< UMikha 2 >

1 Maye kulabo abaceba ububi, kulabo abaceba ukwenza okubi emibhedeni yabo! Ekudabukeni kokusa bayakwenza ngoba kusemandleni abo ukukwenza.
Taku ta ƙare, ku da kuke shirya makirci, ku da kuke ƙulle-ƙullen mugunta a kan gadonku! Da gari ya waye sai ku fita ku aikata mugunta domin ikon aikatawa yana hannunku.
2 Bahawukela amasimu bawathumbe, kanye lezindlu, bazithathe. Badlelezela umuntu ngomuzi wakhe, lomuntu wakibo ngelifa lakhe.
Kukan yi ƙyashin gonaki ku kuma ƙwace su, ku yi ƙyashin gidaje ku kuma ƙwace. Kukan zalunci mutum, ku ƙwace masa gidansa, har ku ƙwace masa gādonsa.
3 Ngakho uThixo uthi: “Ngiceba ukwenza umonakalo kulababantu, elingeke liziphephise kuwo. Kalisayikuhamba ngokuziqhenya, ngoba kuzakuba yisikhathi sencithakalo.
Saboda haka, Ubangiji ya ce, “Ina shirya wa waɗannan mutane bala’i, yadda ba za ku iya ceton kanku ba. Ba za ku ƙara tafiya kuna taƙama ba, gama zai zama lokacin bala’i ne.
4 Ngalolosuku abantu bazalihleka; bazaliklolodela ngale ingoma yokulila bathi: ‘Thina sichithwe okupheleleyo; ilifa labantu bami labiwe. Uyangithathela! Amasimu ethu uwanika abathengisi.’”
A wannan rana mutane za su yi muku ba’a za su yi muku gwalo da wannan waƙar makoki, ‘An lalatar da mu sarai; an rarraba mallakar mutanena. Ya ɗauke shi daga gare ni! Ya miƙa filayenmu ga maciyan amanarmu.’”
5 Ngakho-ke kawuzukuba laye ebandleni likaThixo ozalabela ilizwe ngenkatho.
Saboda haka ba za ku kasance da wani a taron jama’ar Ubangiji da zai raba ƙasar ta wurin jefa ƙuri’a ba.
6 Abaphrofethi babo bathi, “Lingaphrofethi. Lingaphrofethi ngalezizinto; ihlazo kaliyikusehlela.”
“Kada ku yi annabci” in ji annabawansu. “Kada ku yi annabci game da waɗannan abubuwa; abin kunya ba zai same mu ba.”
7 Wena ndlu kaJakhobe, kufanele yini ukuba kuthiwe, “UMoya kaThixo uzondile na? Uyazenza izinto ezinje na?” “Amazwi ami kawenzi okulungileyo kuye ozindlela zakhe ziqondile na?
Daidai ne a ce, ya gidan Yaƙub, “Ruhun Ubangiji yana fushi ne? Yana yin irin waɗannan abubuwa?” “Ashe, maganata ba tă amfane wanda ayyukansa suke daidai ba?
8 Okwamanje abantu bami sebehlamuke njengesitha. Lihlubula ingubo eligugu kulabo abedlulayo linganakile, njengabantu abavela empini.
Ba da daɗewa ba mutanena sun tashi kamar magabci. Kun tuɓe riga mai tsada daga waɗanda suke wucewa ba tare da kun damu ba, sai ka ce mutanen da suke komowa daga yaƙi.
9 Abesifazane babantu bami liyabaxotsha emizini yabo emihle. Lisusa isibusiso sami kokuphela ebantwaneni babo.
Kun kori matan mutanena daga gidajensu masu daɗi. Kuka kawar da albarkata har abada daga wurin’ya’yansu.
10 Sukani lihambe! Ngoba le akusindawo yenu yokuphumula, ngoba ingcolile, ichithekile, okungeke kulungiswe.
Ku tafi, ku ba ni wuri! Gama wannan ba wurin hutunku ba ne, gama ya ƙazantu, ya zama kangon da ya wuce gyara.
11 Nxa umqambi wamanga lomkhohlisi efika athi, ‘Ngizaliphrofethela iwayini elinengi lotshwala,’ uyabe engumphrofethi walababantu nje kuphela!”
In maƙaryaci da mazambaci ya zo ya ce, ‘Zan yi muku annabci ku sami wadataccen ruwan inabi da barasa,’ zai dai zama annabin da ya dace da wannan mutane ne!
12 “Impela ngizalibutha lonke, wena Jakhobe; impela ngizabaqoqela ndawonye abako-Israyeli abasalayo. Ngizabaqoqela ndawonye njengezimvu esibayeni, njengomhlambi wezimvu emadlelweni awo; indawo ibe lokuphithizela kwabantu.
“Tabbatacce zan tattara ku duka, ya gidan Yaƙub; zan tattara ku raguwar Isra’ila. Zan kawo su wuri ɗaya kamar tumaki a cikin garke, kamar garke a wajen kiwonsa; wurin zai cika da mutane.
13 Lowo ozavula indlela uzahamba phambi kwabo; bazafohla isango baphume. Inkosi yabo izadlulela phambi kwabo, uThixo abe phambi kwabo.”
Wanda ya fasa ƙofa ya buɗe, shi zai haura yă yi musu jagora, za su fashe bangon su fita. Sarkinsu zai wuce gabansu, Ubangiji kuma zai kasance a gaba.”

< UMikha 2 >