< Imisebenzi 15 >

1 Kwasekusehla abathile bevela eJudiya, bafundisa abazalwane ukuthi: Nxa lingasokwanga ngokwesiko likaMozisi, lingesindiswe.
Waɗansu mutane suka gangara daga Yahudiya zuwa Antiyok suna kuma koya wa’yan’uwa cewa, “Sai ko an yi muku kaciya bisa ga al’ada da Musa ya koyar, in ba haka ba, ba za ku sami ceto ba.”
2 Ngakho kwathi sekulokuphambana lokuphikisana okungekuncinyane ngoPawuli loBarnabasi bemelane labo, bamisa ukuthi uPawuli loBarnabasi labanye abathile kubo benyukele kubaphostoli labadala eJerusalema, ngaloludaba.
Wannan ya kai Bulus da Barnabas suka shiga babban gardama da muhawwara da su. Saboda haka aka naɗa Bulus da Barnabas tare da waɗansu masu bi, su haura zuwa Urushalima don su ga manzanni da dattawa a kan wannan magana.
3 Ngakho, kwathi sebephelekezelwe libandla, badabula iFenekiya leSamariya, balandisa ngokuphenduka kwabezizwe; benzela bonke abazalwane intokozo enkulu.
Ikkilisiya ta raka su suka tafi, yayinda suke ratsawa ta Funisiya da Samariya, suka ba da labari yadda Al’ummai suka tuba. Wannan labarin ya sa dukan’yan’uwa suka yi murna ƙwarai.
4 Kwathi sebefikile eJerusalema, bemukelwa libandla labaphostoli labadala, njalo balandisa ukuthi zingakanani izinto uNkulunkulu ayezenze labo.
Sa’ad da suka isa Urushalima, sai ikkilisiya da manzanni da kuma dattawa suka marabce su, sai suka ba su rahoton dukan abin da Allah ya aikata ta wurinsu.
5 Kodwa kwasukuma abanye abakholwayo abangabehlelo labaFarisi, besithi: Kufanele ukubasoka, lokubalaya bagcine umlayo kaMozisi.
Sai waɗansu daga cikin masu bin da suke na ƙungiyar Farisiyawa suka miƙe tsaye suka ce, “Dole ne a yi wa Al’ummai kaciya a kuma bukace su su yi biyayya da dokokin Musa.”
6 Kwasekubuthana abaphostoli labadala ndawonye ukuze baluhlole loludaba.
Sai manzanni da dattawa suka taru don su duba maganar.
7 Kwathi sebephikisene kakhulu, uPetro wasukuma wathi kubo: Madoda bazalwane, lina liyazi ukuthi ensukwini zakuqala uNkulunkulu wakhetha phakathi kwethu, ukuthi ngomlomo wami abezizwe balizwe ilizwi levangeli, bakholwe.
Bayan aka yi muhawwara da sosai, sai Bitrus ya miƙe tsaye ya yi musu jawabi ya ce, “’Yan’uwa, kun san cewa a kwanakin baya Allah ya yi zaɓe a cikinku don Al’ummai su ji daga leɓunana saƙon bishara su kuma gaskata.
8 Njalo uNkulunkulu umazi wenhliziyo wabafakazela, ebanika uMoya oyiNgcwele, lanjengathi;
Allah, wanda ya san zuciya, ya nuna cewa ya karɓe su ta wurin ba su Ruhu Mai Tsarki, kamar yadda ya ba mu.
9 futhi kehlukanisanga phakathi kwethu labo, ehlambulula inhliziyo zabo ngokholo.
Bai nuna bambanci tsakaninmu da su ba, gama ya tsarkake zukatansu ta wurin bangaskiya.
10 Pho-ke limlingelani uNkulunkulu, ngokubeka ijogwe entanyeni yabafundi, obaba bethu kanye lathi esingabanga lamandla okulithwala?
To, fa, don me kuke ƙoƙari ku gwada Allah ta wurin ɗora wa almajiran nan kayan da mu ko kakanninmu ba mu iya ɗauka ba?
11 Kodwa sikholwa ukuthi sisindiswa ngomusa weNkosi uJesu Kristu, ngandlelanye labo.
A’a! Mun gaskata cewa ta wurin alherin Ubangiji Yesu ne muka sami ceto, kamar yadda su ma suka samu.”
12 Ixuku lonke laselithula; laselisizwa uBarnabasi loPawuli belandisa ukuthi zingakanani izibonakaliso lezimangaliso uNkulunkulu ayezenze ngabo phakathi kwabezizwe.
