< Izaga 18 >
1 Umuntu ongelamusa uzifunela okwakhe; uyazilahla zonke iziqondiso ezinhle.
Mutumin da ba ya abokantaka yakan nema ya cika burinsa ne kaɗai; yakan ƙi yarda da kowace maganar da take daidai.
2 Isiwula kasikuthakazeleli ukuzwisisa kodwa sithokoza ngokutsho eyaso imibono.
Wawa ba ya sha’awa ya sami fahimta amma abin da yake so ya yi kaɗai, shi ne ya ba da ra’ayinsa.
3 Nxa kufika ububi kufika lokweyisa, njalo ihlazo liza lokudumazeka.
Sa’ad da mugunci ya zo, reni ma kan zo, haka kuma sa’ad da kunya ta zo, shan kunya kan biyo.
4 Amazwi omlomo womuntu ayinziki yamanzi, kodwa umthombo wokuhlakanipha ngumfudlana ontuntuzayo.
Kalmomin bakin mutum suna da zurfi kamar ruwaye, amma maɓulɓulan hikima rafi ne mai gudu.
5 Kakukuhle ukulungisela ababi loba ukungehluleli kuhle abangelacala.
Ba shi da kyau ka yi wa mugu alheri ko ka hana wa marar laifi adalci.
6 Izindebe zesiwula zisilethela ingxabano, lomlomo waso unxusa ukutshaywa.
Leɓunan wawa kan jawo masa faɗa, bakinsa kuma kan gayyaci dūka.
7 Umlomo wesiwula yiwo osidilizayo, lezindebe zaso zingumjibila womphefumulo waso.
Bakin wawa lalatar da kansa yake yi leɓunansa kuma tarko ne ga ransa.
8 Amazwi omuntu onyeyayo anjengezibiliboco; angena ekujuleni kwenhliziyo yomuntu.
Kalmomin mai gulma kamar abinci mai daɗi suke; sukan gangara zuwa can cikin gaɓoɓin mutum.
9 Lowo ovilaphayo emsebenzini wakhe ungumfowabo walowo odilizayo.
Wanda yake ragwanci a aikinsa ɗan’uwa ne ga wanda yakan lalatar da abubuwa.
10 Ibizo likaThixo liyinqaba eqinileyo; abalungileyo babalekela kulo baphephe.
Sunan Ubangiji hasumiya ce mai ƙarfi; masu adalci kan gudu zuwa wurinta don su zauna lafiya.
11 Inotho yezikhulu ingumuzi wazo ovikelweyo; zicabanga ukuthi imiduli yawo ayikhweleki.
Dukiyar masu arziki ita ce birninsu mai katanga; suna gani cewa ba za a iya huda katangar ba.
12 Umuntu uyazikhukhumeza ngenhliziyo yakhe, mandulo kokuba awe, ikanti ukuzithoba kwandulela udumo.
Kafin fāɗuwarsa zuciyar mutum takan yi girman kai, amma sauƙinkai kan zo kafin girmamawa.
13 Lowo ophendulayo engaqali alalele lobo yibuwula bakhe lehlazo lakhe.
Duk wanda yakan ba da amsa kafin ya saurara, wannan wauta ce da kuma abin kunya.
14 Umphefumulo womuntu uyamqinisa nxa egula, kodwa ngubani ongaphila elomoya owephukileyo na?
Sa rai da mutum ke yi kan taimake shi sa’ad da yake ciwo, amma in ya karai, to, tasa ta ƙare.
15 Inhliziyo yabaqedisisayo izuza ulwazi; indlebe zabahlakaniphileyo ziyakudinga.
Zuciya mai la’akari kan nemi sani; kunnuwan mai hikima kan bincika don yă koya.
16 Isipho siyamvulela indlela ophayo azuze ithuba lokubonana labakhulu.
Kyauta kan buɗe hanya wa mai bayarwa yakan kuma kai shi a gaban babban mutum.
17 Ecaleni okhuluma kuqala ubonakala enguye olungileyo, kuze kuqhamuke omunye ambuzisise.
Wanda ya fara mai da jawabi yakan zama kamar shi ne mai gaskiya, sai wani ya fito ya yi masa tambaya tukuna.
18 Ukwenza inkatho kuyakuqeda ukulwisana, kubehlukanise abaxabanayo.
Jefa ƙuri’a kan daidaita tsakanin masu faɗa ta kuma ajiye masu faɗan a rabe.
19 Umzalwane owonelweyo uba lukhuni kulomuzi ohonqolozelweyo, lezingxabano zinjengamasango enqaba avaliweyo.
Ɗan’uwan da aka yi wa laifi ya fi birni mai katanga wuyan shiryawa, kuma faɗace-faɗace suna kama da ƙofofin ƙarfe na fada.
20 Isisu somuntu sigcwaliswa yizithelo zomlomo wakhe; usuthiswa yisivuno sezindebe zakhe.
Daga abin da baki ya furta ne cikin mutum kan cika; girbi daga leɓunansa kuma yakan ƙoshi.
21 Ulimi lulamandla okuphila lokufa, njalo labo abaluthandayo bazakudla izithelo zalo.
Harshe yana da ikon rai da mutuwa, kuma waɗanda suke ƙaunarsa za su ci amfaninsa.
22 Lowo ozuza umfazi ufumana okuhle, athole umusa kuThixo.
Duk wanda ya sami mace ya sami abu mai kyau ya kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
23 Umyanga uyancenga ukuthi axolelwe, kodwa isinothi siphendula ngolaka.
Matalauci kan yi roƙo da taushi, amma mawadaci kan amsa da kakkausar murya.
24 Umuntu olabangane abanengi ucina kubi, kodwa kuba khona umngane othembeka okudlula umfowenu.
Mutum mai abokai masu yawa kan lalace, amma akwai abokin da yakan manne kurkusa fiye da ɗan’uwa.