< Izaga 23 >

1 Nxa uhlala phansi usidla lombusi, nanzelela ukuthi kuyini okuphambi kwakho,
Sa’ad da ka zauna domin cin abinci da mai mulki, ka lura sosai da abin da yake gabanka,
2 ungazifaki ingqamu entanyeni nxa uhugwa yibuhwaba.
ka kuma sa wuƙa a maƙogwaronka in kai mai ci da yawa ne.
3 Ungahawukeli izibiliboco zakhe ngoba lokho kudla kuyakhohlisa.
Kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi gama wannan abinci ruɗu ne.
4 Ungazihlukuluzi uzigugise ngomsebenzi uzama inotho; hlakanipha wazi ukuzikhuza.
Kada ka gajiyar da kanka don ka yi arziki; ka kasance da hikimar dainawa.
5 Ungayibona manje inotho, masinyane isinyamalele, ngoba ngempela izamila impiko iphaphele emkhathini njengengqungqulu.
Da ƙyiftawar ido a kan wadata ta ɓace, gama tabbatacce sukan yi fikafikai sukan tashi sama kamar gaggafa.
6 Ungakudli ukudla komuntu oncitshanayo, ungazihawukeli izibiliboco zakhe;
Kada ka ci abincin mai rowa, kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi;
7 ngoba yena uhlezi ebalisa ngendleko. Angathi kuwe, “Dlana unathe,” kodwa kungasuki enhliziyweni yakhe.
gama shi wani irin mutum ne wanda kullum yana tunani game da tsadar abincin. Zai ce maka, “Ci ka sha,” amma zuciyarsa ba ta tare da kai.
8 Uzakuhlanza okuncane lokho okudlileyo ube udlalise amazwi akho okubonga.
Za ka yi amai ɗan abin da ka ci dukan daɗin bakinka kuwa zai tafi a banza.
9 Ungakhulumi lesithutha ngoba sizakweyisa inhlakanipho yamazwi akho.
Kada ka yi magana da wawa, gama zai yi wa maganar hikimarka ba’a.
10 Ungasusi ilitshe lakudala elomngcele loba uzithathele amasimu ezintandane,
Kada ka kawar da shaidar iyaka ta dā ko ka ɗiba gonar marayu,
11 ngoba uMhlengi wazo ulamandla; uzakuba ngumeli wazo aphikisane lawe.
gama mai Kāriyarsu yana da ƙarfi; zai kuwa yi magana dominsu.
12 Nikela inhliziyo yakho ekufundisweni lezindlebe zakho emazwini olwazi.
Ka mai da hankali ga umarni ka kuma kasa kunne ga kalmomin sani.
13 Ungayekeli ukumlaya umntwana; ukumtshaya ngoswazi akuyikumbulala.
Kada ka bar yaro ba horo; in ka yi masa horo da sanda, ba zai mutu ba.
14 Mjezise ngoswazi ukuze uphephise umphefumulo wakhe ekufeni. (Sheol h7585)
Ka hukunta shi da sanda ka ceci ransa daga mutuwa. (Sheol h7585)
15 Ndodana yami, aluba inhliziyo yakho ihlakaniphile, inhliziyo yami layo izathokoza;
Ɗana, in zuciyarka mai hikima ce, to, zuciyata za tă yi murna;
16 ingaphakathi yami izajabula lapho izindebe zakho zikhuluma okulungileyo.
cikin cikina zai yi farin ciki in leɓunanka suna maganar abin da yake daidai.
17 Inhliziyo yakho mayingahawukeli izoni, kodwa hlala utshisekela ukwesaba uThixo.
Kada ka bar zuciyarka tă yi ƙyashin masu zunubi, amma kullum tsoron Ubangiji za ka yi kishi.
18 Ngeqiniso lihle ikusasa lakho, lethemba lakho kaliyikucitshwa.
Tabbatacce akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
19 Lalela, ndodana yami, uhlakaniphe, ubeke inhliziyo yakho endleleni elungileyo.
Ka saurara, ɗana, ka zama mai hikima, ka kafa zuciyarka a hanyar da take daidai.
