< U-Eksodusi 32 >

1 Abantu sebebonile ukuthi uMozisi uphuzile ukwehla entabeni, abantu babuthana kuAroni bathi kuye: Sukuma, usenzele onkulunkulu abazahamba phambi kwethu; ngoba uMozisi lo, indoda eyasikhuphula elizweni leGibhithe, kasazi ukuthi yehlelwe yini.
Sa’ad da mutane suka ga Musa ya daɗe bai sauko daga dutse ba, sai suka taru kewaye da Haruna suka ce, “Zo, ka yi mana alloli waɗanda za su yi mana jagora. Game da wannan Musa wanda ya fitar da mu daga Masar dai, ba mu san abin da ya faru da shi ba.”
2 UAroni wasesithi kubo: Qamulani amacici egolide asendlebeni zabomkenu, zamadodana enu, lezamadodakazi enu, liwalethe kimi.
Haruna ya amsa musu ya ce, “Ku tuttuɓe zoban zinariya waɗanda suke kunnuwan matanku, da na’ya’yanku maza da mata, ku kawo mini.”
3 Bonke abantu basebeqamula amacici egolide ayesendlebeni zabo, bawaletha kuAroni.
Saboda haka dukan mutane suka tuttuɓe’yan kunnensu suka kawo wa Haruna.
4 Wawemukela ezandleni zabo, walibumba ngesikhali sokukhanda, wawenza aba lithole elibunjwe ngokuncibilikisa. Basebesithi: Laba ngonkulunkulu bakho, Israyeli, abakukhuphule elizweni leGibhithe.
Sai ya karɓi abubuwan da suka ba shi, ya yi gunki na siffar ɗan maraƙi, ya sassaƙa shi da kayan aiki. Sa’ad da mutane suka gani, sai suka tā da murya suka ce, “Waɗannan su ne allolinku, ya Isra’ila, waɗanda suka fitar da ku daga Masar.”
5 UAroni eselibonile wakha ilathi phambi kwalo; uAroni wamemezela wathi: Kusasa kuzakuba khona umkhosi weNkosi.
Da Haruna ya ga haka, sai ya gina bagade a gaban ɗan maraƙi, ya yi shela ya ce, “Gobe akwai biki ga Ubangiji.”
6 Basebevuka ekuseni kakhulu, banikela iminikelo yokutshiswa, basondeza iminikelo yokuthula; abantu bahlala phansi ukudla lokunatha, basebesukuma ukudlala.
Saboda haka kashegari, mutane suka tashi da sassafe suka miƙa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Bayan haka suka zauna suka ci, suka sha, suka kuma tashi suka yi rawa.
7 INkosi yasisithi kuMozisi: Hamba wehle, ngoba abantu bakho owabakhuphula elizweni leGibhithe bonakalisile;
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Sauka, gama mutanenka, waɗanda ka fitar da su daga Masar sun ƙazantu.
8 baphambukile masinyane endleleni engabalaya ngayo; bazenzele ithole elibunjwe ngokuncibilikisa, balikhonza, balihlabela, bathi: Laba ngonkulunkulu bakho, Israyeli, abakukhuphule elizweni leGibhithe.
Sun yi saurin juyawa daga abin da na umarce su, sun kuma yi wa kansu gunki na siffar ɗan maraƙi. Sun yi sujada ga ɗan maraƙi, suka yi hadaya gare shi, suka kuma ce, waɗannan su ne allolinka ya Isra’ila, waɗanda suka fito da kai daga Masar.”
9 INkosi yasisithi kuMozisi: Ngibabonile lababantu, khangela-ke, bangabantu abantamo zilukhuni.
Ubangiji ya ce wa Musa, “Na ga waɗannan mutane, mutane ne masu taurinkai.”
10 Khathesi-ke ngiyekela ukuze ulaka lwami lubavuthele, ngibaqede; kodwa wena ngizakwenza ube yisizwe esikhulu.
Yanzu ka bar ni kurum fushina yă yi ƙuna a kansu, in hallaka su. Sa’an nan in maishe ka al’umma mai girma.
11 Kodwa uMozisi wancenga ubuso beNkosi uNkulunkulu wakhe wathi: Kungani, Nkosi, ulaka lwakho lubavuthela abantu bakho owabakhupha elizweni leGibhithe ngamandla amakhulu langesandla esiqinileyo?
Amma Musa ya nemi tagomashin Ubangiji, Allahnsa ya ce, “Ya Ubangiji don me fushinka zai yi ƙuna a kan mutanenka, waɗanda ka fisshe su daga Masar da ikon hannunka mai girma?
