< UDutheronomi 13 >

1 Uba kuvela phakathi kwakho umprofethi kumbe umphuphi wamaphupho, akunike isibonakaliso loba isimangaliso,
In wani annabi ko mai mafarkai, ya bayyana a cikinku, ya kuma yi muku shelar wata alama mai banmamaki ko al’ajabi,
2 lesibonakaliso loba isimangaliso akhulume ngaso kuwe senzakale, esithi: Asilandele abanye onkulunkulu ongabazanga, sibakhonze;
in kuwa alamar, ko al’ajabin da annabin ya yi faɗin ya faru, ya kuma ce, “Bari mu bi waɗansu alloli (allolin da ba ku sani ba) mu kuma yi musu sujada,”
3 ungalaleli amazwi alowomprofethi loba lowomphuphi wamaphupho; ngoba iNkosi uNkulunkulu wenu iyalilinga ukuze yazi ukuthi liyayithanda yini iNkosi uNkulunkulu wenu ngenhliziyo yenu yonke langomphefumulo wenu wonke.
kada ku saurari kalmomin wannan annabi ko mai mafarki. Ubangiji Allahnku yana gwada ku ne don yă sani ko kuna ƙaunarsa da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
4 INkosi uNkulunkulu wenu lizayilandela, yona liyesabe, imithetho yayo liyigcine, ilizwi layo lililalele, yona liyikhonze, kuyo linamathele.
Ubangiji Allahnku ne za ku bi, shi ne kuma za ku girmama. Ku kiyaye umarnansa, ku kuma yi masa biyayya; ku bauta masa, ku kuma manne masa.
5 Lalowomprofethi loba lowomphuphi wamaphupho kabulawe, ngoba ukhulume ukuhlamukela iNkosi uNkulunkulu wenu, eyalikhupha elizweni leGibhithe, yakuhlenga endlini yobugqili, ukukufuqa uphambuke endleleni iNkosi uNkulunkulu wakho eyakulaya ukuhamba ngayo. Ngalokhu uzakhupha ububi phakathi kwakho.
Dole a kashe wannan annabi ko mai mafarki, domin ya yi wa’azin tawaye ga Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, ya fanshe ku daga ƙasar bauta; gama annabin nan ya yi ƙoƙari yă juye daga hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, ku bi. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
6 Uba umfowenu, indodana kanyoko, loba indodana yakho, loba indodakazi yakho, loba umfazi wesifuba sakho, kumbe umngane wakho onjengomphefumulo wakho, ekuyenga ensitha esithi: Asihambe, siyekhonza abanye onkulunkulu, ongabazanga, wena laboyihlo,
In ɗan’uwanka, ko ɗanka, ko’yarka, ko matar da kake ƙauna, ko abokinka na kusa, a ɓoye ya ruɗe ka, yana cewa, “Mu je mu yi wa waɗansu alloli sujada” (allolin da ko kai, ko kakanninka ba su sani ba,
7 babonkulunkulu babantu abalizingelezeleyo, abaseduze lawe loba abakhatshana lawe, kusukela komunye umkhawulo womhlaba kuze kufike komunye umkhawulo womhlaba,
allolin mutanen kewayenku, ko na kusa, ko na nisa, daga wannan ƙarshen ƙasar zuwa wancan),
8 ungamvumeli, ungamlaleli, futhi ilihlo lakho lingamhawukeli, njalo ungamyekeli, ungamfihli,
kada ka yarda da shi, kada ma ka saurare shi. Kada ka ji tausayinsa. Kada ka haƙura da shi, ko ka tsare shi.
9 kodwa umbulale lokumbulala; isandla sakho sizakuba ngesokuqala phezu kwakhe ukumbulala, lemva kwalokho isandla sabantu bonke.
Dole ka kashe shi. Dole hannunka yă zama na farko a kisansa, sa’an nan hannuwan sauran dukan mutane.
10 Njalo mkhande ngamatshe aze afe, ngoba ubedinga ukukufuqa uphambuke eNkosini uNkulunkulu wakho, eyakukhupha elizweni leGibhithe, endlini yobugqili.
Ku jajjefe shi da duwatsu har sai ya mutu, domin ya yi ƙoƙari yă juye ku daga Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta kuma.
11 LoIsrayeli wonke uzakuzwa, esabe, angabe esenza ububi obunjengalobo phakathi kwakho.
Sa’an nan dukan Isra’ila za su ji su kuma tsorata, babu kuma wani a cikinku da zai ƙara yin irin wannan mugun abu.
12 Uba usizwa komunye wemizi yakho, iNkosi uNkulunkulu wakho ekunika yona, ukuthi uhlale khona, kuthiwa:
In kuka ji an yi magana a kan wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku zauna a ciki
13 Kuphumile amadoda, abantwana bakaBheliyali, phakathi kwakho, afuqa aphambula abakhileyo bomuzi wawo esithi: Asihambe siyekhonza abanye onkulunkulu elingabazanga;
cewa mugaye sun taso a cikinku, suna rikitar da mutane a birni, suna cewa, “Mu je mu yi wa waɗansu alloli sujada” (allolin da ba ku sani ba),
14 khona uzabuza, uhlolisise, udingisise; khangela, uba kuliqiniso, leyonto iqinisekile, lesisinengiso senziwe phakathi kwakho,
to, sai ku bincike labarin sosai a hankali. In kuwa gaskiya ne, an kuma tabbatar wannan abin ƙyama ya faru a cikinku,
15 uzatshaya lokubatshaya abakhileyo balowomuzi ngobukhali benkemba, uwutshabalalise, lakho konke okukuwo lezifuyo zawo, ngobukhali benkemba.
dole a karkashe dukan waɗanda suke zama a wannan birni da takobi. Ku hallaka su ƙaƙaf, ku karkashe mutanen birnin da kuma dabbobinsa.
16 Uzabuthela yonke impango yawo phakathi komdanga wawo, utshise ngomlilo umuzi lempango yawo yonke uphele du, eNkosini uNkulunkulu wakho; njalo uzakuba yinqumbi phakade, awuyikwakhiwa futhi.
Ku tattara dukan ganimar birnin a tsakiyar gari, ku ƙone birnin da kuma ganimar ƙurmus a matsayin hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji Allahnku. Birnin zai kasance kufai har abada, kada a sāke gina shi.
17 Kunganamatheli lutho kwalokho okuqalekisiweyo esandleni sakho, ukuze iNkosi iphenduke ekuvutheni kwentukuthelo yayo, ikuphe umusa, ibe lobubele kuwe, ikwandise, njengalokhu yafunga kuboyihlo,
Ba za a iske wani daga cikin abubuwan nan da aka haramta a hannuwanku ba, saboda Ubangiji yă juya daga fushinsa mai ƙuna, yă nuna jinƙai, yă ji tausayinku, yă kuma ƙara yawanku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa ga kakanninku,
18 uba ulalela ilizwi leNkosi uNkulunkulu wakho, ukugcina yonke imithetho yayo engikulaya yona lamuhla, ukwenza okulungileyo emehlweni eNkosi uNkulunkulu wakho.
domin kun yi biyayya da Ubangiji Allahnku, kuna kiyaye dukan umarnan da nake ba ku a yau, kuna kuma aikata abin da yake daidai a idanunsa.

< UDutheronomi 13 >