< U-Amosi 2 >

1 Itsho njalo iNkosi: Ngenxa yeziphambeko ezintathu zikaMowabi, langenxa yezine, kangiyikuphambula isijeziso sabo, ngoba watshisa amathambo enkosi yeEdoma aba yikalaga.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Mowab, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama ya ƙone ƙasusuwan sarkin Edom suka zama sai ka ce toka.
2 Ngakho ngizathumela umlilo koMowabi, ozaqeda izigodlo zeKeriyothi, uMowabi afele phakathi kokuxokozela, ngokumemeza, ngokukhala kophondo.
Zan sa wuta a Mowab da za tă ƙone kagarun Keriyot Mowab za tă gangara cikin hayaniya mai girma cikin kururuwar yaƙi da kuma ƙarar ƙaho.
3 Ngiqume umahluleli asuke phakathi kwakhe, ngibulale zonke iziphathamandla zakhe kanye laye, itsho iNkosi.
Zan hallaka mai mulkinta zan kuma kashe shugabanninta.”
4 Itsho njalo iNkosi: Ngenxa yeziphambeko ezintathu zakoJuda, langenxa yezine, kangiyikuphambula isijeziso sabo, ngoba bawalile umlayo weNkosi, kabagcinanga izimiso zayo, lamanga abo abaduhisile, oyise abawalandelayo.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Yahuda, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama sun ƙi bin dokar Ubangiji ba su kuma yi biyayya da ƙa’idodinsa ba, domin allolin ƙarya sun ruɗe su, allolin da kakanninsu suka bauta.
5 Ngakho ngizathumela umlilo koJuda, futhi uzaqeda izigodlo zeJerusalema.
Zan sa wuta a Yahuda da za tă ƙone kagarun Urushalima.”
6 Itsho njalo iNkosi: Ngenxa yeziphambeko ezintathu zakoIsrayeli, langenxa yezine, kangiyikuphambula isijeziso sabo, ngoba bathengisa olungileyo ngesiliva, loswelayo ngamanyathela amabili,
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Isra’ila, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun sayar da adalai waɗanda suka kāsa biyan bashinsu. Sun kuma sayar da matalauta waɗanda bashinsu bai ma kai ko kuɗin bi-labi ba.
7 abaphefuzelela uthuli lomhlaba oluphezu kwekhanda labayanga, baphambukisa indlela yabamnene; njalo umuntu loyise baya entombini, ukuze bangcolise ibizo lami elingcwele.
Sun tattake kawunan matalauta kamar yadda suke taka laka suka kuma danne wa marasa galihu gaskiya. Uba da ɗa su na kwana da yarinya guda, suna kuma ɓata sunana mai tsarki.
8 Bacambalale ezembathweni zesibambiso eceleni kwalelo lalelo ilathi, banathe iwayini labalahliweyo endlini yabonkulunkulu babo.
Suna kwanciya kurkusa da kowane bagade a kan tufafin da suka karɓe jingina. A gidajen allolinsu sukan sha ruwan inabin da suka karɓo daga wurin waɗanda suka ci wa tara.
9 Kanti mina ngachitha umAmori phambi kwabo, obude bakhe babunjengobude bamasedari, eqine njengama-okhi; kodwa ngachitha isithelo sakhe ngaphezulu, lempande zakhe ngaphansi.
“Na hallaka mutumin Amoriyawa a gabansu, ko da yake ya yi dogo kamar itacen al’ul kuma mai ƙarfi kamar itacen oak. Na hallaka’ya’yan itatuwansa daga sama, da kuma jijiyoyinsa daga ƙasa.
10 Futhi mina ngalenyusa elizweni leGibhithe, ngalikhokhela enkangala iminyaka engamatshumi amane, ukuze lidle ilifa lelizwe lomAmori.
Na fitar da ku daga ƙasar Masar, na kuma bishe ku tsawon shekaru arba’in a cikin hamada don in ba ku ƙasar Amoriyawa.
11 Ngavusa abanye emadodaneni enu babe ngabaprofethi, labanye emajaheni enu babe ngamaNaziri. Kakunjalo yini, lina bantwana bakoIsrayeli? itsho iNkosi.
“Na kuma tā da annabawa daga cikin’ya’yanku maza waɗansu kuma su zama keɓaɓɓu daga cikin samarinku. Ba haka ba ne, mutanen Isra’ila?” In ji Ubangiji.
12 Kodwa lawanathisa amaNaziri iwayini, lalaya abaprofethi lisithi: Lingaprofethi.
“Amma kuka sa keɓaɓɓun suka sha ruwan inabi kuka kuma umarci annabawa kada su yi annabci.
13 Khangelani, ngizalicindezela phansi, njengenqola igcwele izithungo icindezela.
“Saboda haka, yanzu zan murƙushe ku kamar yadda amalanke yakan murƙushe sa’ad da aka yi masa labtun hatsi.
14 Ngakho isiphephelo sizabhubha kolejubane, lolamandla kayikuqinisa amandla akhe, leqhawe kaliyikukhulula impilo yalo.
Masu gudu da sauri ba za su tsira ba, masu ƙarfi ba za su iya yin amfani da ƙarfinsu ba, jarumi kuma ba zai iya ceton ransa ba.
15 Lophethe idandili kayikuma, lolenyawo ezilula kayikuzikhulula, logade ibhiza kayikukhulula impilo yakhe.
’Yan baka ba za su iya dāgewa ba, masu saurin gudu ba za su tsira ba mahayin dawakai kuma ba zai tsere da ransa ba.
16 Lolenhliziyo eqinileyo phakathi kwamaqhawe uzabaleka eze ngalolosuku, itsho iNkosi.
Ko jarumawa mafi jaruntaka za su gudu tsirara a ranan nan,” in ji Ubangiji.

< U-Amosi 2 >