< 2 Amakhosi 21 >

1 UManase wayeleminyaka elitshumi lambili lapho esiba yinkosi; wabusa iminyaka engamatshumi amahlanu lanhlanu eJerusalema. Lebizo likanina lalinguHefiziba.
Manasse yana da shekara goma sha biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara hamsin da biyar a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hefziba.
2 Wasesenza okubi emehlweni eNkosi njengokwamanyala ezizwe iNkosi eyazixotsha elifeni phambi kwabantwana bakoIsrayeli.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, ya bi munanan al’adun al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
3 Ngoba wabuya wakha indawo eziphakemeyo uyise uHezekhiya ayezichithile, wamisela uBhali amalathi, wenza isixuku, njengokwenza kukaAhabi inkosi yakoIsrayeli, wakhothamela ibutho lonke lamazulu, walikhonza.
Ya sāke gina masujadan da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe. Ya kuma gina wa Ba’al bagadai. Ya kafa ginshiƙin Ashera kamar yadda Ahab sarkin Isra’ila ya yi. Ya durƙusa wa dukan rundunan taurari ya yi musu sujada.
4 Wasesakha amalathi endlini yeNkosi, iNkosi eyathi ngayo: EJerusalema ngizabeka ibizo lami.
Ya gina bagadai a haikalin Ubangiji, wurin da Ubangiji ya ce, “A Urushalima ne zan sa Sunana.”
5 Wasesakhela ibutho lonke lamazulu amalathi emagumeni womabili endlini yeNkosi.
Cikin filaye biyu na haikalin Ubangiji kuwa, ya gina bagadai na dukan rundunan taurari.
6 Wasedabulisa indodana yakhe emlilweni, wachasisa ngemibono, wenza imilingo, wasebenza labalamadlozi labalumbayo. Wenza okubi kakhulu emehlweni eNkosi ukuyithukuthelisa.
Ya miƙa ɗansa hadaya ta ƙonawa, ya yi sihiri da tsubu, ya tuntuɓi masu duba da masu ruhohi. Ya aikata mugunta ƙwarai a gaban Ubangiji, ya sa Ubangiji ya yi fushi.
7 Wasemisa isithombe esibaziweyo sesixuku ayesenzile endlini, iNkosi eyakhuluma ngayo kuDavida lakuSolomoni indodana yakhe yathi: Kulindlu, leJerusalema engiyikhethe kuzo zonke izizwe zakoIsrayeli, ngizabeka ibizo lami kuze kube nininini.
Ya ɗauki siffar ginshiƙin Asherar da ya yi, ya sa a haikalin da Ubangiji ya ce wa Dawuda da ɗansa Solomon, “A cikin wannan haikali, da kuma cikin Urushalima inda na zaɓa daga kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
8 Kangisayikuzulisa unyawo lukaIsrayeli luphume futhi elizweni engalinika oyise, kuphela uba bezananzelela ukwenza njengakho konke engabalaya khona langokomlayo wonke inceku yami uMozisi eyabalaya wona.
Ba zan ƙara sa Isra’ilawa su fita daga ƙasar da na ba kakanninsu ba, idan dai za su kula su aikata dukan abin da na umarce su, su kuma kiyaye dukan dokokin da na ba wa bawana Musa yă umarce su.”
9 Kodwa kabalalelanga; uManase wasebaphambukisa ukuthi benze okubi okwedlula izizwe iNkosi eyazichitha phambi kwabantwana bakoIsrayeli.
Amma mutanen ba su kasa kunne ba. Manasse ya ɓad da su, har suka yi muguntar da ta fi ta al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
10 INkosi yasikhuluma ngezinceku zayo abaprofethi isithi:
Ubangiji ya yi magana ta bakin bayinsa annabawa,
11 Ngenxa yokuthi uManase inkosi yakoJuda wenzile lamanyala, wenze okubi okwedlula konke amaAmori akwenzayo, ayephambi kwakhe, wonisa loJuda ngezithombe zakhe.
“Manasse, sarkin Yahuda ya aikata waɗannan ƙazantattun zunubai. Ya aikata mugunta fiye da ta Amoriyawan da suka riga shi, ya kuma sa Yahuda ta bauɗe ta wurin yin zunubi saboda gumakansa.
12 Ngakho itsho njalo iNkosi, uNkulunkulu kaIsrayeli: Khangela, ngiletha okubi phezu kweJerusalema loJuda kuthi laye wonke ozwayo indlebe zakhe zombili zizakhenceza ngakho.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, zan jawo wa Urushalima da kuma Yahuda masifar da duk kunnen da ya ji, sai ya kusa suma.
