< 1 USamuyeli 28 >
1 Kwasekusithi ngalezonsuku amaFilisti abuthanisela impi amabutho awo ukuze alwe loIsrayeli. UAkishi wasesithi kuDavida: Yazi lokwazi ukuthi uzaphuma impi lami, wena labantu bakho.
Filistiyawa suka tattara sojojinsu domin su yaƙi Isra’ila. Akish ya ce wa Dawuda, “Sai ka sani fa, kai da mutanenka za ku tafi tare da ni da sojojina.”
2 UDavida wasesithi kuAkishi: Sibili, wena uzakwazi ukuthi inceku yakho ingenzani. UAkishi wasesithi kuDavida: Ngakho, ngizakubeka ube ngumlindi wekhanda lami zonke izinsuku.
Dawuda ya ce, “Kai da kanka za ka ga abin da bawanka zai yi.” Akish ya ce, “Da kyau, zan sa ka zama mai kāre ni.”
3 USamuweli wayesefile, loIsrayeli wonke wayemlilele, bamngcwabela eRama, ngitsho emzini wakibo. USawuli wayebasusile-ke elizweni abalamadlozi labalumbayo.
Sama’ila dai ya riga ya rasu, dukan Isra’ila suka yi makokinsa suka binne shi a garinsa a Rama. Shawulu kuma ya kori duk masu duba da masu maitanci daga ƙasar.
4 AmaFilisti asebuthana afika amisa inkamba eShunemi. USawuli wasebuthanisa uIsrayeli wonke, bamisa inkamba eGilibowa.
Filistiyawa suka tattaru suka yi sansani a Shunem. Shawulu ya tattara dukan Isra’ila suka yi sansani a Gilbowa.
5 Lapho uSawuli ebona inkamba yamaFilisti, wesaba, lenhliziyo yakhe yathuthumela kakhulu.
Da Shawulu ya ga sojojin Filistiyawa sai ya ji tsoro, ya firgita ƙwarai.
6 Lapho uSawuli ebuza eNkosini, iNkosi kayimphendulanga langamaphupho langeUrimi langabaprofethi.
Ya nemi nufin Ubangiji amma bai sami amsa daga wurin Ubangiji ko ta wurin mafarki, ko ta wurin Urim, ko ta wurin annabawa ba.
7 USawuli wasesithi ezincekwini zakhe: Ngidingelani owesifazana oledlozi ukuze ngiye kuye, ngibuze kuye. Inceku zakhe zasezisithi kuye: Khangela, kulowesifazana oledlozi eEndori.
Shawulu ya ce wa fadawansa, “Ku nemo mini wata mace mai duba domin in tafi wurinta in yi tambaya.” Suka ce, “Akwai guda a En Dor.”
8 USawuli wasezifihla isimo, wagqoka ezinye izigqoko, wahamba, yena lamadoda amabili laye; basebefika kowesifazana ebusuku. Wathi: Akungivumisele ngedlozi, ungenyusele engizamutsho kuwe.
Sai Shawulu ya sa waɗansu tufafi ya ɓad da kama, shi da waɗansu mutum biyu suka tafi wurin matar da dare, ya ce mata, “Ki yi mini duba ta hanyar sihiri, ki hawar mini duk wanda zan faɗa miki.”
9 Kodwa owesifazana wathi kuye: Khangela, wena uyazi ukuthi uSawuli wenzeni, ukuthi ubaqumile elizweni abalamadlozi labalumbayo. Pho, uwuthiyelani umphefumulo wami ukungibulala?
Amma matar ta ce masa, “Tabbatacce ka dai san abin da Shawulu ya yi, ya karkashe masu duba da masu maitanci a ƙasar. Me ya sa kake sa mini tarko, don ka sa a kashe ni?”
10 Kodwa uSawuli wafunga kuye ngeNkosi, esithi: Kuphila kukaJehova, isijeziso kasiyikuza kuwe ngaloludaba.
Shawulu ya rantse mata da Ubangiji. Ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, ba za a hukunta ki a kan wannan ba.”
11 Owesifazana wasesithi: Ngikwenyusele bani? Wasesithi: Ngenyusela uSamuweli.
Sai matar ta ce, “Wa kake so in hauro maka?” Sai ya ce, “Ki hauro mini da Sama’ila.”
12 Lapho owesifazana ebona uSamuweli, wakhala ngelizwi elikhulu; owesifazana wasekhuluma kuSawuli esithi: Ungikhohliseleni? Ngoba unguSawuli.
Da matar ta ga Sama’ila sai ta yi ihu da ƙarfi ta ce wa Shawulu, “Me ya sa ka ruɗe ni? Kai ne Shawulu!”
13 Inkosi yasisithi kuye: Ungesabi; kodwa ubonani? Owesifazana wasesithi kuSawuli: Ngibona onkulunkulu besenyuka emhlabathini.
Sai sarki ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Me kika gani?” Matar ta ce, “Na ga wani kurwa tana fitowa daga ƙasa.”
