< 2 Amakhosi 22 >

1 UJosiya wayeleminyaka eyisificaminwembili lapho esiba yinkosi; wabusa iminyaka engamatshumi amathathu lanye eJerusalema. Lebizo likanina lalinguJedida indodakazi kaAdaya weBhozikhathi.
Yosiya yana da shekara takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara talatin da ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Yedida’yar Adahiya; mutuniyar Bozkat.
2 Wasesenza okulungileyo emehlweni eNkosi, wahamba ngayo yonke indlela kaDavida uyise, kaze aphambukela ngakwesokunene langakwesokhohlo.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma bi dukan gurbin kakansa Dawuda, bai bauɗe hagu ko dama ba.
3 Kwasekusithi ngomnyaka wetshumi lesificaminwembili wenkosi uJosiya, inkosi yathuma uShafani indodana kaAzaliya indodana kaMeshulamu, umabhalane, endlini yeNkosi, esithi:
A shekara ta goma sha takwas ta mulkinsa, Sarki Yosiya ya aiki Shafan ɗan Azaliya, ɗan Meshullam, magatakarda, zuwa haikalin Ubangiji. Ya ce,
4 Yenyukela kuHilikhiya umpristi omkhulu ukuthi ahlanganise imali elethwe endlini yeNkosi, abalindi bombundu womnyango ababeyiqoqe ebantwini.
“Ka haura zuwa wurin Hilkiya babban firist ka sa yă shirya kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji, wanda masu tsaron ƙofa suka tara daga mutane.
5 Kabayinikele esandleni sabenzi bomsebenzi abamiswe phezu kwendlu yeNkosi, kabayinike abenzi bomsebenzi osendlini yeNkosi, ukulungisa izikhala zendlu,
Ka sa su danƙa su a hannun waɗanda aka zaɓa don biyan ma’aikatan da suka yi gyara a haikalin Ubangiji,
6 kubabazi, lakubakhi, lakubabazi bamatshe, lokuthenga amapulanka lamatshe abaziweyo ukulungisa indlu.
wato, kafintoci, da magina, da masu tsara gini. Ka kuma sa su sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu don a gyara haikalin.
7 Kodwa akubalelwananga labo imali eyayinikelwe esandleni sabo ngoba benza ngokuthembeka.
Amma ba sa bukata su ba da bayanin kuɗin da aka danƙa musu domin suna aikinsu da aminci.”
8 UHilikhiya umpristi omkhulu wasesithi kuShafani umabhalane: Sengifice ugwalo lomlayo endlini yeNkosi. UHilikhiya wasenika uShafani ugwalo, waselufunda.
Hilkiya babban firist ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan, shi kuma ya karanta.
9 UShafani umabhalane wasefika enkosini, wabuyisela ilizwi enkosini wathi: Izinceku zakho seziyithulule imali eficwe endlini, zayinikela esandleni sabenzi bomsebenzi abamiswe phezu kwendlu yeNkosi.
Sa’an nan Shafan ya koma wurin sarki ya ce masa, “Hafsoshinka sun kwashe kuɗin da suke a haikalin Ubangiji, suka ba wa masu aiki da masu lura da haikalin.”
10 UShafani umabhalane wasebika enkosini esithi: UHilikhiya umpristi unginike ugwalo. UShafani waselufunda phambi kwenkosi.
Sa’an nan Shafan magatakarda ya ce wa sarki, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta shi a gaban sarki.
11 Kwasekusithi inkosi isizwile amazwi ogwalo lomlayo, yadabula izigqoko zayo.
Da sarki ya ji kalmomin Littafin Doka, sai ya kece tufafinsa.
