< 1 Amakhosi 17 >
1 UElija umTishibi wabahlali beGileyadi wasesithi kuAhabi: Kuphila kukaJehova, uNkulunkulu kaIsrayeli, engimi phambi kwakhe, kakuyikuba khona lamazolo lezulu kuliminyaka, kuphela njengokwelizwi lami.
To, Iliya mutumin Tishbe, daga Tishbe a Gileyad, ya ce wa Ahab, “Muddin Ubangiji, Allah na Isra’ila wanda nake bauta wa yana a raye, ba za a yi raɓa ko ruwan sama a’yan shekaru masu zuwa ba, sai ko na faɗa haka.”
2 Ilizwi leNkosi laselifika kuye lisithi:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya, ta ce,
3 Suka lapha, wena uphendukele empumalanga, uzicatshise esifuleni iKerithi, esiphambi kweJordani.
“Ka bar nan, ka nufi wajajen gabas, ka ɓuya a Rafin Kerit, gabas da Urdun.
4 Kuzakuthi-ke unathe esifuleni; sengilaye amawabayi ukuthi akondle khona.
Za ka sha daga rafin, zan kuma umarci hankaki su ciyar da kai a can.”
5 Wasehamba wenza njengokwelizwi leNkosi, ngoba wayahlala esifuleni iKerithi esiphambi kweJordani.
Saboda haka sai Iliya ya yi abin da Ubangiji ya faɗa masa. Ya tafi Rafin Kerit, gabas da Urdun, ya zauna a can.
6 Amawabayi asemlethela isinkwa lenyama ekuseni, lesinkwa lenyama ntambama; wanatha esifuleni.
Hankaki suka riƙa kawo masa abinci da nama, safe da yamma, ya kuma sha daga rafin.
7 Kwasekusithi emva kwesikhathi isifula satsha, ngoba kwakungelazulu elizweni.
Ana nan sai rafin ya bushe saboda ba a yi ruwan sama a ƙasar ba.
8 Ilizwi leNkosi laselifika kuye lisithi:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya cewa,
9 Sukuma uye eZarefathi engeyeSidoni, uhlale khona. Khangela, ngilayile owesifazana ongumfelokazi khona ukuthi akondle.
“Je ka, nan take, zuwa Zarefat na Sidon, ka zauna a can. Na umarci wata gwauruwa a can tă ciyar da kai.”
10 Wasukuma-ke waya eZarefathi. Lapho efika esangweni lomuzi, khangela, owesifazana ongumfelokazi wayelapho etheza inkuni; wasembiza wathi: Ake ungikhele amanzi amalutshwana ngenkezo ukuze nginathe.
Saboda haka sai ya tafi Zarefat. Sa’ad da ya isa ƙofar gari, sai ga wata gwauruwa tana tattara’yan itace. Sai ya kira ta, ya ce, “Ki kawo mini ɗan ruwa a tulu don in sha.”
11 Kwathi esahamba ukuyawathatha, wambiza wathi: Ake ungiphathele ucezu lwesinkwa esandleni sakho.
Da ta kama hanya za tă tafi tă kawo, sai ya sāke kiranta ya ce, “Ina roƙonki, ki kuma kawo mini ɗan abinci.”
12 Wasesithi: Kuphila kukaJehova uNkulunkulu wakho, kangilaqebelengwana, kuphela impuphu egcwala isandla embizeni lamafutha ayingcosana esiphisweni; khangela-ke ngitheza izinkuni ezimbili ukuze ngingene ngizilungisele khona mina lendodana yami, ukuze sidle sife.
Sai ta ce masa, “Na rantse da Ubangiji Allahnka, ba ni da wani abinci, sai dai ɗan gari hannu guda a tulu, da kuma ɗan mai a kwalaba. Ina tattara’yan itacen nan ne don in kai gida in yi abinci wa kaina da ɗana, don mu ci, mu mutu.”
13 UElija wasesithi kuye: Ungesabi; hamba wenze njengokwelizwi lakho, kodwa ngenzela kuqala iqebelengwana elincinyane ngakho, ulilethe lapha kimi, ngemva kwalokho-ke wenzele wena lendodana yakho.
