< UDutheronomi 1 >
1 La ngamazwi uMozisi awakhuluma kuIsrayeli wonke nganeno kweJordani enkangala, egcekeni eliqondene leSufi, phakathi kweParani leTofeli leLabani leHazerothi leDizahabi.
Waɗannan su ne kalmomin da Musa ya yi wa dukan Isra’ila, a hamada gabas da Urdun, wato, Araba, ɗaura da Suf, tsakanin Faran da Tofel, Laban, Hazerot da Dizahab.
2 Kulensuku ezilitshumi lanye kusukela eHorebe ngendlela yentaba yeSeyiri kusiya eKadeshi-Bhaneya.
(Yakan ɗauki kwana goma sha ɗaya daga Horeb zuwa Kadesh Barneya ta hanyar Dutsen Seyir.)
3 Kwasekusithi ngomnyaka wamatshumi amane, ngenyanga yetshumi lanye, ngolokuqala lwenyanga, uMozisi wakhuluma kubantwana bakoIsrayeli njengakho konke iNkosi eyamlaya ngakho kubo,
A shekara ta arba’in, a rana ta fari ga wata na goma sha ɗaya, Musa ya yi shela ga Isra’ilawa game da dukan abin da Ubangiji ya umarta shi game da su.
4 esemtshayile uSihoni inkosi yamaAmori owayehlala eHeshiboni, loOgi inkosi yeBashani owayehlala eAshitarothi eEdreyi.
Wannan ya faru bayan ya ci Sihon sarkin Amoriyawa wanda ya yi mulki a Heshbon da yaƙi. A Edireyi kuma ya ci Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot da yaƙi.
5 Nganeno kweJordani, elizweni lakoMowabi, uMozisi waqala ukuchasisa lumlayo esithi:
Gabas da iyakar Mowab, Musa ya fara bayyana wannan doka, yana cewa,
6 INkosi uNkulunkulu wethu yakhuluma kithi eHorebe isithi: Selihlale isikhathi eseneleyo kulintaba.
Ubangiji Allahnmu ya faɗa mana a Horeb cewa, “Daɗewarku a wannan dutse ya isa haka.
7 Phendukani lisuke, liye entabeni yamaAmori, lendaweni ezakhelene lawo, egcekeni, entabeni, lesihotsheni, leningizimu, lekhunjini lolwandle, ilizwe lamaKhanani, leLebhanoni, kuze kube semfuleni omkhulu, umfula iYufrathi.
Ku tashi, ku ci gaba zuwa ƙasar tudun Amoriyawa; ku tafi wurin dukan maƙwabta a cikin Araba, a cikin duwatsu, a gindin yammancin tuddai, a Negeb da kuma a ta kwaruruka, da ƙasar Kan’aniyawa da kuma zuwa Lebanon, har zuwa babban kogi, wato, Yuferites.
8 Bonani, ngibeke ilizwe phambi kwenu. Ngenani, lidle ilifa lelizwe iNkosi eyalifungela oyihlo, oAbrahama, uIsaka, loJakobe, ukubanika lona lenzalo yabo emva kwabo.
Duba na riga na ba ku wannan ƙasa. Ku shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub, da kuma ga zuriyarsu bayansu.”
9 Njalo ngakhuluma kini ngalesosikhathi ngisithi: Kangilakulithwala ngingedwa.
A wancan lokaci na faɗa muku cewa, “Ku kaya ne masu nauyi da ni kaɗai ba zan iya ɗauka ba.
10 INkosi uNkulunkulu wenu ilandisile, khangelani-ke, lamuhla linjengenkanyezi zamazulu ngobunengi.
Ubangiji Allahnku ya ƙara yawanku har yau kuka zama da yawa kamar taurari a sarari.
11 INkosi, uNkulunkulu waboyihlo, kayandise kini, njengoba linjalo, ngokuphindwe kankulungwane, ilibusise, njengokukhuluma kwayo kini.
Bari Ubangiji, Allahn kakanninku yă ƙara yawanku sau dubu, yă kuma albarkace ku yadda ya yi alkawari!
12 Ngingedwa ngingathwala njani ubunzima benu lomthwalo wenu lenkani yenu?
Amma yaya zan ɗauka dukan damuwoyinku da nawayarku da kuma faɗace-faɗacenku duka ni kaɗai?
