< 1 UPhetro 2 >
1 Ngakho lahlani ububi bonke lobuqili bonke lokuzenzisa lomhawu lokuhleba konke,
Saboda haka, ku rabu da kowace ƙeta da dukan ruɗu, munafunci, kishi, da kuma kowace irin ɓata suna.
2 njengezingane ezisanda ukuzalwa, fisani uchago olungaqungwanga lwelizwi, ukuze likhuliswe ngalo,
Kamar sababbin jarirai, ku yi marmarin madara zalla ta ruhaniya, domin ta wurinta za ku yi girma cikin cetonku,
3 uba-ke selinambithile ukuthi iNkosi ilomusa.
yanzu da kuka ɗanɗana alherin Ubangiji.
4 Elizayo kuyo, ilitshe eliphilayo, elaliwa isibili ngabantu, kodwa kuNkulunkulu likhethiwe, liligugu,
Da kuka zo gare shi, rayayyen Dutse, da mutane suka ƙi amma Allah ya zaɓa, kuma mai daraja a gare shi
5 lani njengamatshe aphilayo lakhiwe indlu yokomoya, ubupristi obungcwele, ukuze linikele imihlatshelo yokomoya eyemukelekayo kuNkulunkulu ngoJesu Kristu.
ku ma, a matsayinku na duwatsu masu rai, ana gina ku ga zama gidan ruhaniya don ku zama tsattsarkar ƙungiyar firistoci, kuna miƙa hadayun ruhaniya, abin karɓa ga Allah ta wurin Yesu Kiristi.
6 Ngakho kukhona lembhalweni ukuthi: Khangela ngiyabeka eSiyoni ilitshe lengonsi, elikhethiweyo eliligugu; lokholwa kuye kasoze ayangeke.
Gama a cikin Nassi an ce, “Ga shi, na kafa dutse a Sihiyona, zaɓaɓɓen dutse na kusurwar gini mai daraja, wanda kuma ya dogara gare shi ba zai taɓa kunyata ba.”
7 Ngakho kini elikholwayo uligugu; kodwa kwabangalaleliyo, ilitshe abakhi abalalayo, leli selibe yinhloko yengonsi,
A gare ku da kuka gaskata, wannan dutse mai daraja ne. Amma ga waɗanda ba su gaskata ba, “Dutsen da magina suka ƙi ya zama dutsen kusurwar gini,
8 lelitshe lokukhubekisa, ledwala lokuwisa; abakhubeka elizwini, bengalaleli; okuyikho labo ababekumiselwe;
kuma, “Dutse ne da yake sa mutane tuntuɓe kuma fā ne da yake sa su fāɗi.” Sun yi tuntuɓe domin sun ƙi su yi biyayya da saƙon, wanda kuma yake abin da aka ƙaddara musu.
9 kodwa lina liluhlanga olukhethiweyo, ubupristi bobukhosi, isizwe esingcwele, abantu abatholiweyo, ukuze litshumayele jikelele ukulunga kwalowo owalibiza livela emnyameni laya ekukhanyeni kwakhe okumangalisayo;
Amma ku zaɓaɓɓu ne, ƙungiyar firistocin babban Sarki, al’umma mai tsarki, jama’a mallakar Allah, domin ku shaida yabon shi wanda ya kira ku daga cikin duhu zuwa haskensa mai banmamaki.
10 elalikade lingeyisibo abantu, kodwa khathesi lingabantu bakaNkulunkulu; elalingahawukelwanga, kodwa khathesi selihawukelwe.
Dā ku ba mutane ba ne, amma yanzu ku mutanen Allah ne; Dā ba ku karɓi jinƙai ba, amma yanzu kun karɓi jinƙai.
11 Bathandekayo, ngiyalincenga njengabemzini lezihambi ukuthi lizithinte enkanukweni zenyama, ezilwa lomphefumulo;
Abokaina ƙaunatattu, ina roƙonku, a matsayin bare da kuma baƙi a duniya, ku rabu da sha’awace-sha’awacen zunubin da suke yaƙi da ranku.
12 lilokuhamba okuhle phakathi kwabezizwe, ukuze kuthi, ekulihlebeni njengabenzi bobubi, ezenzweni ezinhle abazibonileyo bangadumisa uNkulunkulu osukwini lokuhanjelwa.
