< 2 UPhetro 2 >

1 Kodwa kwakukhona labaprofethi bamanga phakathi kwabantu, njengoba lakini kuzakuba khona abafundisi bamanga, abazangenisa ngensitha imfundiso ezehlukanisayo ezichithayo, bephika leNkosi eyabathengayo, bezehlisela ukuchitheka okuphangisayo,
Annabawan karya sun zo ga mutane, hakannan kuma malaman karya suma sun zo. A asirce za su zo maku da karkatacciyar koyarwa mai hallakarwa, su kuma yi musun sanin Ubangiji da ya fanshe su. Su na jawowa kansu hallaka da sauri.
2 labanengi bazalandela incithakalo zabo; okungabo indlela yeqiniso izahlanjazwa,
Da yawa za su bi gurbinsu, kuma ta wurinsu za a sabawa sahihiyar gaskiya.
3 njalo emhawini ngamazwi alungisiweyo bazakwenza inzuzo ngani; okulahlwa kwabo kwakudala kakulibalanga, lencithakalo yabo kayiwozeli.
Ta wurin hadama za su ribace ku ta wurin maganganunsu na yaudara. Hallakarsu ba za ta yi jinkiri ba; hukuncinsu na nan tafe.
4 Ngoba uba uNkulunkulu engaziyekelanga ingilosi ezonayo, kodwa eziphosela esihogweni ezinikela emaketaneni obumnyama ukuze zigcinelwe isigwebo; (Tartaroō g5020)
Allah bai kebe mala'ikkun da suka yi zunubi ba. Maimakon haka ya tura su a cikin bakin duhun jahannama daure da sarkoki, har ya zuwa ranar shari'a. (Tartaroō g5020)
5 njalo kaliyekelanga ilizwe lendulo, kodwa walondoloza owesificaminwembili uNowa umtshumayeli wokulunga, mhla eletha uzamcolo emhlabeni wabeyisa uNkulunkulu;
Hakan nan kuma bai kebe duniya ta zamanin da ba. Maimakon haka, ya kebe Nuhu, wanda yake wa'azin adalci, tare da mutane bakwai, lokacin da ya kawo ambaliyar ruwan Tsufana a fuskar duniyar marasa bin Allah.
6 ngokuyichitha eyitshisa imizi yeSodoma leGomora waseyilahla, waseyenza isibonelo kulabo abazakweyisa uNkulunkulu;
Sa'annan Allah ya kone biranen Sadoma da Gomrata da wuta ya maishe su toka, wannan ya zama misalin abin da zai faru da marasa ibada.
7 wasemophula uLothi olungileyo, owahlutshwa yikuhamba ngamanyala kwabangalunganga;
Amma ga adalinnan Lutu, wanda ya zaku a ransa ta wurin miyagun halayen mutanen, Ubangiji kuwa ya cece shi.
8 ngoba lowo olungileyo, ehlala phakathi kwabo, ngokubona lokuzwa insuku ngensuku wazwisa ubuhlungu umphefumulo wakhe olungileyo ngemisebenzi yabo engelamthetho;
Ga wannan mutum mai adalci, wanda yayi zama a cikinsu kowace rana ransa na baci, domin abin da yake gani yake kuma ji.
9 iNkosi iyakwazi ukubophula ekulingweni labo abamkhonzayo uNkulunkulu, lokubagcina abangalunganga kuze kube lusuku lwesigwebo, bajeziswe;
Saboda haka Allah ya san yadda zai ceci masu adalci daga gwaji, da yadda kuma zai kama masu rashin adalci da hukunci a ranar shari'a.
10 kodwa ikakhulu bona abalandela inyama enkanukweni engcolileyo, labadelela ubukhosi. Abangakhathaliyo, abalenkani, kabesabi ukuhlambaza ubukhosi;
Wannan kuwa musamman gaskiya ce ga wadanda suka ci gaba da ayyuka na jiki suka kuma raina masu mulki. Suna da taurin kai da kuma yin ganin dama. Ba sa tsoron sabo ga wadanda aka daukaka.
11 kanti ingilosi, ezinkulu ngamandla langengalo, kazilethi isigwebo senhlamba ukumelana labo phambi kweNkosi.
Ko da shike mala'iku suna da karfi da iko fiye da su, amma basu kawo karar batanci a kansu a gaban Ubangiji ba.