13 Zithatheleni amadoda ahlakaniphileyo, azwisisayo, laziwayo ezizweni zenu, ngiwabeke-ke abe zinhloko zenu.
Ku zaɓi waɗansu masu hikima, masu ganewa, da kuma mutanen da ake girmama daga kowace kabilarku, zan kuma sa su a kanku.”
14 Laselingiphendula lisithi: Ilizwi olikhulumileyo lilungile ukulenza.
Kuka amsa mini, kuka ce, “Abin da ka ce za ka yi, yana da kyau.”
15 Ngasengithatha inhloko zezizwe zenu, amadoda ahlakaniphileyo, aziwayo, ngawabeka aba zinhloko phezu kwenu, induna zezinkulungwane, lenduna zamakhulu, lenduna zamatshumi amahlanu, lenduna zamatshumi, leziphathamandla zezizwe zenu.
Saboda haka na ɗauko shugabannin kabilanku masu hikima, waɗanda suka saba da ma’amala da jama’a, na sa su shugabanni a gabanku, waɗansu suka zama shugabanni a kan dubu-dubu, waɗansu a kan ɗari-ɗari, waɗansu a kan hamsin-hamsin, waɗansu kuma a kan goma-goma. Na sa su zama shugabanni a kabilanku.
16 Ngasengilaya abahluleli benu ngalesosikhathi ngisithi: Zwanini okuphakathi kwabafowenu, lahlulele ngokulunga phakathi komuntu lomfowabo lowezizweni okuye.
Na kuma umarci alƙalanku a wancan lokaci, na ce, “Ku yi adalci cikin shari’a tsakanin’yan’uwanku, ko damuwar tana tsakanin’yan’uwa Isra’ilawa ne, ko kuwa tsakanin Isra’ilawa da baƙin da suke zaune a cikinku.
17 Lingakhangeli ubuso ekwahluleleni, zwanini omncinyane njengomkhulu; lingesabi ubuso bomuntu, ngoba ukwahlulela kungokukaNkulunkulu. Lendaba elukhuni kini lizayiletha kimi, besengiyizwa.
Kada ku nuna sonkai a cikin hukuncinku, ku saurari kowane ɓangare, babba da ƙarami, kada ku ji tsoron wani, gama hukunci na Allah ne. Ku kawo kowane batun da ya sha ƙarfinku, zan kuwa saurare shi.”
18 Langalesosikhathi ngalilaya zonke izinto elifanele ukuzenza.
A wancan lokacin kuwa na faɗa muku dukan abin da ya kamata ku yi.
19 Sasesisuka eHorebe, sahamba kuyo yonke leyonkangala enkulu leyesabekayo elayibonayo ngendlela yentaba yamaAmori, njengokusilaya kweNkosi uNkulunkulu wethu, saze safika eKadeshi-Bhaneya.
Sa’an nan, muka kama hanya daga Horeb muka ratsa wajen ƙasar tudun Amoriyawa ta dukan hamadarta mai fāɗi, da kuma mai bantsoron da kuka gani, muka kuma kai Kadesh Barneya yadda Ubangiji, Allahnmu ya umarce mu.
20 Ngasengisithi kini: Selifikile entabeni yamaAmori iNkosi uNkulunkulu wethu ezasinika yona.
Sai na ce muku, “Kun iso ƙasar tudun Amoriyawa, wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.
21 Bona, iNkosi uNkulunkulu wakho ilinikile ilizwe phambi kwakho; yenyuka udle ilifa lalo, njengokutsho kweNkosi uNkulunkulu waboyihlo kuwe; ungesabi, ungadideki.
Duba, Ubangiji Allahnku ya ba ku ƙasar. Ku haura ku mallake ta yadda Ubangiji Allahn kakanninku ya faɗa muku. Kada ku ji tsoro, kada ku fid da zuciya.”
22 Laselisondela kimi lonke lathi: Asithume amadoda phambi kwethu ukuze asihlolele ilizwe, abuyise ilizwi kithi, indlela esizakwenyuka ngayo, lemizi esizangena kuyo.