20 Ungahlangani leziminzi zewayini labazitika ngenyama,
Kada ka haɗa kai da waɗanda suke shan ruwan inabi da yawa ko masu haɗama kansu da abinci,
21 ngoba izidakwa lezihwaba ziba ngabayanga, ukuwozela kwazo kuzembese amadabudabu.
gama bugaggu da ruwan inabi da masu yawan ci sukan zama matalauta, gama jiri yakan yi musu sutura da tsummoki.
22 Lalela uyihlo owakuletha emhlabeni, njalo ungeyisi unyoko nxa eseluphele.
Ka kasa kunne ga mahaifinka, wanda ya ba ka rai, kada kuwa ka rena mahaifiyarka sa’ad da ta tsufa.
23 Thenga iqiniso ungalithengisi; zuza ukuhlakanipha lokuzikhuza lokuzwisisa.
Ka saye gaskiya kada kuwa ka sayar da ita; ka nemi hikima, horo da fahimi.
24 Uyise womuntu olungileyo uyathokoza kakhulu; lowo olendodana ehlakaniphileyo uyathokoza ngayo.
Mahaifin adali yana da farin ciki sosai; duk wanda yake da ɗa mai hikima yakan ji daɗinsa.
25 Sengathi uyihlo lonyoko bangathokoza; sengathi lowo owakuzalayo angajabula!
Bari mahaifinka da mahaifiyarka su yi murna; bari wadda ta haife ka tă yi farin ciki!
26 Ndodana yami, ngipha inhliziyo yakho, amehlo akho ahlale ezindleleni zami,
Ɗana, ka ba ni zuciyarka bari kuma idanunka su kiyaye hanyoyina,
27 ngoba isifebe singumgodi otshonayo lomfazi olibele lendlela ungumthombo oyingozi.
gama karuwa rami ne mai zurfi mace marar aminci matsattsiyar rijiya ce.
28 Uyacathamela njengesigebenga, andise amadoda angathembekanga.
Kamar’yan fashi, takan kwanta tana jira tana kuma ninka rashin aminci a cikin maza.
29 Ngubani ohlaba umkhosi? Ngubani olosizi na? Ngubani otshingayo? Ngubani olensolo na? Ngubani omahluzuhluzu ngeze? Ngubani omehlo abomvu gebhu na?
Wa yake wayyo? Wa yake baƙin ciki? Wa yake neman fada? Wa yake gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan idanu?
30 Yilabo abalibala ngewayini, abahamba bedinga inzwisa yewayini elidibanisiweyo.
Waɗanda suke daɗe suna shan ruwan inabi, waɗanda suke neman ƙoƙon damammen ruwan inabi.
31 Ungahugwa liwayini ulibona libomvu, nxa likhazimula enkomitshini, lapho lisehla kamnandi!
Kada ka ƙyifce ido a ruwan inabi sa’ad da ya yi ja, sa’ad da yana da kyan gani a cikin ƙwarya, sa’ad da yana gangarawa sumul a maƙogwaro!
32 Ekucineni liluma njengenyoka libe lobuhlungu obubulalayo njengenhlangwana.
A ƙarshe yana sara kamar maciji da kuma dafi kamar gamsheƙa.
33 Amehlo akho azabona izinto ezingaqedakaliyo lengqondo yakho icabange izinto ezididayo.
Idanunka za su riƙa gane-gane, zuciyarka kuma za su riƙa tunani abubuwa masu rikitarwa.
34 Uzakuba njengomuntu ondendayo phakathi kolwandle, olele esiqongweni sensika yomkhumbi.
Za ka zama kamar wanda yake barci a tsakiyar tekuna, kwance a sama itacen jirgin ruwa.
35 Uzakuthi, “Bangitshayile kodwa kangilimalanga! Bangibethile kodwa kakubuhlungu! Ngizavuka nini bo ngiyodinga obunye utshwala?”
Za ka ce “Sun buge ni, amma ban ji ciwo ba! Sun daddoke ni, amma ba na jin zafinsa! Yaushe zan farka don in ƙara shan wani?”

< Izaga 23 >