12 Kodwa laba, njengezinyamazana ngemvelo ezingelangqondo ezazalelwa ukubanjwa lokubulawa, bahlambaza izinto abangazaziyo, bazabhujiswa ekuboleni kwazo,
Amma wadannan dabbobi marassa tunani an yi su ne musamman domin a kama a yanka. Suna sabawa abin da ba su sani ba. Zasu halaka.
13 bazakwemukela umvuzo wokungalungi, abathi kuyintokozo ukuminza emini; bayisici loyangiso, bejabula enkohlisweni zabo, besidla idili lani,
Za su sami sakamakon mugun aikinsu. Suna tunanin yin nishadi da rana abin annashuwa ne. Su kan su tababbu ne. Suna jin dadin ayyukansu na yaudara yayin da suke liyafa tare da ku.
14 balamehlo agcwele ubufebe, labangayekeli isono, bayenga imiphefumulo ebuthakathaka, belenhliziyo ezejwayele ubuhwaba, abantwana besiqalekiso;
Suna da idanun sha'awace sha'awacen mata mazinata; ba sa koshi da aikata zunubi. Suna rinjayar wandanda ba su da tsayayyan hankali zuwa ga munanan ayyuka, kuma sun kafa zukatansu ga hadama, su 'ya'yan la'ana ne!
15 batshiye indlela eqondileyo baduha, balandela indlela kaBalami kaBosori, owathanda inzuzo yokungalungi,
Sun bar bin hanyar gaskiya. Sun bijire kuma sun bi hanyar Bal'amu dan Be'or wanda yake kaunar ribar rashin adalci.
16 kodwa waba lokusolwa kwesakhe isiphambeko; ubabhemi oyisimungulu, ekhuluma ngelizwi lomuntu, wanqanda ubuhlanya bomprofethi.
Amma ya karbi tsautawa domin zunubinsa. Jaki ma da baya magana ya tsauta wa haukan annabin da muryar dan adam.
17 Laba bayimithombo engelamanzi, amayezi aqhutshwa yisiphepho, okugcinelwe bona ubumnyama bomnyama kuze kube phakade. (questioned)
Wadannan mutane suna kamar mabulbullai da babu ruwa. suna nan kamar gizagizai da iska ke korawa. Duhu mai tsanani yana jiransu.
18 Ngoba bakhuluma okokuziqakisa okweze, babayenga ngenkanuko zenyama langobufebe labo abaphunyuke sibili kubo abahamba ekuduheni,
Su masu babatu ne da girman kai. suna yadaurar mutane ta wurin sha'awowin jiki. Suna yaudarar mutane da suke kokarin su tsere daga wadanda suke rayuwa cikin kuskure.
19 bebathembisa inkululeko, bona uqobo beyizigqili zokubola; ngoba lowo umuntu ehlulwe ngaye, lakuye wenziwa isigqili.
Suna masu alkawarin yanci, amma su da kan su bayi ne ga zunubi. Domin mutum bawa ne ga duk abinda ya rinjaye shi.
20 Ngoba uba sebephunyukile ekungcoleni komhlaba ngolwazi lweNkosi loMsindisi uJesu Kristu, besebebuya behilelwa behlulwa yikho, izinto zokucina sezibe zimbi kubo kulezokuqala.
Duk wanda ya kubuta daga shashanci na duniya ta wurin sanin Ubangiji da mai Ceto Yesu Almasihu, sa'annan ya koma cikin shashaci, yanayinsu na karshe ya zama da muni fiye da na farkon.
21 Ngoba ngabe kwaba ngcono kubo uba babengayazanga indlela yokulunga, kulokuthi sebeyazile bafulathele umlayo ongcwele onikelwe kibo.
Da ma zai fi masu kada su san hanyar adalci da su san ta amma sa'annan su juya daga ka'ida mai tsarki wanda aka damka masu.
22 Kodwa kubehlele lokhu okwesaga esiqinisileyo esithi: Inja ibuyela kwawayo amahlanzo; lengulube ensikazi egezileyo ekugiqikeni edakeni.
Wannan karin magana ya zama gaskiya a kan su: “Kare ya dawo yana lashe amansa. Aladen da akayi masa wanka ya koma cikin tabo.”

< 2 UPhetro 2 >