12 Kungani amaGibhithe ezakhuluma athi: Wabakhuphela ububi ukubabulala ezintabeni, lokubaqeda ebusweni bomhlaba? Phenduka ekuvutheni kolaka lwakho, uzisole ngobubi obumelene labantu bakho.
Don me za ka sa Masarawa su ce, ‘Ai, da mugun nufi ne ya fito da su don yă shafe su daga fuskar duniya’? Ka juya daga fushinka mai zafi, ka ji tausayi, kada ka kawo masifa a kan mutanenka.
13 Khumbula uAbrahama, uIsaka loIsrayeli, inceku zakho, owazifunga wena kizo wathi kuzo: Ngizakwandisa inzalo yenu njengezinkanyezi zamazulu, lalelilizwe lonke engikhulume ngalo, ngizalipha inzalo yenu, njalo bazalidla ilifa lalo kuze kube nininini.
Ka tuna da bayinka Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, waɗanda ka rantse da kanka cewa, ‘Zan mai da zuriyarka kamar taurarin sama kuma zan ba wa zuriyarka wannan ƙasa wadda na yi musu alkawari, za tă kuma zama abin gādonsu har abada.’”
14 INkosi yasizisola ebubini eyayisithi izabenza ebantwini bayo.
Sai Ubangiji ya yi juyayi, bai kuwa kawo wa mutanensa bala’in da ya yi niyya ba.
15 UMozisi wasetshibilika wehla entabeni, lezibhebhe ezimbili zobufakazi esandleni sakhe; izibhebhe zazibhalwe inhlangothi zazo zombili; zibhalwe ngapha langapha.
Musa ya juya, ya sauka daga kan dutsen da alluna biyu na Alkawari a hannuwansa. An yi rubutun a kowane gefe, gaba da baya.
16 Lezibhebhe zazingumsebenzi kaNkulunkulu, lombhalo wawungumbhalo kaNkulunkulu, ubazwe ezibhebheni.
Allunan aikin Allah ne; rubutun kuma rubutun Allah ne, da ya zāna a kan alluna.
17 Kwathi uJoshuwa esezwile umsindo wabantu beklabalala, wathi kuMozisi: Kulomsindo wempi enkambeni.
Sa’ad da Yoshuwa ya ji surutun mutane suna ihu, sai ya ce wa Musa, “Kamar akwai ƙarar yaƙi a sansani.”
18 Kodwa wathi: Kakusumsindo wokuklabalala kokunqoba, njalo kakusumsindo wokuklabalala kokunqotshwa; ngizwa umsindo wokuhlabelela.
Musa ya amsa ya ce, “Ba ƙarar nasara ba ce, ba ƙarar wanda yaƙi ya ci ba ne; ƙarar waƙa ce nake ji.”
19 Kwasekusithi esesondele enkambeni walibona ithole lokugida; ulaka lukaMozisi lwaseluvutha, wasezilahla izibhebhe ezandleni zakhe, waziphahlazela phansi kwentaba.
Da Musa ya kusato sansanin, sai ya ga ɗan maraƙin da kuma mutane suna rawa. Sai fushinsa ya yi ƙuna, ya kuwa jefar da allunan da suke hannuwansa, allunan kuwa suka farfashe a gindin dutsen.
20 Wathatha ithole ababelenzile, walitshisa emlilweni, walichola laze lacoleka, walivuvuzela emanzini, wabanathisa wona abantwana bakoIsrayeli.
Sai ya ɗauki ɗan maraƙin da suka yi, ya ƙone a wuta; sa’an nan ya niƙa shi ya zama gari, ya barbaɗa garin a ruwa, ya sa Isra’ilawa suka sha.
21 UMozisi wasesithi kuAroni: Abantu laba benzeni kuwe ukuze ubehlisele isono esikhulu kangaka?
Ya ce wa Haruna, “Mene ne waɗannan mutane suka yi maka da ka kai su ga wannan zunubi mai girma?”
22 UAroni wasesithi: Kalungavuthi ulaka lwenkosi yami; wena uyabazi abantu ukuthi batshekele ebubini.
Haruna ya amsa ya ce, “Kada ka yi fushi da ni ranka yă daɗe, ka san yadda mutanen nan suke da saurin yin mugunta.
23 Ngoba bathi kimi: Senzele onkulunkulu abazahamba phambi kwethu; ngoba uMozisi lo, indoda eyasikhuphula elizweni leGibhithe, kasazi ukuthi yehlelwe yini.
Sun ce mini, ‘Ka yi mana alloli waɗanda za su yi mana jagora, game da wannan Musa dai, wanda ya fito da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba.’
