< 1 Amakhosi 11 >
1 Inkosi uSolomoni yayithanda-ke abafazi abanengi bezizweni, kanye lendodakazi kaFaro, amaMowabikazi, amaAmonikazi, amaEdomikazi, amaSidonikazi, amaHethikazi,
Sarki Solomon ya ƙaunaci baƙin mata. Ban da’yar Fir’auna, ya auri Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, Sidoniyawa da Hittiyawa.
2 ababevela ezizweni iNkosi eyayithe ngazo kubantwana bakoIsrayeli: Kaliyikungena kibo, labo kabayikungena kini; isibili bazaphendula inhliziyo yenu ilandele onkulunkulu babo. Bona uSolomoni wabanamathela ngothando.
Sun fito daga al’ummai da Ubangiji ya ce wa Isra’ilawa, “Kada ku yi aurayya da su, domin tabbatacce za su juye zukatanku zuwa ga waɗansu alloli.” Duk da haka Solomon ya manne musu, ya nace, yana ƙaunarsu.
3 Wayelabafazi abangamakhulu ayisikhombisa, amakhosazana, labafazi abancane abangamakhulu amathathu; abafazi bakhe basebephambula inhliziyo yakhe.
Ya auri mata ɗari bakwai, haifaffun gidan sarauta, da kuma ƙwarƙwarai ɗari uku. Matan nan nasa suka karkatar da shi.
4 Ngoba kwathi esikhathini sokuluphala kukaSolomoni, abafazi bakhe baphambulela inhliziyo yakhe ekulandeleni abanye onkulunkulu, lenhliziyo yakhe yayingaphelelanga kuJehova uNkulunkulu wakhe, njengenhliziyo kaDavida uyise.
Yayinda Solomon yake tsufa, matansa suka juye zuciyarsa ga bin waɗansu alloli, zuciyarsa kuwa ba tă bi Ubangiji Allahnsa ɗungum kamar yadda zuciyar Dawuda mahaifinsa ta kasance ba.
5 Ngoba uSolomoni wahamba emva kukaAshitarothi unkulunkulu wamaSidoni lemva kukaMilkomu isinengiso samaAmoni.
Ya bi Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
6 USolomoni wasesenza okubi emehlweni eNkosi, kayilandelanga ngokupheleleyo iNkosi njengoDavida uyise.
Saboda haka Solomon ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji. Bai bi Ubangiji gaba ɗaya kamar yadda Dawuda mahaifinsa ya yi ba.
7 Ngalesosikhathi uSolomoni wakhela uKemoshi isinengiso sakoMowabi indawo ephakemeyo entabeni ephambi kweJerusalema, loMoleki isinengiso sabantwana bakoAmoni.
A kan tudu, gabas da Urushalima, Solomon ya gina masujada a can domin Kemosh, allahn da aka hana na Mowab, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
8 Langokunjalo wabenzela bonke abafazi bakhe bezizweni abatshisa impepha bahlabela onkulunkulu babo.
Ya yi haka domin dukan baƙin matansa, waɗanda suka ƙone turare suka kuma miƙa hadayu ga allolinsu.
9 INkosi yasimthukuthelela uSolomoni, ngoba inhliziyo yakhe yayiphambukile eNkosini, uNkulunkulu kaIsrayeli, eyayibonakele kuye kabili,
Ubangiji ya yi fushi da Solomon domin zuciyarsa ya juye daga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bayyana masa sau biyu.
10 yamlaya mayelana lalinto, ukuthi angalandeli abanye onkulunkulu; kodwa kagcinanga lokho iNkosi eyamlaya khona.
Ko da yake ya hana Solomon bin waɗansu alloli, Solomon bai kiyaye umarnin Ubangiji ba.
11 Ngakho iNkosi yathi kuSolomoni: Ngenxa yokuthi lokhu kwenziwe nguwe, ungagcinanga isivumelwano sami lezimiso zami, engakulaya khona, ngizawudabula lokuwudabula umbuso kuwe, ngiwunike inceku yakho.
Saboda haka Ubangiji ya ce wa Solomon, “Da yake halinka ke nan, ba ka kuma kiyaye alkawarina, da ƙa’idodina da na umarce ka ba, tabbatacce zan yage masarautar daga gare ka, in ba da ita ga ɗaya daga cikin bayinka.
