< 2 Amakhosi 6 >
1 Amadodana abaprofethi asesithi kuElisha: Khangela-ke, indawo esihlala kiyo lawe iminyene kakhulu kithi.
Sai ƙungiyar annabawa suka ce wa Elisha, “Duba, wurin da muke taruwa ya kāsa mana.
2 Akusiyekele sihambe siye eJordani, sithathe khona, ngulowo lalowo isigodo esisodwa, sizenzele khona indawo yokuhlala kiyo. Wasesithi: Hambani.
Bari mu je Urdun, inda kowannenmu zai saro itace; mu gina inda za mu zauna.” Sai ya ce musu, “Ku je.”
3 Omunye wasesithi: Akuvume, uhambe lenceku zakho. Wasesithi: Mina ngizahamba.
Sai ɗayansu ya ce, “Ba za ka zo tare da bayinka ba?” Sai Elisha ya ce “Zan zo.”
4 Wasehamba labo; sebefikile eJordani bagamula izihlahla.
Ya kuma tafi tare da su. Suka tafi Urdun suka fara saran itatuwa.
5 Kodwa omunye esagamula ugodo, insimbi yawela emanzini. Wasememeza esithi: Maye, nkosi yami! Ngoba belebolekiwe.
Yayinda ɗayansu yake cikin saran itace, sai kan gatarin ya fāɗi a ruwa, sai ya ce, “Kash, ranka yă daɗe, kayan aro ne fa!”
6 Umuntu kaNkulunkulu wasesithi: Iwele ngaphi? Wasemtshengisa indawo. Wasegamula uswazi, waluphosela khona, wenza insimbi yandenda.
Sai mutumin Allah ya ce, “Daidai ina ya fāɗa?” Da ya nuna masa wurin, sai Elisha ya yanka ɗan sanda ya jefa a wurin, ya sa kan gatarin ya taso sama.
7 Wasesithi: Zenyulele yona. Waseselula isandla sakhe, wayithatha.
Sai ya ce masa, “Ka ɗauko.” Sai mutumin ya miƙa hannu ya ɗauka.
8 Kwathi inkosi yeSiriya isilwa loIsrayeli yacebisana lenceku zayo isithi: Ekuthanathaneni izakuba yinkamba yami.
To, fa, sarkin Aram yana yaƙi da Isra’ila. Bayan ya tattauna da hafsoshinsa, sai ya ce, “Zan kafa sansanina a wurin kaza da kaza.”
9 Umuntu kaNkulunkulu wasethumela enkosini yakoIsrayeli esithi: Qaphela ungedluli kulindawo, ngoba amaSiriya ehlele khona.
Sai mutumin Allah ya aika wa sarkin Isra’ila cewa, “Ka yi hankali da wuce wuri kaza, domin Arameyawa za su gangara can.”
10 Inkosi yakoIsrayeli yasithumela kuleyondawo umuntu kaNkulunkulu ayitshela yona wayixwayisa ngayo. Yasizilondoloza khona, kungekanye, njalo kungekabili.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya lura da inda mutumin Allah ya ambata. Sau da sau Elisha yakan yi wa sarki kashedi, don haka ya riƙa taka yi tsantsan a wuraren nan.
11 Inhliziyo yenkosi yeSiriya yasikhathazeka kakhulu ngenxa yalinto. Yasibiza inceku zayo yathi kuzo: Kaliyikungitshela yini ukuthi ngubani kithi ongowenkosi yakoIsrayeli?
Wannan ya husata sarkin Aram. Ya kira hafsoshinsa ya tambaye su ya ce, “Ku faɗa mini, wane ne a cikinmu yake gefen sarkin Isra’ila?”
12 Omunye wenceku zakhe wasesithi: Hatshi, nkosi yami, nkosi; kodwa uElisha umprofethi okoIsrayeli uyayitshela inkosi yakoIsrayeli amazwi owakhuluma phakathi kwekamelo lakho lokulala.
Sai ɗaya daga cikin hafsoshinsa ya ce, “Babu waninmu, ranka yă daɗe; Elisha, annabin da yake a Isra’ila ne, yake faɗa wa sarkin Isra’ila dukan zancen da ka yi a ɗakinka.”
13 Yasisithi: Hambani liyebona lapho akhona, ukuze ngithume ngimthathe. Wasetshelwa kwathiwa: Khangela, useDothani.
Sai sarki ya ba da umarni ya ce, “Ku je ku tabbatar da inda yake don in aika mutane a kamo shi.” Sai ya sami rahoto cewa, “Yana a Dotan.”