12 Inkosi yasilaya uHilikhiya umpristi loAhikhamu indodana kaShafani loAkhibhori indodana kaMikhaya loShafani umabhalane loAsaya inceku yenkosi, isithi:
Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya firist, da Ahikam ɗan Shafan, da Akbor ɗan Mikahiya, da Shafan magatakarda, da kuma Asahiya mai hidimar sarki, ya ce,
13 Hambani liyengibuzela eNkosini mina labantu loJuda wonke mayelana lamazwi alolugwalo oluficiweyo; ngoba yinkulu intukuthelo yeNkosi esesiyibaselwe, ngoba obaba kabawalalelanga amazwi alolugwalo, ukwenza konke okubhaliweyo mayelana lathi.
“Ku je, ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da saboda jama’a da kuma saboda dukan Yahuda game da abin da wannan littafi da aka samo ya ƙunsa. Fushin Ubangiji mai girma ne a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye kalmomin littafin nan ba; ba su aikata bisa ga abin da yake a rubuce game da mu ba.”
14 Ngakho uHilikhiya umpristi loAhikhamu loAkhibhori loShafani loAsaya baya kuHulida umprofethikazi umkaShaluma indodana kaTikiva indodana kaHarihasi, umgcini wezigqoko. Wayehlala-ke eJerusalema esiGabeni seSibili. Basebekhuluma laye.
Sai Hilkiya firist, da Ahikam, Akbor, da Shafan, da kuma Asahiya suka je don su yi magana da annabiya Hulda, matan Shallum ɗan Tikba, ɗan Harhas, mai ajiyar tufafi. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
15 Wasesithi kibo: Itsho njalo iNkosi, uNkulunkulu kaIsrayeli: Mtsheleni lowomuntu olithume kimi:
Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ku faɗa wa mutumin da ya aike ku wurina,
16 Itsho njalo iNkosi: Khangela, ngizakwehlisela okubi kulindawo laphezu kwabakhileyo bayo, wonke amazwi ogwalo inkosi yakoJuda elufundileyo.
‘Ga abin da Ubangiji ya ce, zan kawo masifa wa wannan wuri da kuma wa kan mutanen wurin, bisa ga dukan abubuwan da suke a rubuce a cikin littafin da sarkin Yahuda ya karanta.
17 Ngenxa yokuthi bangidelile, batshisela abanye onkulunkulu impepha, ukuze bangithukuthelise ngawo wonke umsebenzi wezandla zabo. Ngakho intukuthelo yami izavutha imelene lale indawo, ingacitshwa.
Domin sun yashe ni suka ƙona turare wa waɗansu alloli, suka tozarta ni da dukan gumakan da hannuwansu suka sassaƙa, fushina zai yi ƙuna a kan wannan wuri, ba kuwa zai huce ba.’
18 Kodwa enkosini yakoJuda elithumileyo ukubuza eNkosini, lizakutsho njalo kuyo: Itsho njalo iNkosi, uNkulunkulu kaIsrayeli: Mayelana lamazwi eliwezwileyo:
Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da kalmomin da ka ji.
19 Ngoba inhliziyo yakho ibithambile, wazithoba phambi kweNkosi, lapho usizwa engikukhulume ngimelene lalindawo labakhileyo bayo, ukuthi bazakuba yincithakalo lesiqalekiso, wadabula izigqoko zakho, wakhala inyembezi phambi kwami, lami-ke ngizwile, kutsho iNkosi.
Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Ubangiji sa’ad da ka ji abin da na faɗa game da wannan wuri da mutanen wurin, cewa za su zama la’antattu da kuma kango, domin kuma ka kece tufafinka, ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
20 Ngakho, khangela, ngizakubuthela kuboyihlo, njalo uzabuthelwa engcwabeni lakho ngokuthula, lamehlo akho kawayikubona bonke ububi engizabehlisela phezu kwalindawo. Basebebuyisela ilizwi enkosini.
Saboda haka zan haɗa ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka kuma ba za su ga dukan wannan masifan da zan jawo wa wurin nan ba.’” Sai suka kai wa sarki abin da ta faɗa.

< 2 Amakhosi 22 >