Sai dukanku kuka zo wurina kuka ce, “Bari mu aiki mutane su yi gaba su leƙi mana asirin ƙasar, su kuma kawo mana labari game da hanyar da za mu bi, da kuma biranen da za mu shiga.”
23 Lendaba yayinhle emehlweni ami; ngakho ngathatha kini amadoda alitshumi lambili, indodanye ngesizwe.
Ra’ayin nan naku ya yi mini kyau, saboda haka na zaɓe ku goma sha biyu, mutum guda daga kowace kabila.
24 Wona aphenduka, enyukela entabeni aze afika esihotsheni seEshikoli, asihlola.
Suka tafi, suka haura zuwa ƙasar tudu, suka kai Kwarin Eshkol, suka leƙo asirin ƙasar.
25 Asethatha okwezithelo zelizwe esandleni sabo, azehlisela kithi; abuyisa ilizwi kithi athi: Ilizwe lihle iNkosi uNkulunkulu wethu esinika lona.
Suka ɗebi’ya’yan itatuwan ƙasar, suka sauko mana da su, suka kuma ba da labari cewa, “Ƙasar da Ubangiji Allahnmu yake ba mu, kyakkyawa ce.”
26 Kanti kalifunanga ukwenyuka, kodwa lavukela umlomo weNkosi uNkulunkulu wenu,
Amma ba ku yi niyya ku haura ba, kuka yi tawaye gāba da umarnin Ubangiji Allahnku.
27 langunguna emathenteni enu lathi: Ngoba iNkosi yayisizonda, yasikhupha elizweni leGibhithe ukusinikela esandleni samaAmori ukusibhubhisa.
Kuka yi gunaguni a cikin tentunanku, kuna cewa, “Ubangiji ya ƙi mu; shi ya sa ya fitar da mu daga Masar don yă ba da mu ga hannuwan Amoriyawa su hallaka mu.
28 Sizakwenyukela ngaphi? Abafowethu benze inhliziyo yethu iphele amandla besithi: Abantu bakhulu bade kulathi; imizi mikhulu, ibiyelwe ngemithangala efika emazulwini; futhi-ke sibonile khona amadodana amaAnaki.
Ina za mu?’Yan’uwanmu suka sa muka fid da zuciya. Suka ce, ‘Mutanen sun fi mu ƙarfi, sun kuma fi mu tsayi; biranen manya ne, da katanga har sama. Mun ma ga Anakawa a can.’”
29 Ngasengisithi kini: Lingatshaywa luvalo, libesabe.
Sai na ce muku, “Kada ku firgita; kada ku ji tsoronsu.
30 INkosi uNkulunkulu wenu ehamba phambi kwenu, yona izalilwela njengakho konke eyalenzela khona eGibhithe phambi kwamehlo enu,
Ubangiji Allahnku yana a gabanku, zai yi yaƙi saboda ku, kamar yadda ya yi a kan idanunku a Masar,
31 lenkangala, lapho obone khona ukuthi iNkosi uNkulunkulu wakho yakuthwala njengendoda ithwala indodana yayo, endleleni yonke elahamba ngayo laze lafika kulindawo.
da kuma a cikin hamada. A can ma kun ga yadda Ubangiji Allahnku ya riƙe ku ko’ina da kuka tafi, kamar yadda mahaifi yakan riƙe ɗansa, sai da kuka kai wannan wuri.”
32 Kodwa ngalelilizwi kalikholwanga iNkosi uNkulunkulu wenu
Duk da haka, ba ku amince da Ubangiji Allahnku ba,
33 eyahamba phambi kwenu endleleni, ukulidingela indawo ukuze limise inkamba, ngomlilo ebusuku, ukulitshengisa indlela elizahamba ngayo, langeyezi emini.
shi da ya sha gabanku a tafiyarku, cikin wuta da dad dare da kuma girgije da rana, don yă nemi wurare domin ku kafa sansani, don kuma yă nuna muku hanyar da za ku bi.
