma yi makyarkyata don tsoro yayinda kake shan ruwanka.
19 Ubususithi ebantwini belizwe: Itsho njalo iNkosi uJehova ngabahlali beJerusalema, ngelizwe lakoIsrayeli: Bazakudla isinkwa sabo ngokukhathazeka, banathe amanzi abo ngokwesabisayo, ukuze ilizwe labo libe lunxiwa ngokugcwala kwalo ngenxa yodlakela lwabo bonke abahlala kilo.
Ka faɗa wa mutanen ƙasar cewa, ‘Ga abin Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da waɗanda suke zama a Urushalima da kuma cikin ƙasar Isra’ila. Za su ci abincinsu da razana, su sha ruwansu da tsoro, gama za a washe dukan abin da yake ƙasarsu saboda hargitsin dukan waɗanda suna zama a can.
20 Lemizi okuhlalwa kiyo izakuba ngamanxiwa, lelizwe libe yinkangala; njalo lizakwazi ukuthi ngiyiNkosi.
Garuruwan da mutane suna ciki za su zama kufai ƙasar kuma za tă zama kango. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
21 Ilizwi leNkosi laselifika kimi lisithi:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
22 Ndodana yomuntu, kuyini lesisaga elilaso elizweni lakoIsrayeli esithi: Insuku ziyelulwa, lawo wonke umbono uyabhubha?
“Ɗan mutum, mene ne wannan karin magana da kuke da shi a ƙasar Isra’ila mai cewa, ‘Kwanaki suna ta wucewa, wahayi bai gudana ba’?
23 Ngakho batshele uthi: Itsho njalo iNkosi uJehova: Ngizakwenza lesisaga siphele, njalo kabasayikusisebenzisa njengesaga koIsrayeli; kodwa tshono kubo: Kusondele izinsuku lelizwi lawo wonke umbono.
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo ƙarshen wannan karin magana, ba za su ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.’ Ka ce musu, ‘Kwanaki sun gabato da za a tabbatar da kowane wahayi.
24 Ngoba kakusayikuba khona lamunye umbono oyize, lokuvumisa okubutshelezi phakathi kwendlu yakoIsrayeli.
Gama ba za a ƙara ganin wahayin ƙarya ko a yi duba na daɗin baki a cikin mutanen Isra’ila ba.
25 Ngoba mina Nkosi ngizakhuluma; ilizwi engizalikhuluma lizakwenzeka, kalisayikuphuziswa; ngoba ezinsukwini zenu, lina ndlu evukelayo, ngizakhuluma ilizwi, ngilenze, itsho iNkosi uJehova.
Amma Ni Ubangiji zan yi magana abin da na nufa, za tă kuwa tabbata ba tare da jinkiri ba. Gama cikin kwanakinku, kai gidan’yan tawaye, zan cika duk abin da na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
26 Lafika futhi kimi ilizwi leNkosi lisithi:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
27 Ndodana yomuntu, khangela, abendlu yakoIsrayeli bathi: Umbono awubonayo ungowensuku ezinengi, njalo uprofetha ngezikhathi ezikhatshana.
“Ɗan mutum, gidan Isra’ila suna cewa, ‘Wahayin da yake gani na shekaru masu yawa ne nan gaba, yana kuma annabce-annabce game da wani zamani ne can.’
28 Ngakho uthi kubo: Itsho njalo iNkosi uJehova: Kakusayikuphuziswa lelilodwa lamazwi ami, kodwa ilizwi engizalikhuluma lizakwenzeka, itsho iNkosi uJehova.
“Saboda haka ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa ba wata maganata da za tă ƙara yin jinkiri; duk abin da na faɗa zai cika, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”