< Amahubo 8 >
1 Kumqondisi wokuhlabela. Ngendlela yegithithi. Ihubo likaDavida. Oh Thixo, Thixo wethu, ibizo lakho libabazeka kangaka emhlabeni wonke! Uyibekile inkazimulo yakho ngaphezulu emazulwini.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, shugabanmu, sunanka da girma take a cikin dukan duniya! Ka kafa ɗaukakarka bisa sammai.
2 Ukumisile ukudunyiswa yizindebe zabantwana lensane ngenxa yezitha zakho, ukuze uthulise isitha lomphindiseli.
Daga leɓunan yara da jarirai ka kafa yabo domin su sa abokan gābanka da masu ɗaukan fansa su yi shiru.
3 Nxa nginakana ngamazulu akho, umsebenzi weminwe yakho, inyanga lezinkanyezi ozibeke endaweni yazo,
Sa’ad da na dubi sammai, aikin yatsotsinka, wata da taurari waɗanda ka ajiye a wurarensu,
4 uyini umuntu osungaze uzihluphe ngaye na, indodana yomuntu ukuba uyinanze?
wane ne mutum da kake tunawa da shi, ɗan mutum da kake lura da shi?
5 Wamenza waba mncinyazana kulezingilosi, wamethesa umqhele wodumo lobukhosi.
Ka yi shi ƙasa kaɗan da Allah ka yi masa rawani da ɗaukaka da girma.
6 Wamenza umbusi phezu kwemisebenzi yezandla zakho; wabeka zonke izinto ngaphansi kwezinyawo zakhe:
Ka mai da shi mai mulki bisa ayyukan hannuwanka; ka sa kome a ƙarƙashin ƙafafunsa,
7 yonke imihlambi yezimvu leyenkomo lezinyamazana zeganga,
dukan shanu da tumaki, da kuma namun jeji,
8 izinyoni zasemkhathini lenhlanzi zolwandle, konke okuntsheza emanzini olwandle.
tsuntsayen sararin sama da kifin teku, da dukan abin da yake yawo a ƙarƙashin ruwan teku.
9 Oh Thixo, Thixo wethu, ibizo lakho libabazeka kangaka emhlabeni wonke!
Ya Ubangiji, shugabanmu, sunanka da girma take a cikin dukan duniya!