Ku yi irin rayuwa mai kyau a cikin masu bautar gumaka, yadda ko da sun zarge ku da yin laifi, za su iya ganin ayyukanku nagari, su ɗaukaka Allah a ranar da zai ziyarce mu.
13 Ngakho zehliseleni ngaphansi kwaso sonke isimiso sabantu ngenxa yeNkosi; loba kuyinkosi, njengebusayo;
Saboda Ubangiji, ku yi biyayya ga kowace hukumar da aka kafa cikin mutane, ko ga sarki, a matsayi wanda ya fi iko,
14 loba kubabusi, njengabathunywe yiyo ekujezisweni kwabenzi bobubi, kodwa kube lodumo lwabenzi bokuhle.
ko ga gwamnoni, waɗanda ya aika domin su hukunta masu laifi su kuma yabi masu aikata abin da yake daidai.
15 Ngoba injalo intando kaNkulunkulu, ukuthi ngokwenza okuhle lifake isayeke emlonyeni wokungazi kwabantu abayizithutha;
Gama nufin Allah ne cewa ta wurin yin nagarta za ku toshe jahilcin marasa azanci.
16 njengabakhululekileyo, kodwa lingabi lenkululeko njengesigubuzelo sobubi, kodwa njengezigqili zikaNkulunkulu.
Ku yi rayuwa kamar mutanen da aka’yantar, sai dai kada ku yi amfani da’yancinku a matsayin hujjar aikata mugunta; ku yi rayuwa kamar bayin Allah.
17 Hloniphani bonke. Thandani ubuzalwane. Mesabeni uNkulunkulu. Hloniphani inkosi.
Ku nuna ladabin da ya dace ga kowa. Ku ƙaunaci’yan’uwantakar masu bi, ku ji tsoron Allah, ku girmama sarki.
18 Zinceku, zehliseleni ngaphansi kwamakhosi ngokwesaba konke, kungeyisikho kulawo alungileyo lamnene kuphela, kodwa lakulawo angaqondanga.
Bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku da matuƙar ladabi, ba kawai ga waɗanda suke da kirki da masu sauƙinkai ba, amma har ga masu zafin rai ma.
19 Ngoba lokhu kungumusa, uba umuntu ethwala izinhlupheko ngenxa yesazela kuNkulunkulu, ehlupheka ngokungafanelanga.
Gama abin yabo ne in mutum ya yi haƙuri cikin zafin wahalar rashin adalci saboda yana sane da Allah.
20 Ngoba kulenzuzo bani, uba lisona beselitshaywa libekezela? Kodwa uba lisenza okuhle njalo lihlupheke libekezela, lokhu kungumusa kuNkulunkulu.
Amma ina abin taƙama in kuka sha duka saboda kun yi laifi kuka kuma jimre? Sai dai in kuka sha wahala saboda yin nagari kuka kuma jimre, abin yabo ne a gaban Allah.
21 Ngoba labizelwa lokho, ngoba uKristu laye wasihluphekela, esitshiyela isibonelo, ukuze lilandele izinyathelo zakhe;
Ga wannan ne aka kira ku, domin Kiristi ya sha wahala dominku, ya bar muku gurbin da ya kamata ku bi.
22 ongenzanga isono, lenkohliso kayificwanga emlonyeni wakhe;
“Bai taɓa yin laifi ba sam, ba a kuma sami ƙarya a bakinsa ba.”
23 owathi ethukwa kazaphindisela ngokuthuka, ehlupheka kazasongela, kodwa wazinikela kulowo owahlulela ngokulunga;
Sa’ad da suka zazzage shi, bai rama ba; sa’ad da ya sha wahala, bai yi barazana ba. A maimakon haka, ya miƙa kansa ga wanda yake shari’ar adalci.
24 yena ngokwakhe owathwala izono zethu emzimbeni wakhe esihlahleni, ukuze kuthi, sesifile esonweni, siphile ekulungeni; okungemivimvinya yakhe lisilisiwe.
Shi kansa ya ɗauki zunubanmu a jikinsa a kan itace, domin mu mutu ga zunubai mu kuma rayu ga adalci; ta wurin raunukansa ne kuka sami warkarwa.
25 Ngoba lalinjengezimvu ezilahlekayo; kodwa khathesi selibuyele kuMelusi loMbonisi wemiphefumulo yenu.
Gama dā kuna kama da tumakin da suka ɓace, amma yanzu kun dawo ga Makiyayi da kuma Mai lura da rayukanku.