14 Yasithuma khona amabhiza lezinqola lebutho elinzima; basebefika ebusuku, bawuzingelezela umuzi.
Sai ya aika da dawakai da kekunan yaƙi da babban rukunin soja zuwa can. Suka bi dare, suka kewaye birnin.
15 Kwathi inceku yomuntu kaNkulunkulu isivukile ngovivi yaphuma, khangela-ke, ibutho lizingelezele umuzi kanye lamabhiza lezinqola. Inceku yakhe yasisithi kuye: Maye, nkosi yami! Sizakwenza njani?
Sa’ad da bawan mutumin Allah ya farka ya kuma fita kashegari da sassafe, sai ga mayaƙa tare da dawakai da kekunan yaƙi sun kewaye birni. Sai bawan ya ce, “Ranka yă daɗe! Me za mu yi?”
16 Wasesithi: Ungesabi, ngoba labo abalathi banengi okwedlula labo abalabo.
Sai annabin ya ce, “Kada ka ji tsoro, waɗanda suke tare da mu sun fi waɗanda suke tare da su.”
17 UElisha wasekhuleka wathi: Nkosi, akuvule amehlo ayo ukuze ibone. INkosi yasiwavula amehlo alelojaha, laselibona, khangela-ke, intaba igcwele amabhiza lenqola zomlilo zihanqe uElisha.
Sa’an nan Elisha ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji, ka buɗe idanunsa yă gani!” Sai Ubangiji ya buɗe idanun bawan, ya duba, ya ga tuddai cike da dawakai da keken yaƙin wuta kewaye da Elisha.
18 Sebehlele kuye, uElisha wakhuleka eNkosini wathi: Akutshaye lababantu ngobuphofu. Yasibatshaya ngobuphofu njengokwelizwi likaElisha.
Yayinda abokan gāba suka gangaro wajensa, sai Elisha ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ka sa mutanen nan su zama makafi.” Sai Ubangiji ya buge su da makanta kamar yadda Elisha ya roƙa.
19 UElisha wasesithi kibo: Kayisiyo le indlela, futhi kayisiwo lo umuzi; ngilandelani, ngizalisa kulowomuntu elimdingayo. Kodwa wabasa eSamariya.
Elisha ya ce musu, “Wannan ba ita ce hanyar ba, ba kuma gari ke nan ba, ku bi ni, zan kuwa kai ku wurin mutumin da kuke nema!” Sai ya kai su Samariya.
20 Kwasekusithi sebengene eSamariya, uElisha wathi: Nkosi, vula amehlo alaba ukuze babone. INkosi yasivula amehlo abo, basebebona; khangela-ke, babephakathi kweSamariya.
Bayan suka shiga birnin, sai Elisha ya ce, “Ubangiji, ka buɗe idanun mutanen nan don su gani.” Sa’an nan Ubangiji ya buɗe idanunsu suka ga kansu a tsakiyar Samariya.
21 Inkosi yakoIsrayeli yasisithi kuElisha ibabona: Baba, ngibatshaye, ngibatshaye yini?
Da sarkin Isra’ila ya gan su, sai ya tambayi Elisha ya ce, “In kashe su ne, mahaifina? In kashe su?”
22 Wasesithi: Ungatshayi. Ungatshaya yini labo obathumbe ngenkemba yakho langedandili lakho? Beka isinkwa lamanzi phambi kwabo ukuze badle banathe, baye enkosini yabo.
Elisha ya ce, “Kada ka kashe su. Za ka kashe mutanen da ka kame da takobi ko bakanka? Ka ba su abinci da ruwa su ci, su sha, sa’an nan su koma wurin maigidansu.”
23 Yasibalungisela idili elikhulu; sebedlile banatha, yabayekela bahamba, baya enkosini yabo. Ngakho amaviyo amaSiriya kawabesaphinda ukubuya elizweni lakoIsrayeli.
Saboda haka aka shirya musu babban liyafa, bayan sun ci, suka kuma sha, sai ya tura su zuwa wurin maigidansu. Ta haka’yan harin Aram suka daina kai hari a yankin Isra’ila.
24 Kwasekusithi emva kwalokho uBenihadadi inkosi yeSiriya wabutha ibutho lakhe lonke, wenyuka wavimbezela iSamariya.
Bayan wani lokaci, Ben-Hadad sarkin Aram ya tattara dukan rundunarsa, ya je ya kewaye Samariya da yaƙi.