12 Kanti kangiyikukwenza ensukwini zakho ngenxa kaDavida uyihlo; ngizawudabula usuke esandleni sendodana yakho.
Amma saboda Dawuda mahaifinka, ba zan yi haka a zamaninka ba. Zan yage ta daga hannun ɗanka.
13 Loba kunjalo kangiyikudabula wonke umbuso; ngizanika indodana yakho isizwe esisodwa ngenxa kaDavida inceku yami langenxa yeJerusalema engiyikhethileyo.
Amma ba zan yage dukan masarautar daga gare shi ba, zan ba shi kabila ɗaya saboda Dawuda bawana, da kuma saboda Urushalima, wadda na zaɓa.”
14 INkosi yasimvusela uSolomoni isitha, uHadadi umEdoma; wayengowenzalo yenkosi eEdoma.
Sai Ubangiji ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Hadad, mutumin Edom daga gidan sarautar Edom.
15 Ngoba kwathi uDavida eseEdoma, uJowabi induna yebutho wayenyukele ukungcwaba ababuleweyo, watshaya wonke owesilisa eEdoma.
A shekarun baya Dawuda ya ci Edom da yaƙi. Yowab, shugaban sojojinsa ya tafi can domin yă binne Isra’ilawa waɗanda suka mutu a yaƙi. Sa’ad da suke a can, sojojin Isra’ila suka kashe kowane ɗa namiji a Edom.
16 Ngoba uJowabi wahlala lapho inyanga eziyisithupha, loIsrayeli wonke, waze waquma wonke owesilisa eEdoma.
Yowab da dukan Isra’ilawa suka zauna a can, wata shida, sai da suka hallaka dukan mutane a Edom.
17 Kodwa uHadadi wabaleka, yena lamaEdoma athile avela encekwini zikayise kanye laye, ukungena eGibhithe; njalo uHadadi wayengumfanyana.
Amma Hadad yana ɗan yaro a lokaci, wanda ya gudu zuwa Masar tare da shugabannin mutanen Edom waɗanda suka yi wa mahaifinsa hidima.
18 Basebesuka eMidiyani, bafika eParani, bathatha amadoda labo eParani, bafika eGibhithe, kuFaro inkosi yeGibhithe, owamnika indlu, wammisela ukudla, wamnika umhlabathi.
Suka taso daga Midiyan suka tafi Faran. Sa’an nan suka ɗauki mutane daga Faran suka tafi Masar, zuwa wurin Fir’auna wanda ya ba wa Hadad gida da ƙasa, ya kuma tanada masa da abinci.
19 UHadadi wasethola umusa omkhulu emehlweni kaFaro, waze wamendisela udadewabo womkakhe, udadewabo kaTapenesi indlovukazi.
Fir’auna ya ji daɗin Hadad har ya ba shi’yar’uwar matarsa, Sarauniya Tafenes, aure.
20 Udadewabo kaTapenesi wasemzalela uGenubathi indodana yakhe, uTapenesi amlumulela phakathi kwendlu kaFaro; njalo uGenubathi wayesendlini kaFaro phakathi kwabantwana bakaFaro.
’Yar’uwar Tafenes ta haifi masa ɗa wanda ya kira Genubat, wanda Tafenes ta yi renonsa a fadan sarki. A can, Genubat ya yi zama da’ya’yan Fir’auna.
21 Kwathi uHadadi esezwile eseGibhithe ukuthi uDavida ulele laboyise lokuthi uJowabi induna yebutho usefile, uHadadi wathi kuFaro: Ngivumela ngisuke ukuthi ngiye elizweni lakithi.
Yayinda yake a Masar, Hadad ya ji Dawuda ya huta tare da kakanninsa, ya kuma ji cewa Yowab shugaban mayaƙa ya mutu. Sai Hadad ya ce wa Fir’auna, “Bari in tafi, don in koma ƙasata.”
22 UFaro wasesithi kuye: Kodwa usweleni ulami ukuthi, khangela, udinge ukuya elizweni lakini? Wasesithi: Akulalutho, loba kunjalo ngivumela lokungivumela ngihambe.
Fir’auna ya tambaye shi, ya ce, “Me ka rasa a nan da kake so ka koma garinka?” Ya ce, “Ba kome, amma ka dai bar ni in tafi!”
