< Amahubo 35 >
1 ElikaDavida. Xabana labo, Thixo abaxabana lami; lwana labo abalwa lami.
Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
2 Thatha isihlangu lewisa; phakama uzongilamulela.
Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
3 Phakamisa umkhonto lesijula, ukuqondise kwabangihlaselayo. Ngitshela ukuthi, “Ngiyikusindiswa kwakho.”
Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
4 Sengathi labo abazingela impilo yami bangayangiswa bathelwe ngehlazo; sengathi labo abazama ukungidiliza bangabuyiselwa emuva bedumazekile.
Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
5 Sengathi bangaba njengamakhoba emoyeni, ingilosi kaThixo ibe ibadudula ibaxotsha;
Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
6 sengathi indlela yabo ingaba mnyama itshelele, ingilosi kaThixo ibe ibahlezi ezithendeni.
bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
7 Ngoba bangithiya ngamambule abo ngingonanga lutho, baphinda bangembela umgodi kungelasizatho,
Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
8 sengathi bangadilizwa belibele lawomambule abawathiyileyo abahilele, sengathi bangawela kulowomgodi babhidlizwe.
bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
9 Lapho-ke umoya wami uzathokoza kuThixo ujabule ekusindiseni Kwakhe.
Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
10 Mina qobo lwami ngizamemeza ngithi, “Ngubani onjengawe, Oh Thixo? Uyabakhulula abahluphekayo kulabo abalamandla kulabo, abahluphekayo labaswelayo kulabo ababantshontshelayo.”
Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
11 Ofakazi bolunya bayangivelela; bangibuza ngezinto engingazaziyo.
Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
12 Bangiphindisela okuhle ngokubi umphefumulo wami usale usudabukile.
Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
13 Ikanti kwathi bona begula ngembatha amasaka ngazithoba ngazila ukudla. Kwathi lapho imikhuleko yami ingaphendulwa
Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
14 ngaba sesililweni kwangathi ngililela umngane wami loba umfowethu. Ngakhothamisa ikhanda lami ngokudabuka kwangathi ngililela umama.
nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
15 Kodwa ngathi sengikhubekile baqwebana bokha insini; abahlaseli bangihlanganyela ngilibele. Bangichothoza okungapheliyo.
Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
16 Bakloloda ngomona njengabangakholwayo; bangigedlela amazinyo abo.
Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
17 Nkosi, uzakuma ubukele kuze kube nini na? Yenyula impilo yami ekungilimazeni kwabo, impilo yami eligugu kulezizilwane.
Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
18 Ngizakubonga phakathi komhlangano omkhulu; ngikudumise ngiphakathi kwamaxuku abantu.
Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
19 Ungabayekeli abayizitha zami ngingabonelanga lutho, bantele phezu kwami. Ungayekeli labo abangizondayo kungelasizatho, banginyonkoloze ngomona.
Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
20 Kabakhulumi okuqondileyo kodwa babumba amacala amanga, ngalabo abaphila ngokuthula elizweni.
Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
21 Bangikhamisela imilomo bathi, “Hiya belo! Sizibonele ngawethu amehlo la.”
Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
22 Oh Thixo, usukubonile lokhu; ungathuli. Ungabi khatshana kwami, Oh Nkosi.
Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
23 Vuka, uphakame ungilamulele! Ngilwela, Nkulunkulu Thixo wami.
Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
24 Ngigeza ngokulunga Kwakho, Thixo, Nkulunkulu wami; ungabayekeli bantele phezu kwami.
Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
25 Ungabayekeli bacabange bathi, “Ehe, yikho ebesikufuna!” loba bathi, “Sesimginyile.”
Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
26 Sengathi bonke abantela ngokuhlupheka kwami bangathelwa ngehlazo basanganiseke; sengathi bonke abazikhukhumezayo phezu kwami bangembeswa ngokuyangeka langehlazo.
Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
27 Sengathi labo abathokoza ngokugezwa kwami bangahalalisa ngentokozo lenjabulo; sengathi bangatsho kokuphela bathi, “Makaphakanyiswe uThixo othokoza ngokuhlala kuhle kwenceku yakhe.”
Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
28 Ulimi lwami luzakhuluma ngokulunga Kwakho langendumiso Yakho ilanga lonke.
Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.