< Izaga 7 >

1 Ndodana yami, agcine amazwi ami ulondoloze imilayo yami ngaphakathi kwakho.
Ɗana, ka kiyaye kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka.
2 Gcina imilayo yami ukuze uphile; ulinde imfundiso yami njengegugu lakho elikhulu.
Ka kiyaye umarnaina za ka kuwa rayu; ka tsare koyarwata kamar ƙwayar idonka.
3 Ibophele eminweni yakho; uyilobe enhliziyweni yakho.
Ka daure su a yatsotsinka; ka rubuta su a allon zuciyarka.
4 Tshela ukuhlakanipha uthi, “Ungudadewethu wena,” uthi ukuqedisisa kuyisihlobo sakho;
Ka faɗa wa hikima, “Ke’yar’uwata ce,” ka kuma kira fahimi danginka;
5 lezizinto zizakuvikela emfazini oyisifebe, lakumkakho ongelambeko ngamazwi akhe adukisayo.
za su kiyaye ka daga mazinaciya, daga mace marar aminci da kalmominta masu ɗaukan hankali.
6 Ngema ewindini lendlu yami ngalunguza ngesikhala.
A tagar gidana na leƙa ta labule mai rammuka.
7 Ngabona phakathi kwabayizithutha, ngananzelela phakathi kwamajaha ngabona ijaha elingelangqondo.
Sai na gani a cikin marasa azanci, na lura a cikin samari, wani matashi wanda ba shi da hankali.
8 Lalisehla ngomgwaqo liseduze lejiko, liqonda endlini yowesifazane
Yana gangarawa a titi kusa da kusurwarta, yana tafiya a gefen wajen gidanta
9 ntambama sekunqunda amehlo, umnyama wobusuku usujiya.
da magariba, yayinda rana tana fāɗuwa, yayinda duhun dare yana farawa.
10 Khonokho nje kwaqhamuka owesifazane elihlangabeza egqoke okwesifebe ngoba eqophile.
Sai ga mace ta fito don ta sadu da shi, saye da riga kamar karuwa shirye kuma don ta yaudare shi.
11 (Umfazi lowo, ngumuntu womsindo uyisiqholo, inyawo zakhe kazihlali phansi;
(Ba ta jin tsoro, ko kuma kunya, ƙafafunta ba sa zama a gida;
12 khathesi nangu emgwaqweni, njalo nangu enkundleni, utshobatshoba izindawana zonke.)
wani lokaci a titi, wani lokaci a dandali, tana yawo a kowace kusurwa.)
13 Wafika waligona lelijaha walanga wakhuluma engelanhloni wathi:
Sai ta kama shi ta rungume shi da duban soyayya a fuskarta ta ce,
14 “Ngenzile umnikelo wobudlelwano ngekhaya; lamuhla ngizigcwalisile izifungo zami.
“Ina da hadaya ta salama a gida; yau zan cika alkawarina.
15 Yikho ngilapha ukukuhlangabeza; sengikudinge ngaze ngakuthola!
Saboda haka na fito don in sadu da kai; na neme ka na kuma same ka!
16 Sengiwendlele umbheda wami ngamalineni eGibhithe awemibalabala.
Na lulluɓe gadona da lili masu launi dabam-dabam daga Masar.
17 Sengiwuqholile umbheda wami ngemure, ngenhlaba langesinamoni.
Na yayyafa turare a gadona da mur, aloyes da kuma kirfa.
18 Woza sizitike ngothando kuze kuse; kasizijabulise ngothando!
Zo, mu sha zurfin ƙauna har safe; bari mu ji wa ranmu daɗi da ƙauna!
19 Indoda yami kayikho ekhaya; ihambile iye khatshana.
Mijina ba ya gida; ya yi tafiya mai nisa.
20 Ithwele isikhwama sayo sigcwele imali, ngakho kayibuyi kuze kube phakathi kwenyanga.”
Ya ɗauki jakarsa cike da kuɗi ba zai kuwa dawo gida ba sai tsakiyar wata.”
21 Ngamazwi akhe amnandi waledukisa ijaha lelo; walihuga ijaha lelo ngolimi olumnandi.
Da kalmomin rarrashi ta sa ya kauce; ta ɗauki hankalinsa da sulɓin maganarta.
22 Khonokho nje lahle lamlandela njengenkabi idonselwa ukuyabulawa, njengomziki uzingenisa emjibileni,
Nan take, ya bi ta kamar saniyar da za a kai mayanka, kamar wawa zuwa wurin da za a ba shi horo
23 umtshoko uze uyehlaba isibindi, njengenyoni ithothela ngaphansi kwesifu, ingaboni ukuthi isizingenise ekufeni.
sai da kibiya ta soki hantarsa, kamar tsuntsun da ya ruga cikin tarko, ba tare da sani zai zama sanadin ransa ba.
24 Ngakho-ke madodana ami, ngilalelani; zwanini lokhu engikutshoyo.
Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; ku kasa kunne ga abin da nake faɗa.
25 Lingayivumeli inhliziyo ikhangwe yizindlela zakhe, langabe iphumputhekele emikhubeni yakhe.
Kada ku bar zuciyarku ta juya zuwa hanyoyinta ko ku kauce zuwa hanyoyinta.
26 Banengi labo asebadilizile; izinkubela zakhe zilucaca olwesabekayo.
Ta zama sanadin fāɗuwar yawanci; kisan da ta yi ba ta ƙidayuwa.
27 Indlu yakhe ingumgudu oya engcwabeni, iholela phansi ezindongeni zokufa. (Sheol h7585)
Gidanta babbar hanya ce zuwa kabari mai yin jagora zuwa ɗakunan lahira. (Sheol h7585)

< Izaga 7 >