Sai duk taron suka yi tsit yayinda suke sauraron Barnabas da Bulus suna ba da labari game da ayyuka da kuma abubuwan banmamakin da Allah ya yi a cikin Al’ummai ta wurinsu.
13 Kwathi bona sebeqedile ukukhuluma, uJakobe waphendula wathi: Madoda bazalwane, ngilalelani:
Da suka gama, sai Yaƙub ya yi magana ya ce, “’Yan’uwa, ku saurare ni.
14 USimeyoni uselandisile ukuthi uNkulunkulu wahambela njani abezizwe ekuqaleni ukuze azuzele ibizo lakhe abantu kubo.
Siman ya bayyana mana yadda Allah da farko ya nuna damuwarsa ta wurin ɗaukan mutane daga cikin Al’ummai su zama nasa.
15 Njalo amazwi abaprofethi ayavumelana lalokhu, njengoba kulotshiwe ukuthi:
Kalmomin annabawa sun yi daidai da wannan, kamar yadda yake a rubuce cewa,
16 Emva kwalezizinto ngizabuya, ngilakhe futhi ithabhanekele likaDavida eliwileyo; njalo ngizakwakha okudilikileyo kwalo, njalo ngilimise;
“‘Bayan wannan zan koma in kuma sāke gina tentin Dawuda da ya rushe. Kufansa zan sāke gina, in kuma mai da shi,
17 ukuze abaseleyo babantu bayidinge iNkosi, labezizwe bonke ibizo lami elibizwa phezu kwabo, itsho iNkosi eyenza lezizinto zonke.
don ragowar mutane su nemi Ubangiji, kuma duk Al’umman da suke kira bisa sunana, in ji Ubangiji, wanda yake yin waɗannan abubuwa’
18 Kwaziwa kuNkulunkulu imisebenzi yonke yakhe kusukela ephakadeni. (aiōn g165)
da aka sani tun zamanai. (aiōn g165)
19 Ngakho mina ngiquma ukuthi singabakhathazi labo kwabezizwe abaphendukela kuNkulunkulu;
“Saboda haka, a ganina, kada mu matsa wa Al’ummai waɗanda suke juyowa ga Allah.
20 kodwa sibabhalele ukuthi bazile amanyala ezithombe, lokufeba, lokukhanyiweyo, legazi.
A maimakon haka, ya kamata mu rubuta musu cewa, su guji abincin da alloli suka ƙazantar, da fasikanci, da naman dabbar da aka murɗe da kuma jini.
21 Ngoba uMozisi ulabo kusukela ezizukulwaneni zendulo abamtshumayelayo umuzi ngomuzi, efundwa emasinagogeni isabatha ngesabatha.
Gama Musa ya yi wa’azi a kowace birni tun zamanin dā, ana kuma karanta shi a majami’u kowane Asabbaci.”
22 Kwasekubonakala kukuhle kubaphostoli lakubadala kanye lebandla lonke, ukuthuma amadoda akhethiweyo phakathi kwabo eAntiyoki loPawuli loBarnabasi; babe ngoJudasi othiwa futhi nguBarsaba, loSilasi, amadoda angabakhokheli phakathi kwabazalwane,
Sai manzanni da dattawa, tare da dukan ikkilisiya, suka yanke shawara su zaɓi waɗansu daga cikin mutanensu su kuma aike su zuwa Antiyok tare da Bulus da Barnabas. Sai suka zaɓi Yahuda (wanda ake kira Barsabbas) da kuma Sila, mutum biyu da suke shugabanni cikin’yan’uwa.
23 basebebhala lokhu ngesandla sabo ukuthi: Abaphostoli labadala labazalwane kubazalwane abangabezizwe eAntiyoki leSiriya leKilikhiya, bayabingelela;
Tare da su suka aika da wannan wasiƙa. Daga manzanni da dattawa,’yan’uwanku. Zuwa ga Al’ummai masu bi a Antiyok, Suriya da Silisiya. Gaisuwa.
24 njengoba sizwile ukuthi abathile abaphume kithi balikhathazile ngamazwi, bedunga imiphefumulo yenu, besithi lisokwe lilonde umthetho, bona esingabalayanga;
Mun ji cewa, waɗansu da sun fita daga cikinmu ba tare da izininmu ba suka kuma dame ku, suna tā da hankalinku ta wurin abin da suka ce.
25 kwabonakala kukuhle kithi singqondonye, ukuthi siwakhethe amadoda siwathume kini, kanye labathandekayo bethu uBarnabasi loPawuli,
Saboda haka dukanmu mun yarda mu zaɓi waɗansu mutane mu kuma aike su wurinku tare da ƙaunatattun abokanmu Barnabas da Bulus
26 abantu abanikele impilo yabo ngenxa yebizo leNkosi yethu uJesu Kristu.
mutanen da suka sa rayukansu cikin hatsari saboda sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi.
