< U-Eksodusi 19 >

1 Ngenyanga yesithathu emva kokuphuma kwabantwana bakoIsrayeli elizweni leGibhithe, ngalelolanga bafika enkangala yeSinayi.
A rana ta farko a cikin watan uku bayan da Isra’ilawa suka bar Masar, a wannan rana, suka iso Hamadar Sinai.
2 Sebesukile eRefidimi, bafika enkangala yeSinayi, bamisa inkamba enkangala; uIsrayeli wamisa-ke inkamba khona phambi kwentaba.
Bayan da suka tashi daga Refidim, suka shiga Hamadar Sinai, sai Isra’ilawa suka yi sansani a gaban dutsen.
3 UMozisi wasesenyukela kuNkulunkulu. INkosi yasimemeza kuye esentabeni isithi: Uzakutsho njalo kuyo indlu kaJakobe, ubatshele abantwana bakoIsrayeli uthi:
Sai Musa ya hau kan dutsen don yă sadu da Allah, Ubangiji kuwa ya kira shi daga dutsen ya ce, “Wannan shi ne abin da za ka faɗa wa gidan Yaƙub, da kuma abin da za ka faɗa wa mutanen Isra’ila.
4 Lina libonile lokho engikwenze kumaGibhithe, lokuthi ngalithwala phezu kwempiko zenkozi, ngaliletha kimi.
‘Ku da kanku kun ga abin da na yi wa Masar, da yadda na ɗauko ku a kan fikafikan gaggafa na kawo ku wurina.
5 Ngakho-ke uba lilalela lokulalela ilizwi lami, ligcine isivumelwano sami, khona lizakuba yimfuyo ekhethekileyo kimi kulazo zonke izizwe; ngoba umhlaba wonke ungowami;
Yanzu, in kuka yi mini cikakken biyayya, kuka kuma kiyaye yarjejjeniyata, to, za ku zama keɓeɓɓiyar taska a gare ni a cikin dukan al’ummai. Ko da yake duk duniya tawa ce,
6 njalo lizakuba ngumbuso wabapristi lesizwe esingcwele kimi. Yiwo lamazwi ozawatsho kubantwana bakoIsrayeli.
za ku zama firistoci masu tsarki da kuma al’umma keɓaɓɓiya a gare ni.’ Waɗannan su ne kalmomin da za ka faɗa wa Isra’ilawa.”
7 UMozisi wasesiza wabiza abadala babantu, wabeka phambi kwabo wonke la amazwi iNkosi emlaye wona.
Sai Musa ya koma ya aika a kira dukan dattawan mutane, ya bayyana dukan kalmomin da Ubangiji ya umarta, ya faɗa.
8 Bonke abantu basebephendula kanyekanye bathi: Konke iNkosi ekukhulumileyo sizakwenza. UMozisi wasebuyisela amazwi abantu eNkosini.
Dukan mutane suka amsa gaba ɗaya suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa.” Sai Musa ya mayar wa Ubangiji amsar da mutane suka bayar.
9 INkosi yasisithi kuMozisi: Khangela, ngizakuza kuwe eyezini elinzima ukuze abantu bezwe nxa ngikhuluma lawe, lokuthi bakholwe kuwe kuze kube nininini. UMozisi wasebikela iNkosi amazwi abantu.
Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ina zuwa wurinka a cikin baƙin hadari, domin mutane su ji ni ina maganar da kai, domin su amince da kai koyaushe.” Sa’an nan Musa ya faɗa wa Ubangiji abin da mutane suka ce.
10 INkosi yasisithi kuMozisi: Hamba uye ebantwini, ubangcwelise lamuhla lakusasa, bawatshe izembatho zabo,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tafi wurin mutanen, ka tsarkake su yau da gobe, ka sa su wanke tufafinsu.
11 babe sebelungele usuku lwesithathu; ngoba ngosuku lwesithathu iNkosi izakwehla phambi kwamehlo abantu bonke phezu kwentaba yeSinayi.
Su zama da shiri a rana ta uku, gama a ranar ce Ubangiji zai sauko a kan Dutsen Sinai a idon dukan mutane.
12 Uzabamisela abantu umngcele inhlangothi zonke uthi: Ziqapheleni ukukhwela entabeni, lokuthinta ewatheni layo. Wonke othinta intaba uzabulawa lokubulawa.
Sai ka yi wa jama’a iyaka kewaye da dutsen, ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ku mai da hankali, kada ku hau dutsen ko ku taɓa gefensa. Duk wanda ya taɓa dutsen, lalle za a kashe shi.