24 Ngasengisithi kubo: Loba ngubani olegolide, kabaliqamule. Basebenginika lona. Ngasengiliphosela emlilweni, kwasekuphuma lelithole.
Sai na gaya musu, ‘Duk wanda yana da kayan ado na zinariya, ya cire?’ Sa’an nan suka ba ni zinariya, sai na jefa cikin wuta, wannan ɗan maraƙi ya fito.”
25 Kwathi uMozisi esebonile abantu ukuthi babengabambeki (ngoba uAroni wabayekela bangabambeki ukuze bayangeke kwababengabavukela),
Musa ya duba ya ga mutane sun kauce gaba ɗaya domin Haruna ya sa suka kauce, har suka zama abin dariya ga abokan gābansu.
26 uMozisi wasesima esangweni lenkamba, wathi: Loba ngubani ongoweNkosi, keze kimi! Kwasekubuthana kuye wonke amadodana kaLevi.
Saboda haka sai ya tsaya a ƙofar sansani ya ce, “Duk wanda yake na Ubangiji yă zo wurina.” Sai dukan Lawiyawa suka taru wurinsa.
27 Wasesithi kuwo: Itsho njalo iNkosi uNkulunkulu kaIsrayeli ithi: Ngulowo lalowo kahlome inkemba yakhe ethangazini lakhe, adabule aphenduke esuka esangweni esiya esangweni enkambeni, langulowo lalowo abulale umfowabo, langulowo lalowo umngane wakhe, langulowo lalowo umakhelwane wakhe.
Sa’an nan ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Kowane mutum yă rataya takobinsa, yă kai yă kawo daga wannan gefe zuwa wancan cikin sansani, kowa yă kashe ɗan’uwansa, da abokinsa, da kuma maƙwabcinsa.’”
28 Amadodana kaLevi asesenza njengelizwi likaMozisi; njalo kwawa ebantwini ngalolosuku abantu abangabazinkulungwane ezintathu.
Lawiyawa suka yi yadda Musa ya umarta, a ranar, mutane wajen dubu uku suka mutu.
29 UMozisi wasesithi: Lizehlukanisele iNkosi lamuhla, ngoba ngulowo lalowo ubemelene lendodana yakhe amelane lomfowabo, ukuze aphe isibusiso phezu kwenu lamuhla.
Sa’an nan Musa ya ce, “An keɓe ku ga Ubangiji a yau, gama kun yi gāba da’ya’yanku da’yan’uwanku, ya kuma albarkace ku a wannan rana.”
30 Kwasekusithi kusisa uMozisi wathi ebantwini: Lina lenze isono esikhulu; khathesi sengizakwenyukela eNkosini; mhlawumbe ngingenza inhlawulo yokuthula ngesono senu.
Kashegari Musa ya ce wa mutane, “Kun yi zunubi mai girma. Amma yanzu zan hau wurin Ubangiji; wataƙila zan iya yin kafara domin zunubinku.”
31 UMozisi wasebuyela eNkosini wathi: Maye! Lababantu bonile isono esikhulu, bazenzele onkulunkulu begolide.
Don haka Musa ya koma wurin Ubangiji ya ce, “Kaito, mutanen nan sun yi zunubi mai girma! Sun yi wa kansu allolin zinariya.
32 Khathesi-ke, uba uthethelela isono sabo - kodwa uba kungenjalo, ake ungesule egwalweni lwakho olubhalileyo.
Amma yanzu, ina roƙonka ka gafarta zunubinsu, in ba haka ba, to, ka shafe ni daga littafin da ka rubuta.”
33 INkosi yasisithi kuMozisi: Owonileyo kimi ngizamesula egwalweni lwami.
Ubangiji ya amsa wa Musa, “Duk wanda ya yi mini zunubi, shi zan shafe daga littafina.
34 Kodwa hamba-ke, ukhokhele abantu baye lapho engikhulume lawe ngakho; khangela, ingilosi yami izahamba phambi kwakho. Kanti mhla ngiphindisela ngizaphindisela isono sabo phezu kwabo.
Yanzu tafi, ka jagoranci mutanen zuwa inda na yi zance, mala’ikana kuma zai sha gabanku. Duk da haka sa’ad da lokaci ya yi da zan yi horo, zan hore su domin zunubinsu.”
35 INkosi yasibatshaya abantu ngoba babenze ithole, uAroni ayelenzile.
Ubangiji kuwa ya bugi mutanen da annoba, saboda abin da suka yi da ɗan maraƙin da Haruna ya yi.

< U-Eksodusi 32 >