27 Ngakho sithumile uJudasi loSilasi, abazakuthi labo ngelizwi lomlomo balitshele izinto ezifananayo.
Saboda haka muna aika Yahuda da Sila don su tabbatar muku da baki abin da muka rubuta.
28 Ngoba kwabonakala kukuhle kuMoya oNgcwele, lakithi, ukuthi singalethesi umthwalo omkhulu, ngaphandle kwalezizinto ezifunekayo:
Ya gamshe Ruhu Mai Tsarki da mu ma kada a ɗora muku nauyi fiye da na waɗannan abubuwa.
29 Ukuthi lizile okuhlatshelwe izithombe, legazi, lokukhanyiweyo, lokufeba; lezizinto nxa lizazizila, lizabe lenze kuhle. Salani kuhle.
Ku guji abincin da aka yi wa alloli hadaya, da jini, da naman dabbar da aka murɗe da kuma fasikanci. Za ku kyauta in kun kiyaye waɗannan abubuwa. Ku huta lafiya.
30 Ngakho sebebakhululile beza eAntiyoki; futhi sebelihlanganisile ixuku, balinika incwadi.
Aka sallami mutanen sai suka gangara zuwa Antiyok, inda suka tara ikkilisiya wuri ɗaya suka ba da wasiƙar.
31 Kwathi sebefundile, bathokoza ngenduduzo.
Mutanen suka karantata suka kuma yi farin ciki saboda saƙonta mai ƙarfafawa.
32 UJudasi kanye loSilasi, njengoba labo babengabaprofethi, balaya abazalwane ngamazwi amanengi, babaqinisa.
Yahuda da Sila, waɗanda su kansu annabawa ne, suka yi magana sosai don su gina su kuma ƙarfafa’yan’uwa.
33 Sebehlale isikhathi, bayekelwa basuka ngokuthula kubazalwane baya kubaphostoli,
Bayan suka yi’yan kwanaki a can, sai’yan’uwa suka sallame su da albarkar salama su dawo wurin waɗanda suka aike su.
34 kodwa kwabonakala kukuhle kuSilasi ukuthi asale khona.
35 UPawuli loBarnabasi basebesala eAntiyoki, befundisa betshumayela indaba ezinhle zelizwi leNkosi, kanye labanye abanengi.
Amma Bulus da Barnabas kuwa suka dakata a Antiyok, inda su da waɗansu da yawa suka yi koyarwa suka kuma yi wa’azin maganar Ubangiji.
36 Emva kwensuku ezithile uPawuli wasesithi kuBarnabasi: Ake sibuye sihambele abazalwane bethu emizini yonke, lapho esatshumayela khona ilizwi leNkosi, sibone ukuthi bahlezi njani.
Bayan’yan kwanaki sai Bulus ya ce wa Barnabas, “Mu koma mu ziyarci’yan’uwa a duk garuruwan da muka yi wa’azin bisharar Ubangiji mu ga yadda suke.”
37 UBarnabasi wasehlosa ukuthatha uJohane, othiwa nguMarko, ahambe labo.
Barnabas ya so Yohanna, wanda ake kira Markus ya tafi tare da su,
38 Kodwa uPawuli wacabanga ukuthi kufanele ukuthi bangamthathi ahambe labo lowo owabatshiya ePamfiliya, kaze aya labo emsebenzini.
amma Bulus bai ga ya kyautu ya tafi da shi ba, domin ya yashe su a Famfiliya bai kuwa ci gaba tare da su a aikin ba.
39 Kwasekuvela ukuphikisana okukhulu, baze behlukana phakathi; uBarnabasi wasethatha uMarko wahamba laye ngomkhumbi, baya eKuprosi.
Suka sami saɓanin ra’ayi tsakaninsu har suka rabu. Barnabas ya ɗauki Markus suka shiga jirgin ruwa zuwa Saifurus,
40 Kodwa uPawuli wakhetha uSilasi wasuka wahamba, esenikelwe emuseni kaNkulunkulu ngabazalwane.
amma Bulus ya zaɓi Sila suka kuwa tashi, bayan’yan’uwa suka danƙa su ga alherin Ubangiji.
41 Wasedabula iSiriya leKilikhiya, eqinisa amabandla.
Ya ratsa ta Suriya da Silisiya, yana ƙarfafa ikkilisiyoyi.

< Imisebenzi 15 >