23 UNkulunkulu wasemvusela isitha, uRezoni indodana kaEliyada owayebalekile enkosini yakhe uHadadezeri inkosi yeZoba.
Allah kuwa ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Rezon, ɗan Eliyada, wanda ya gudu daga maigidansa, Hadadezer sarkin Zoba.
24 Wasezibuthela amadoda, waba ngumkhokheli weviyo, lapho uDavida ebabulala; basebesiya eDamaseko, bahlala kuyo, babusa eDamaseko.
Rezon ya tattara mutane kewaye da shi, ya zama kuma shugaban’yan tawaye sa’ad da Dawuda ya hallaka mayaƙan Zoba;’yan tawayen suka tafi Damaskus, inda suka zauna, suka kuma yi mulki.
25 Wasesiba yisitha kuIsrayeli insuku zonke zikaSolomoni, phezu kobubi uHadadi abenzayo; njalo wanengwa nguIsrayeli, wabusa phezu kukaSiriya.
Rezon ya zama babban abokin gāban Isra’ila cikin dukan kwanakin mulkin Solomon. Ya ƙara rikici a kan rikicin Hadad. Rezon ya ƙi mulkin Isra’ila da dukan ransa. Saboda haka Rezon ya yi mulki a Aram ya kuma ƙi jinin Isra’ila.
26 LoJerobhowamu, indodana kaNebati, umEfrayimi weZereda, inceku kaSolomoni, obizo likanina lalinguZeruwa, owesifazana ongumfelokazi, laye waphakamisa isandla emelene lenkosi.
Haka ma Yerobowam, ɗan Nebat, shi ma ya yi wa sarki tawaye. Shi ɗaya ne daga shugabannin Solomon, shi mutumin Efraim ne daga Zereda, mahaifiyarsa kuwa gwauruwa ce, mai suna Zeruwa.
27 Yilolu-ke udaba lokuthi aphakamise isandla emelene lenkosi. USolomoni wakha iMilo, wavala isikhala somuzi kaDavida uyise.
Ga yadda ya tayar wa sarki Solomon. Sarki Solomon ya gina madogaran gini, ya ciccika wurare a katangar birnin Dawuda mahaifinsa da ƙasa.
28 UJerobhowamu wayeliqhawe elilamandla. Kwathi uSolomoni ebona lelijaha ukuthi likhuthele emsebenzini, walibeka phezu kwawo wonke umthwalo wendlu kaJosefa.
To, Yerobowam mutum ne mai fasaha. Sa’ad da Solomon ya ga yadda matashin yake aiki da himma, sai ya sa shi yă lura da dukan aikin gandu na gidan Yusuf.
29 Kwasekusithi ngalesosikhathi lapho uJerobhowamu ephuma eJerusalema, uAhiya umShilo umprofethi wamfica endleleni. Njalo wayezigqokise isigqoko esitsha; bobabili babebodwa egangeni.
Da Yerobowam ya fita Urushalima, sai annabi Ahiya, mutumin Shilo ya tarar da shi a hanya. Lokacin kuwa Ahiya yana saye da sabuwar riga, ba kowa a filin sai su biyu kaɗai.
30 UAhiya wasesibamba isigqoko esitsha esasikuye, wasidabula iziqa ezilitshumi lambili,
Sai Ahiya ya kama sabuwar rigar da yake saye da ita ya yage ta gida goma sha biyu.
31 wathi kuJerobhowamu: Zithathele iziqa ezilitshumi, ngoba itsho njalo iNkosi, uNkulunkulu kaIsrayeli: Khangela, ngizadabula umbuso usuke esandleni sikaSolomoni, ngikunike izizwe ezilitshumi.
Sa’an nan ya ce wa Yerobowam, “Ɗauki gida goma wa kanka, gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce ke nan, ‘Duba, zan yage masarauta daga hannun Solomon in ba ka kabilu goma.
32 Kodwa yena uzakuba lesizwe esisodwa ngenxa yenceku yami uDavida langenxa yeJerusalema, umuzi engiwukhethileyo ezizweni zonke zakoIsrayeli.
Amma saboda bawana Dawuda da kuma birnin Urushalima, wadda na zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila, zai sami kabila guda.
33 Ngenxa yokuthi bangitshiyile, bakhonza uAshitarothi unkulunkulu wamaSidoni, uKemoshi unkulunkulu wamaMowabi, loMilkomu unkulunkulu wabantwana bakoAmoni, kabahambanga ngendlela zami, ukwenza okulungileyo emehlweni ami, lokulondoloza izimiso zami lezahlulelo zami, njengoDavida uyise.