25 Kwasekusiba lendlala enkulu eSamariya; khangela-ke, bayivimbela, kwaze kwathi inhloko kababhemi yathengiswa ngenhlamvu zesiliva ezingamatshumi ayisificaminwembili, lengxenye eyodwa kwezine yegajana lobudolilo bejuba ngenhlamvu zesiliva ezinhlanu.
Aka yi babban yunwa a cikin birnin. Saboda daɗewar wannan kewayewar da aka yi wa birnin, sai yunwa ta ɓarke a birnin, har ana sayar da kan jaki a kan shekel tamanin, kashin kurciya kuma a kan shekel biyar.
26 Kwasekusithi inkosi yakoIsrayeli idlula phezu komduli, owesifazana wamemeza kiyo esithi: Siza, nkosi yami, nkosi!
Yayinda sarkin Isra’ila yake wucewa kusa da katanga, sai wata mace ta yi masa kuka ta ce, “Ka taimake ni, ranka yă daɗe, sarki!”
27 Yasisithi: Uba iNkosi ingakusizi, ngikusize ngokuvela ngaphi? Ebaleni lokubhulela kumbe esikhamelweni sewayini yini?
Sai sarki ya amsa ya ce, “In Ubangiji bai taimake ki ba, me zan iya yi? Ina da hatsi ko ruwan inabin da zan ba ki ne?”
28 Inkosi yasisithi kuye: Ulani? Wasesithi: Lo owesifazana uthe: Letha indodana yakho ukuze siyidle lamuhla; kusasa-ke sizakudla indodana yami.
Sa’an nan ya tambaye ta ya ce, “Me ya faru?” Sai ta amsa ta ce, “Wannan mace ta ce mini, ‘Kawo ɗanki mu ci yau, gobe kuwa mu ci ɗana.’
29 Sasesiyipheka indodana yami, sayidla. Ngasengisithi kuye ngosuku olulandelayo: Letha indodana yakho ukuze siyidle. Kodwa wayifihla indodana yakhe.
Saboda haka muka dafa ɗana muka ci. Kashegari na ce mata, ‘Kawo ɗanki mu ci,’ amma ta ɓoye shi.”
30 Kwasekusithi inkosi isizwa amazwi alowo owesifazana yadabula izigqoko zayo. Yedlula phezu komduli; abantu basebebona, khangela-ke, kwakulesaka emzimbeni wayo, ngaphakathi.
Da sarki ya ji maganar macen sai ya yage rigunansa. Sa’ad da sarki yake wucewa a kan katangar birnin, sai mutane suka gan yana saye da rigar makoki a ciki.
31 Yasisithi: UNkulunkulu kenze njalo kimi langokunjalo engezelele, uba ikhanda likaElisha indodana kaShafati lizahlala kuye lamuhla.
Ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani har ma fiye da haka, idan ban cire kan Elisha ɗan Shafat yau ba!”
32 Kodwa uElisha wayehlezi endlini yakhe labadala babehlezi laye. Inkosi yasithuma umuntu esuka phambi kwayo; isithunywa singakafiki kuye, yena wathi kubadala: Liyabona yini ukuthi indodana le yombulali ithume ukususa ikhanda lami? Bonani, lapho isithunywa sifika, livale umnyango, lisibandezele emnyango. Kakusizisinde zenkosi yaso yini emva kwaso?
To, Elisha yana zaune a cikin gidansa, dattawa kuwa suna zaune tare da shi. Sai sarki ya aiki ɗan aika yă ci gaba, amma kafin ɗan aikan yă isa, Elisha ya ce wa dattawan, “Kun gani ko? Wannan mai kisa ya aiko a cire mini kai! To, idan ɗan aikan ya iso, sai ku rufe ƙofar da ƙarfi, ku bar shi a waje. Ba da jimawa ba, maigidansa zai bi bayansa?”
33 Kwathi esakhuluma labo, khangela-ke, inkosi yehlela kuye, yathi: Khangela, lobububi buvela eNkosini. Ngingabe ngisayilindelelani iNkosi?
Yana magana da su ke nan, sai ga ɗan aikan ya gangaro wajensa. Sarki kuma ya ce, “Wannan bala’in daga wurin Ubangiji ya fito. Don me zan sa zuciya ga Ubangiji kuma?”