14 Wasesithi kuye: Sinjani isimo sakhe? Wasesithi: Kwenyuka ixhegu elembethe isembatho. Lapho uSawuli esesazi ukuthi nguSamuweli, wakhothama ngobuso emhlabathini, wakhonza.
Ya ce, “Yaya kamanninsa yake?” Ta ce, “Wani tsoho sanye da taguwa ne yake haurawa.” Shawulu ya gane cewa Sama’ila ne, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
15 USamuweli wasesithi kuSawuli: Ungikhathazeleni ngokungenyusa? USawuli wasephendula wathi: Ngibandezelekile kakhulu, ngoba amaFilisti alwa lami, loNkulunkulu usukile kimi, kasangiphenduli, langesandla sabaprofethi langamaphupho. Ngakho ngikubizile ukuthi ungazise ukuthi ngenzeni.
Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Don me ka dame ni, ta wurin hauro da ni?” Shawulu ya ce, “Ina cikin babban damuwa ce, Filistiyawa sun fāɗa mini, Allah kuma ya juya mini baya. Bai amsa mini, ko ta mafarki, ko kuma ta annabawa ba, saboda haka na kira ka don ka gaya mini abin yi.”
16 USamuweli wasesithi: Pho, ubuzelani kimi, lokhu iNkosi isisukile kuwe, yaba yisitha sakho?
Sama’ila ya ce, “Don me kake tambayata bayan Ubangiji ya rabu da kai? Ya zama maƙiyinka?
17 INkosi isizenzele njengokukhuluma kwayo ngesandla sami; iNkosi isidabule umbuso usuka esandleni sakho, yawunika umakhelwane wakho, uDavida.
Ubangiji ya cika abin da ya yi magana ta wurina. Ubangiji ya fizge mulki daga hannunka, ya ba maƙwabcinka Dawuda.
18 Njengoba ungalilalelanga ilizwi leNkosi, futhi ungenzanga ukuvutha kolaka lwayo kumaAmaleki, ngakho iNkosi yenzile linto kuwe lamuhla.
Gama ba ka yi biyayya ga Ubangiji ba, ba ka zartar da hukuncinsa mai zafi a kan Amalekawa ba. Saboda haka Ubangiji ya yi maka haka yau.
19 Futhi iNkosi izanikela uIsrayeli laye kanye lawe esandleni samaFilisti; kusasa-ke wena lamadodana akho lizakuba lami. Lenkamba yakoIsrayeli iNkosi izayinikela esandleni samaFilisti.
Ubangiji zai ba da Isra’ila da kuma kai ga Filistiyawa, gobe kuwa da kai da’ya’yanka za ku kasance tare da ni. Ubangiji kuma zai ba da sojojin Isra’ila a hannun Filistiyawa.”
20 USawuli wasehle edilikela emhlabathini, ngokuphelela kobude bakhe, wesaba kakhulu ngenxa yamazwi kaSamuweli, njalo kwakungelamandla kuye, ngoba wayengadlanga kudla usuku lonke lobusuku bonke.
Da jin maganar Sama’ila sai Shawulu ya faɗi ƙasa warwas. Tsoro ya kama shi ƙwarai. Ba shi kuma da ƙarfi domin bai ci kome ba dukan yini da kuma dukan dare.
21 Owesifazana wasesiza kuSawuli, wabona ukuthi wethukile kakhulu, wathi kuye: Khangela, incekukazi yakho ililalele ilizwi lakho, ngifakile umphefumulo wami esandleni sami, ngalalela amazwi owakhulume kimi.
Da matar ta zo wurin Shawulu, ta ga shi a firgice, sai ta ce masa, “Duba baranyarka ta yi maka biyayya ta yi kasai da ranta, ta yi abin da ka ce ta yi.
22 Ngakho-ke lawe akulalele ilizwi lencekukazi yakho, ngifake phambi kwakho ucezwana lwesinkwa ukuze udle, ukuze amandla abe kuwe nxa uhamba indlela yakho.
To, kai ma ka kasa kunne ga baranyarka, zan ba ka abinci ka ci don ka sami ƙarfin tafiya.”
23 Kodwa wala wathi: Kangiyikudla. Kodwa inceku zakhe kanye lowesifazana bamcindezela; waselalela ilizwi labo. Wasesukuma emhlabathini, wahlala embhedeni.
Sai ya ƙi. Ya ce, “Ba zan ci abinci ba.” Sai da bayinsa da matar suka roƙe shi, sa’an nan ya ji maganarsu, ya tashi daga ƙasa, ya zauna a bakin gado.
24 Njalo owesifazana wayelethole elinonileyo endlini; waphangisa walihlaba; wathatha impuphu, wayixova, wabhaka isinkwa esingelamvubelo ngayo;
Matar kuwa tana da maraƙin da take kiwo a gida, sai ta ɗauke shi nan da nan ta yanka. Ta ɗauki garin fulawa ta kwaɓa, ta yi waina marar yisti.
25 wasisondeza phambi kukaSawuli laphambi kwenceku zakhe; badla. Basukuma bahamba ngalobobusuku.
Sai ta kawo wa Shawulu da bayinsa suka kuwa ci. A daren nan suka tashi suka tafi.