13 Kakulasandla esizayithinta, kodwa sibili uzakhandwa ngamatshe loba sibili uzatshokwa; loba inyamazana loba umuntu, kakuyikuphila. Lapho uphondo lwenqama lukhala isikhathi eside bazakwenyukela entabeni.
Za a jajjefe shi da duwatsu, ko a harbe shi da kibiyoyi, ba hannun da zai taɓa shi. Mutum ko dabbar da ya taɓa, ba za a bar shi da rai ba.’ Lokacin da aka ji muryar ƙaho ne kawai za su iya taru a gindin dutsen.”
14 UMozisi wasesehla entabeni waya ebantwini, wangcwelisa abantu, njalo bahlamba izembatho zabo.
Bayan da Musa ya gangara wurin mutane, ya tsarkake su, sai suka wanke tufafinsu.
15 Wathi ebantwini: Lungelani usuku lwesithathu; lingasondeli kowesifazana.
Sa’an nan ya ce wa mutane, “Ku shirya kanku domin rana ta uku. Ku ƙame kanku daga yin jima’i.”
16 Kwasekusithi ngosuku lwesithathu sekusile, kwakulemidumo lemibane leyezi elinzima phezu kwentaba, lelizwi lophondo olulamandla amakhulu; kwaze kwathi bonke abantu ababesenkambeni bathuthumela.
A safiyar rana ta uku, aka yi tsawa, da walƙiyoyi, sai ga girgije mai duhu a bisa dutsen, aka tsananta busar ƙaho, sai dukan jama’ar da suke cikin sansani suka yi rawar jiki.
17 UMozisi wasebakhupha abantu enkambeni ukuyamhlangabeza uNkulunkulu; basebesima ngaphansi kwentaba.
Sa’an nan Musa ya jagoranci mutane daga sansani domin su sadu da Allah, sai suka tsaya a gefen dutsen.
18 Intaba yonke-ke yeSinayi yathunqa intuthu, ngoba iNkosi yehlela phezu kwayo ngomlilo; njalo intuthu yayo yenyuka njengentuthu yesithando; intaba yonke yasizamazama kakhulu.
Dutsen Sinai kuwa ya tunnuƙe duka da hayaƙi, gama Ubangiji ya sauko a bisan dutsen cikin wuta. Hayaƙin ya hau kamar hayaƙin da yake fitowa daga matoya, duk dutsen ya yi rawa da ƙarfi,
19 Kwathi ilizwi lophondo liqhubeka lisiba lamandla amakhulu, uMozisi wakhuluma; njalo uNkulunkulu wamphendula ngelizwi.
sai karar ƙaho ya yi ta ƙaruwa. Sa’an nan Musa ya yi magana, murya Allah kuwa ta amsa masa.
20 INkosi yasisehlela entabeni yeSinayi, engqongeni yentaba; iNkosi yambizela uMozisi engqongeni yentaba; uMozisi wenyuka-ke.
Ubangiji ya sauko a kan ƙwanƙolin Dutsen Sinai, ya kira Musa zuwa ƙwanƙolin dutsen. Musa kuwa ya haura
21 INkosi yasisithi kuMozisi: Yehla, ubaxwayise abantu hlezi bafohlele eNkosini ukubona, njalo abanengi babo bawe.
sai Ubangiji ya ce masa, “Ka sauka ka faɗa wa jama’a, kada su kuskura su ƙetare layin iyakan nan, garin son zuwa don ganin Ubangiji, gama duk waɗanda suka yi haka za su mutu.
22 Labapristi labo abasondela eNkosini kabazingcwelise hlezi iNkosi ibadumele.
Ko firistocin da za su kusato Ubangiji sai su tsarkake kansu, don kada in hallaka su.”
23 UMozisi wasesithi eNkosini: Abantu bangenyukele entabeni yeSinayi, ngoba wena usixwayisile usithi: Misa umngcele wentaba, uyingcwelise.
Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutanen ba za su hau Dutsen Sinai ba, gama kai da kanka ka gargaɗe mu, ‘Ku sa iyaka kewaye da dutsen ku kuma tsarkake shi.’”
24 INkosi yasisithi kuye: Hamba wehle, ubuye wenyuke, wena loAroni elawe; kodwa abapristi labantu kabangafohli benyukele eNkosini, hlezi ibadumele.
Ubangiji ya amsa, “Sauka ka kawo Haruna tare da kai. Amma kada firistoci da mutane su zarce iyakan nan, a kan za su zo wurin Ubangiji, don kada in hallaka su.”
25 UMozisi wasesehlela ebantwini, wabatshela.
Saboda haka Musa ya sauka wurin mutane ya kuma faɗa musu.

< U-Eksodusi 19 >