< Amahubo 41 >

1 Kumqondisi wokuhlabela. Ihubo likaDavida. Ubusisiwe lowo onanza abahluphekayo; uThixo uyamkhulula ngezikhathi zokuhlupheka.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
2 UThixo uzamvikela alondoloze impilo yakhe; uzambusisa phakathi kwelizwe akasoze amnikele emandleni ezitha zakhe.
Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
3 UThixo uzamqinisa lanxa elele egula njalo amsilise avuke ekuguleni kwakhe.
Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
4 Ngathi, “Oh Thixo ake ungihawukele; ngisilisa, ngoba ngonile kuwe.”
Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
5 Izitha zami ziyangigcona zithi, “Uzakufa nini licitshe ibizo lakhe?”
Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
6 Nxa omunye wabo efika ezongibona, ukhuluma kuhle angikhohlise, kodwa enhliziyweni yakhe egaya izibozi; athi angaphuma ahambe esekhihliza ebantwini.
Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
7 Bonke abangizondayo banyenyezelana ngami; bangicabangela wonke amanyala besithi,
Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
8 “Usengenwe ngumkhuhlane omubi; kasoze asile avuke futhi.”
“Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
9 Lomngane wami osekhwapheni, ebengimthembile, lowo obesidla lami isinkwa usengihlamukele.
Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
10 Kodwa wena, Oh Thixo ake ungihawukele; ake ungivuse ukuze ngibakhawulise.
Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
11 Ngiyazi ukuthi uyathokoza ngami, ngoba isitha sami kasingehluli.
Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
12 Ubuqotho bami busekelwa nguwe njalo ungimisa phambi kwakho nini lanini.
Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
13 Udumo alube kuye uThixo, uNkulunkulu ka-Israyeli, kusukela nininini kuze kube nininini.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.

< Amahubo 41 >