Zan yi wannan domin sun yashe ni, suka kuma yi wa Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Kemosh, allahn Mowabawa, da kuma Molek, allahn Ammonawa sujada, ba su yi tafiya a hanyoyina ba, ba su kuwa yi abin da yake daidai a idanuna ba, ba su kiyaye farillaina da dokokina kamar yadda Dawuda, mahaifin Solomon ya yi ba.
34 Loba kunjalo kangiyikuwususa umbuso wonke esandleni sakhe; kodwa ngizamenza abe ngumbusi zonke izinsuku zempilo yakhe ngenxa kaDavida inceku yami, engamkhethayo, owagcina imilayo yami lezimiso zami.
“‘Amma ba zan ɗauki dukan masarautar daga hannun Solomon ba; na naɗa shi sarki, dukan kwanaki ransa saboda Dawuda bawana, wanda na zaɓa, wanda kuma ya kiyaye umarnai da farillaina.
35 Kodwa ngizawususa umbuso esandleni sendodana yakhe, ngiwunike wena, izizwe ezilitshumi.
Zan ɗauke masarautar daga hannuwan ɗansa ne, in ba ka kabilu goma.
36 Lendodana yakhe ngizayinika isizwe sibe sinye ukuze uDavida inceku yami abe lesibane zonke izinsuku phambi kwami eJerusalema, umuzi engizikhethele wona ukuze ngibeke ibizo lami khona.
Zan ba da ɗaya ga ɗansa don kullum Dawuda bawana yă kasance da fitila a gabana a Urushalima, birnin da na zaɓa in sa Sunana.
37 Wena-ke ngizakuthatha, uzabusa phezu kwakho konke umphefumulo wakho okuloyisayo, ube yinkosi phezu kukaIsrayeli.
Amma fa, ga kai, zan ɗauke ka, za ka kuwa yi mulki bisa dukan abin da zuciyarka take so; za ka zama sarki a bisa Isra’ila.
38 Kuzakuthi-ke, uba ulalela konke engikulaya khona, uhambe ngezindlela zami, wenze okulungileyo emehlweni ami, ukugcina izimiso zami lemilayo yami, njengokwenza kukaDavida inceku yami, ngizakuba lawe, ngikwakhele indlu eqinileyo, njengengayakhela uDavida, ngizakunika uIsrayeli,
In ka aikata dukan abin da na umarce ka, ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi abin da yake daidai a idanuna ta wurin kiyaye farillaina da umarnaina, kamar yadda Dawuda bawana ya yi, zan kasance tare da kai. Zan gina maka masarauta mai dawwama kamar wadda na gina wa Dawuda, zan kuma ba da Isra’ila gare ka.
39 njalo ngihluphe inzalo kaDavida ngenxa yalokhu, kodwa kungabi kokuphela.
Zan ƙasƙantar da zuriyar Dawuda saboda wannan, amma ba har abada ba.’”
40 Ngakho uSolomoni wadinga ukumbulala uJerobhowamu, kodwa uJerobhowamu wasuka wabalekela eGibhithe, kuShishaki inkosi yeGibhithe, wayeseGibhithe waze wafa uSolomoni.
Solomon ya yi ƙoƙari yă kashe Yerobowam, amma Yerobowam ya tsere zuwa Masar, zuwa wurin sarki Shishak, ya zauna a can sai bayan mutuwar Solomon.
41 Ezinye-ke zezindaba zikaSolomoni, lakho konke akwenzayo, lenhlakanipho yakhe, kakubhalwanga yini egwalweni lwendaba zikaSolomoni?
Game da sauran ayyukan mulkin Solomon, da dukan abubuwan da ya yi, da hikimar da ya nuna, an rubuta su a littafin tarihin Solomon.
42 Isikhathi-ke uSolomoni abusa ngaso eJerusalema phezu kukaIsrayeli wonke saba yiminyaka engamatshumi amane.
Solomon ya yi mulki a Urushalima, a bisa dukan Isra’ila, shekaru arba’in.
43 USolomoni waselala laboyise, wangcwatshelwa emzini kaDavida uyise. URehobhowamu indodana yakhe wasesiba yinkosi esikhundleni sakhe.
Sa’an nan ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dawuda mahaifinsa. Sai Rehobowam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.