13 Ngizakwelula phezu kweJerusalema intambo yeSamariya, lentambo yokulinganisa yendlu kaAhabi, ngiyesule iJerusalema njengowesula umganu, awesule awumbokothe.
Zan auna Urushalima da ma’aunin da na yi amfani da shi a kan Samariya, zan kuma yi amfani da magwajin da na yi amfani da shi a kan gidan Ahab. Zan shafe Urushalima yadda mutum yake wanke kwano yă kife.
14 Njalo ngizatshiya insali yelifa lami, ngibanikele esandleni sezitha zabo, babe ngokubanjiweyo lempango kwezitha zabo zonke,
Zan rabu da ragowar gādona, in kuma miƙa su ga maƙiyansu. Abokan gābansu za su washe suka kuma kwashi ganima daga gare su,
15 ngenxa yokuthi benzile okubi emehlweni ami, bayangithukuthelisa, kusukela osukwini oyise abaphuma ngalo eGibhithe ngitsho kuze kube lamuhla.
domin sun aikata mugunta a idanuna, suka kuma tsokane ni tun daga ranar da kakanninsu suka fito daga Masar, har yă zuwa yau.”
16 Futhi-ke uManase uchithile igazi elinengi kakhulu elingelacala waze wayigcwalisa iJerusalema kusukela ekuqaleni kuze kube sekucineni, ngaphandle kwesono sakhe enza ngaso uJuda ukuthi one, ukwenza okubi emehlweni eNkosi.
Ban da haka ma, Manasse ya zub da jinin marasa laifi har ya cika Urushalima daga wannan ɓangare zuwa wancan, ban da zunubin da ya sa Yahuda ta aikata, ta haka suka yi mugunta a gaban Ubangiji.
17 Ezinye-ke zezindaba zikaManase, lakho konke akwenzayo, lesono sakhe asonayo, kakubhalwanga yini egwalweni lwemilando yamakhosi akoJuda?
Game da sauran ayyukan mulkin Manasse, da duk abin da ya yi, har da zunubin da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
18 UManase waselala laboyise, wangcwatshelwa esivandeni sendlu yakhe, esivandeni sikaUza. UAmoni indodana yakhe wasesiba yinkosi esikhundleni sakhe.
Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a lambun fadansa, lambun Uzza. Sai Amon ɗansa ya gāje shi.
19 UAmoni wayeleminyaka engamatshumi amabili lambili lapho esiba yinkosi; wabusa iminyaka emibili eJerusalema. Lebizo likanina lalinguMeshulemethi indodakazi kaHaruzi weJotiba.
Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki shekara biyu a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Meshullemet’yar Haruz; ita mutuniyar Yotba ce.
20 Wasesenza okubi emehlweni eNkosi njengokwenza kukaManase uyise.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda Manasse mahaifinsa ya yi.
21 Wahamba ngendlela yonke uyise ahamba ngayo, wakhonza izithombe uyise azikhonzayo, wakhothama kuzo.
Ya bi duk gurbin mahaifinsa a kome, ya yi sujada ga gumakan da mahaifinsa ya yi wa, ya kuma durƙusa musu.
22 Wayidela iNkosi, uNkulunkulu waboyise, kahambanga ngendlela yeNkosi.
Ya rabu da Ubangiji Allah na kakanninsa, bai kuwa yi tafiya a hanyar Ubangiji ba.
23 Izinceku zikaAmoni zasezimenzela ugobe, zabulala inkosi endlini yayo.
Fadawan Amon suka ƙulla maƙarƙashiya suka kashe shi a cikin fadarsa.
24 Kodwa abantu belizwe babatshaya bonke labo ababenzele inkosi uAmoni ugobe; abantu belizwe basebebeka uJosiya indodana yakhe ukuba yinkosi esikhundleni sakhe.
Sai mutanen ƙasar suka kashe duk waɗanda suka ƙulla wa Sarki Amon maƙarƙashiya, sa’an nan suka naɗa ɗansa sarki a maimakonsa.
25 Ezinye-ke zezindaba zikaAmoni azenzayo kazibhalwanga yini egwalweni lwemilando yamakhosi akoJuda?
Game da sauran ayyukan mulkin Amon, da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
26 Wasengcwatshelwa engcwabeni lakhe esivandeni sikaUza. UJosiya indodana yakhe wasesiba yinkosi esikhundleni sakhe.
Aka binne shi a kabarinsa a lambun Uzza. Yosiya ɗansa kuma ya gāje shi.

< 2 Amakhosi 21 >