< 1 Amakhosi 2 >

1 Insuku zikaDavida zokuthi afe zasezisondela, waselaya uSolomoni indodana yakhe esithi:
Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
2 Sengihamba indlela yomhlaba wonke. Ngakho qina, ube yindoda,
“Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
3 ugcine imfanelo yeNkosi uNkulunkulu wakho, ukuhamba ngezindlela zayo, ukugcina izimiso zayo, imithetho yayo, lezahlulelo zayo, lobufakazi bayo, njengokubhaliweyo emlayweni kaMozisi, ukuze uphumelele kukho konke okwenzayo, laloba ngaphi lapho ophendukela khona,
ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
4 ukuze iNkosi iqinise ilizwi layo eyalikhuluma mayelana lami isithi: Uba amadodana akho eqaphelisa indlela yawo, ukuhamba ngobuqotho phambi kwami ngenhliziyo yonke yawo langomphefumulo wonke wawo, (isithi) kakuyikusweleka kuwe indoda esihlalweni sobukhosi sikaIsrayeli.
Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
5 Futhi-ke wena uyakwazi ukuthi uJowabi indodana kaZeruya wenzani kimi, ukuthi wenzani kuzinduna ezimbili zamabutho akoIsrayeli, kuAbhineri indodana kaNeri, lakuAmasa indodana kaJetheri, owababulala wachitha igazi lempi ekuthuleni, wafaka igazi lempi ebhantini lakhe elalisekhalweni lwakhe lemanyathelweni asenyaweni zakhe.
“Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
6 Ngakho yenza njengenhlakanipho yakho, ungayekeli ikhanda lakhe elilezimvu lehlele engcwabeni ngokuthula. (Sheol h7585)
Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol h7585)
7 Kodwa kumadodana kaBarizilayi umGileyadi wenze umusa, njalo kawabe phakathi kwabadla etafuleni lakho, ngoba ngokunjalo asondela kimi ekubalekeleni kwami ubuso bukaAbisalomu umfowenu.
“Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
8 Futhi khangela, kukhona kuwe uShimeyi indodana kaGera umBhenjamini weBahurimi, owangithuka ngesethuko esibuhlungu mhla ngisiya eMahanayimi; kodwa wehla ukungihlangabeza eJordani, ngasengifunga kuye ngeNkosi ngathi: Kangiyikukubulala ngenkemba.
“Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
9 Ngakho-ke ungamyekeli abe ngongelacala, ngoba ungumuntu ohlakaniphileyo, ngoba uyakwazi ozakwenza kuye, njalo uzakwehlisela ikhanda lakhe eliyimpunga lilegazi engcwabeni. (Sheol h7585)
Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol h7585)
10 UDavida waselala laboyise, wangcwatshelwa emzini kaDavida.
Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
11 Njalo insuku uDavida abusa ngazo phezu kukaIsrayeli zaziyiminyaka engamatshumi amane; eHebroni wabusa iminyaka eyisikhombisa, leJerusalema wabusa iminyaka engamatshumi amathathu lantathu.
Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
12 USolomoni wasehlala esihlalweni sobukhosi sikaDavida uyise, lombuso wakhe waqiniswa kakhulu.
Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
13 UAdonija indodana kaHagithi wasesiza kuBathisheba unina kaSolomoni; wasesithi: Ukuza kwakho kuyikuthula yini? Wasesithi: Ukuthula.
To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
14 Wathi: Ngilelizwi kuwe. Wasesithi: Khuluma.
Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
15 Wasesithi: Wena uyakwazi ukuthi umbuso wawungowami, lokuthi uIsrayeli wonke babebeke ubuso babo kimi ukuthi ngizabusa; kodwa umbuso waphendulwa, waba ngowomfowethu, ngoba waba ngowakhe uvela eNkosini.
Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
16 Khathesi-ke, ngicela isicelo esisodwa kuwe, ungafulathelisi ubuso bami. Wasesithi kuye: Khuluma.
Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
17 Wasesithi: Ake ukhulume loSolomoni inkosi (ngoba kayikufulathelisa ubuso bakho) ukuthi anginike uAbishagi umShunami abe ngumkami.
Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
18 UBathisheba wasesithi: Kulungile; mina ngizakukhulumela enkosini.
Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
19 Ngakho uBathisheba wasesiya enkosini uSolomoni ukukhulumela uAdonija kuyo. Inkosi yasisukuma ukumhlangabeza, yakhothama kuye, yahlala esihlalweni sayo sobukhosi, yathi kubekelwe unina wenkosi isihlalo sobukhosi; wasehlala ngakwesokunene sayo.
Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
20 Wasesithi: Ngicela isicelo esisodwa esincinyane kuwe, ungafulathelisi ubuso bami. Inkosi yasisithi kuye: Cela, mama, ngoba kangiyikufulathelisa ubuso bakho.
Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
21 Wasesithi: UAbishagi umShunami kanikwe uAdonija umfowenu abe ngumkakhe.
Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
22 Inkosi uSolomoni yasiphendula yathi kunina: Usumcelelelani uAdonija uAbishagi umShunami? Umcelele lombuso, ngoba ungumfowethu omdala kulami, yebo yena loAbhiyatha umpristi loJowabi indodana kaZeruya.
Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
23 Inkosi uSolomoni yasifunga ngeNkosi isithi: Kenze njalo uNkulunkulu kimi lokunjalo engezelele, uba uAdonija engakhulumanga lelilizwi emelene lempilo yakhe.
Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
24 Ngakho-ke, kuphila kukaJehova ongimisileyo wangibeka esihlalweni sobukhosi sikaDavida ubaba, wangenzela indlu njengokukhuluma kwakhe, isibili lamuhla uAdonija uzabulawa.
Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
25 Inkosi uSolomoni yasithuma ngesandla sikaBhenaya indodana kaJehoyada, owamsukelayo, wasesifa.
Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
26 LakuAbhiyatha umpristi inkosi yathi: Yana eAnathothi emasimini akho, ngoba ungumuntu wokufa; kodwa lamuhla kangiyikukubulala ngoba wawuthwala umtshokotsho weNkosi uJehova phambi kukaDavida ubaba, langoba wahlupheka kukho konke ubaba ahlupheka ngakho.
Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
27 Ngakho uSolomoni wamxotsha uAbhiyatha ekubeni ngumpristi weNkosi, ukugcwalisa ilizwi leNkosi eyalikhuluma mayelana lendlu kaEli eShilo.
Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
28 Kwathi umbiko ufika kuJowabi, ngoba uJowabi wayephenduke walandela uAdonija lanxa wayengaphendukanga walandela uAbisalomu, uJowabi wabalekela ethenteni leNkosi, wabamba impondo zelathi.
Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
29 Kwasekubikelwa inkosi uSolomoni ukuthi uJowabi usebalekele ethenteni leNkosi, khangela-ke, useceleni kwelathi. USolomoni wasethuma uBhenaya indodana kaJehoyada esithi: Hamba umsukele.
Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
30 Ngakho uBhenaya waya ethenteni leNkosi, wathi kuye: Itsho njalo inkosi: Phuma! Kodwa wathi: Hatshi, kodwa ngizafela lapha. UBhenaya wasebuyisela ilizwi enkosini, esithi: Utsho njalo uJowabi, ungiphendule njalo.
Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
31 Inkosi yasisithi kuye: Yenza njengokutsho kwakhe, umsukele, umngcwabe; ukuze ususe kimi lendlini kababa igazi elingelacala uJowabi alichithayo.
Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
32 Njalo iNkosi izabuyisela igazi lakhe ekhanda lakhe, owasukela amadoda amabili ayelungile engcono kulaye, wawabulala ngenkemba, ubaba uDavida engazi: UAbhineri indodana kaNeri induna yebutho lakoIsrayeli, loAmasa indodana kaJetheri induna yebutho lakoJuda.
Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
33 Ngakho igazi labo lizabuyela ekhanda likaJowabi lekhanda lenzalo yakhe kuze kube nininini; kodwa kuDavida lenzalweni yakhe, lendlini yakhe, lembusweni wakhe, kuzakuba lokuthula kuze kube nininini okuvela eNkosini.
Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
34 UBhenaya indodana kaJehoyada wasesenyuka, wamsukela wambulala; wasengcwatshelwa endlini yakhe enkangala.
Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
35 Inkosi yasibeka uBhenaya indodana kaJehoyada esikhundleni sakhe phezu kwebutho, loZadoki umpristi inkosi yambeka esikhundleni sikaAbhiyatha.
Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
36 Inkosi yasithuma yabiza uShimeyi, yathi kuye: Zakhele indlu eJerusalema, uhlale khona, ungaphumi lapho uye ngaphi langaphi.
Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
37 Ngoba kuzakuthi mhla uphumayo, uchaphe isifula iKidroni, yazi lokwazi ukuthi uzakufa lokufa; igazi lakho lizakuba phezu kwekhanda lakho.
Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
38 UShimeyi wasesithi enkosini: Lelolizwi lihle; njengokutsho kwenkosi yami, inkosi, inceku yakho izakwenza njalo. UShimeyi wasehlala eJerusalema insuku ezinengi.
Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
39 Kwasekusithi ekupheleni kweminyaka emithathu inceku ezimbili zikaShimeyi zabalekela kuAkishi indodana kaMahaka inkosi yeGathi. Basebebikela uShimeyi besithi: Khangela, inceku zakho ziseGathi.
Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
40 Wasesukuma uShimeyi, wabophela isihlalo kubabhemi wakhe, waya eGathi kuAkishi ukudinga inceku zakhe; uShimeyi wahamba waletha inceku zakhe zivela eGathi.
Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
41 Kwasekubikelwa uSolomoni ukuthi uShimeyi wayesukile eJerusalema waya eGathi, njalo wabuyela.
Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
42 Inkosi yasithuma yabiza uShimeyi yathi kuye: Kangikufungisanga yini ngeNkosi, ngafakaza kuwe ngathi: Mhla uphumayo ukuya ngaphi langaphi yazi lokwazi ukuthi uzakufa lokufa? Wasusithi kimi: Lihle ilizwi engilizwileyo.
Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
43 Pho, kungani ungasigcinanga isifungo seNkosi lomlayo engakulaya ngawo?
To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
44 Inkosi yasisithi kuShimeyi: Wena uyazi bonke ububi inhliziyo yakho ebaziyo owabenza kuDavida ubaba; ngakho iNkosi izabuyisela ububi bakho phezu kwekhanda lakho.
Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
45 Kodwa inkosi uSolomoni ibusisiwe, lesihlalo sobukhosi sikaDavida sizaqiniswa phambi kweNkosi kuze kube nininini.
Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
46 Ngakho inkosi yalaya uBhenaya indodana kaJehoyada, owaphuma wamsukela waze wafa. Ngakho umbuso waqiniswa esandleni sikaSolomoni.
Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.

< 1 Amakhosi 2 >