34 Kwathi iNkosi isizwile ilizwi lamazwi enu, yathukuthela yafunga yathi:
Da Ubangiji ya ji abin da kuka faɗa, sai ya husata, ya kuma yi rantsuwa ya ce,
35 Isibili kakho kulamadoda alesisizukulwana esibi ozabona ilizwe elihle engafunga ukulinika oyihlo,
“Babu wani a cikin wannan muguwar tsara da zai ga ƙasa mai kyau da na rantse zan ba wa kakanninku,
36 ngaphandle kukaKalebi indodana kaJefune; yena uzalibona. Njalo ngizanika kuye ilizwe anyathela kulo, lakubantwana bakhe, ngoba ulandele iNkosi ngokupheleleyo.
sai dai Kaleb ɗan Yefunne. Zai gan ta, zan ba shi duk ƙasar da tafin ƙafarsa ta taka, shi da zuriyarsa, gama ya bi Ubangiji da zuciya ɗaya.”
37 Lami iNkosi yangithukuthelela ngenxa yenu, isithi: Lawe kawuyikungena khona.
Saboda ku Ubangiji ya husata da ni, ya kuma ce, “Kai ma, ba za ka shiga ƙasar ba.
38 UJoshuwa indodana kaNuni oma phambi kwakho, yena uzangena khona; mqinise, ngoba yena uzakwenza uIsrayeli adle ilifa lalo.
Amma mataimakinka, Yoshuwa ɗan Nun, zai shiga. Ka ƙarfafa shi gama shi ne zai jagoranci Isra’ila su gāje ta.
39 Labantwanyana benu elalisithi bazakuba yimpango, labantwana benu, abangaziyo lamuhla okuhle lokubi, bona bazangena khona; lakubo ngizalinika, bona-ke bazakudla ilifa lalo.
Amma’ya’yanku ƙanana waɗanda ba su san mugunta ko nagarta ba, waɗanda kuke tsammani za a kwashe su ganima, su za su shiga ƙasar. Zan ba da ita gare su, za su kuwa mallake ta.
40 Kodwa lina ziphendukeleni, lisuke liye enkangala, indlela yoLwandle oluBomvu.
Amma ku kam, sai ku juya, ku koma cikin hamada ta hanyar Jan Teku.”
41 Laseliphendula lisithi kimi: Sonile eNkosini; thina sizakwenyuka siyekulwa, njengakho konke iNkosi uNkulunkulu wethu eyasilaya khona. Selihlomile, ngulowo lalowo isikhali sakhe sempi, lacabanga ukuthi kulula ukwenyukela entabeni.
Sai kuka amsa, kuka ce, “Mun yi zunubi ga Ubangiji. Za mu haura mu yi yaƙi yadda Ubangiji Allahnmu ya umarce mu.” Saboda haka kowannenku ya yi ɗamara da kayan yaƙinsa, kuka yi tsammani zai zama muku da sauƙi ku ci ƙasar tuddai da yaƙi.
42 INkosi yasisithi kimi: Tshono kubo: Lingenyuki, lingalwi, ngoba kangikho phakathi kwenu, hlezi litshaywe phambi kwezitha zenu.
Amma Ubangiji ya ce mini, “In faɗa muku, ‘Kada ku fāɗa musu da yaƙi, gama ba zai kasance tare da ku ba. Idan kuka kuskura, abokan gābanku za su murƙushe ku.’”
43 Ngasengikhuluma kini, kodwa kalilalelanga, lavukela umlomo weNkosi, laqholoza lenyukela entabeni.
Sai na faɗa muku, amma ba ku saurara ba. Kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji, a cikin jahilcinku kuwa kuka taka, kuka haura cikin ƙasar tudu.
44 Kwathi amaAmori ayehlala entabeni leyo aphuma ukumelana lani, alixotsha njengokwenziwa zinyosi, alihlakaza eSeyiri, kwaze kwaba seHorma.
Amoriyawan da suke zama a waɗannan tuddai, suka fito kamar tarin ƙudan zuma gāba da ku, suka kore ku, suka fatattake ku daga Seyir har zuwa Horma.
45 Laselibuya, lakhala inyembezi phambi kweNkosi, kodwa iNkosi kayilizwanga ilizwi lenu, kayibekanga indlebe kini.
Kuka dawo, kuka yi kuka a gaban Ubangiji, amma bai kula da ku ba, balle yă saurare ku.
46 Laselihlala eKadeshi insuku ezinengi, njengensuku elahlala ngazo.
Haka kuwa kuka zauna a Kadesh kwanaki masu yawa, kuka ci lokaci a can.