Iliya ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Ki tafi gida, ki yi yadda kika ce. Amma da farko ki yi mini’yar wainar burodi daga abin da kike da shi ki kawo mini, sa’an nan ki yi wani abu wa kanki da kuma ɗanki.
14 Ngoba itsho njalo iNkosi uNkulunkulu wakoIsrayeli: Imbiza yempuphu kayiyikuphela, lesiphiso samafutha kasiyikuswela, kuze kube lusuku iNkosi ezanisa ngalo izulu ebusweni bomhlaba.
Gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Tulun garin ba zai ƙare ba, kwalabar man kuma ba zai bushe ba sai ranar da Ubangiji ya bayar da ruwan sama a ƙasar.’”
15 Wasehamba wenza njengokwelizwi likaElija. Njalo yena kanye laye lendlu yakhe badla okwensuku ezinengi.
Sai ta tafi, ta yi yadda Iliya ya faɗa mata. Saboda haka aka kasance da abinci kowace rana wa Iliya da kuma don macen da iyalinta.
16 Imbiza yempuphu kayiphelanga lesiphiso samafutha kasiswelanga, njengokwelizwi leNkosi eyalikhuluma ngesandla sikaElija.
Gama tulun garin bai ƙare ba, kwalabar man kuma bai bushe ba, kamar yadda Ubangiji ya faɗa wa Iliya.
17 Kwasekusithi emva kwalezizinto, indodana yowesifazana, inkosikazi yendlu, yagula; lomkhuhlane wayo wawulamandla kangangokuthi akwaze kwasala umphefumulo kuyo.
Ana nan sai ɗan matan, wato, gwauruwan nan ya fara ciwo. Ciwon ya ƙara muni, daga ƙarshe sai ya daina numfashi.
18 Wasesithi kuElija: Ngilani lawe, muntu kaNkulunkulu? Uze kimi ukuze kukhumbuleke isono sami lokubulala indodana yami na?
Sai ta ce wa Iliya, “Mutumin Allah, yaya haka? Ka zo ne domin ka nuna wa Allah zunubaina, ka kuma jawo mutuwar ɗana?”
19 Wasesithi kuye: Nginika indodana yakho. Waseyithatha esifubeni sakhe, wayenyusela endlini ephezulu lapho ayehlala khona, wayilalisa embhedeni wakhe.
Iliya ya ce, “Ki miƙa mini ɗanki.” Sai ya ɗauke shi daga hannuwanta, ya kai shi ɗakin sama inda yake zama, ya kwantar da shi a gadonsa.
20 Wasekhala eNkosini wathi: Nkosi Nkulunkulu wami, umehlisele ububi lalo umfelokazi engingenise kwakhe ngokubulala indodana yakhe na?
Sa’an nan ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, don me ka kawo wannan masifa a kan gwauruwan nan? Kai ka ce in zauna tare da ita, ga shi yanzu ɗanta ya mutu.”
21 Wasezelulela phezu komntwana kathathu, wakhala eNkosini wathi: Nkosi Nkulunkulu wami, ake ubuyele umphefumulo walumntwana phakathi kwakhe.
Sai ya kwanta, ya miƙe kansa a kan yaron sau uku, ya kuma yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, ka mai da ran yaron nan!”
22 INkosi yasilizwa ilizwi likaElija, umphefumulo womntwana wasubuyela phakathi kwakhe, wasebuya ephila.
Ubangiji kuwa ya ji kukan Iliya, sai ran yaron ya dawo masa, ya kuma rayu.
23 UElija wasemthatha umntwana, wamehlisa esuka endlini ephezulu waya endlini, wamnika unina; uElija wasesithi: Bona, indodana yakho iyaphila.
Iliya ya ɗauki yaron ya sauko da shi daga ɗakin sama zuwa cikin gida. Ya ba da shi ga mahaifiyarsa, ya ce, “Duba, ɗanki yana da rai!”
24 Owesifazana wasesithi kuElija: Khathesi sengisazi lokhu, ukuthi ungumuntu kaNkulunkulu, ukuthi ilizwi leNkosi elisemlonyeni wakho liliqiniso.
Sai matar ta ce wa Iliya, “Yanzu na san cewa kai mutumin Allah ne, Ubangiji kuma yana magana ta wurinka.”