< UMathewu 1 >
1 Umbhalo wosendo lukaJesu Khristu indodana kaDavida, indodana ka-Abhrahama:
Littafin asalin Yesu Almasihu Dan Dauda, Dan Ibrahim.
2 U-Abhrahama wayenguyise ka-Isaka, u-Isaka uyise kaJakhobe, uJakhobe uyise kaJuda labafowabo,
Ibrahim shine mahaifin Ishaku, Ishaku shine mahaifin Yakubu, Yakubu shine mahaifin Yahuza da 'yan'uwansa.
3 uJuda uyise kaPherezi loZera, unina owayenguThamari, uPherezi uyise kaHezironi, uHezironi uyise kaRamu,
Yahuza shine mahaifin Farisa da Zera, ta wurin Tamar. Farisa kuma shine mahaifin Hasruna, Hasruna kuma shine mahaifin Aram.
4 uRamu uyise ka-Aminadabi, u-Aminadabi uyise kaNashoni, uNahishoni uyise kaSalimoni,
Aram shine mahaifin Amminadab, Amminadab shine mahaifin Nashon, Nashon shine mahaifin Salmon.
5 uSalimoni uyise kaBhowazi, unina owayenguRahabi, uBhowazi uyise ka-Obhedi, unina owayenguRuthe, u-Obhedi uyise kaJese,
Salmon shine mahaifin Bo'aza ta wurin Rahab, Bo'aza shine mahaifin Obida ta wurin Rut. Obida shine mahaifin Yesse,
6 uJese uyise wenkosi uDavida. UDavida wayenguyise kaSolomoni, unina owayeke waba ngumka-Uriya,
Yesse shine mahaifin sarki Dauda. Sarki Dauda shine mahaifin Sulaimanu ta wurin matar Uriya.
7 uSolomoni uyise kaRehobhowami, uRehobhowami uyise ka-Abhija, u-Abhija uyise ka-Asa,
Sulaimanu shine mahaifin Rehobo'am, Rehobo'am shine mahaifin Abija, Abija shine mahaifin Asa.
8 u-Asa uyise kaJehoshafathi, uJehoshafathi uyise kaJehoramu, uJehoramu uyise ka-Uziya,
Asa shine mahaifin Yehoshafat, Yehoshafat shine mahaifin Yoram, Yoram kuma shine mahaifin Uziya.
9 u-Uziya uyise kaJothamu, uJothamu uyise ka-Ahazi, u-Ahazi uyise kaHezekhiya,
Uziya shine mahaifin Yotam, Yotam shine mahaifin Ahaz, Ahaz shine mahaifin Hezekiya.
10 uHezekhiya uyise kaManase, uManase uyise ka-Amoni, u-Amoni uyise kaJosiya,
Hezekiya shine mahaifin Manassa, Manassa shine mahaifin Amon, sannan Amon shine mahaifin Yosiya.
11 uJosiya owayenguyise kaJekhoniya labafowabo ngesikhathi bethunjwe eBhabhiloni.
Yosiya shine mahaifin Yekoniya da 'yan'uwansa, dai dai locacin da aka kwashe su zuwa kasar Babila.
12 Emva kokuthunjwa eBhabhiloni: uJekhoniya wayenguyise kaSheyalithiyeli, uSheyalithiyeli uyise kaZerubhabheli,
Bayan kwasar su zuwa kasar Babila, Yekoniya shine mahaifin Sheyaltiyel, Sheyaltiyel shine mahaifin Zarubabel.
13 uZerubhabheli uyise ka-Abhiyudi, u-Abhiyudi uyise ka-Eliyakhimu, u-Eliyakhimu uyise ka-Azori,
Zarubabel shine mahaifin Abihudu, Abihudu shine mahaifin Eliyakim, sannan Eliyakim shine mahaifin Azuru.
14 u-Azori uyise kaZadokhi, uZadokhi uyise ka-Akhimu, u-Akhimu uyise ka-Elihudi,
Azuru shine mahaifin Saduku. Saduku shine mahaifin Akimu, sannan Akimu shine mahaifin Aliyudu
15 u-Elihudi uyise ka-Eliyazari, u-Eliyazari uyise kaMathani, uMathani uyise kaJakhobe,
Aliyudu shine mahaifin Ali'azara, Ali'azara shine mahaifin Matana, sannan Matana shine mahaifin Yakubu.
16 uJakhobe uyise kaJosefa, umkaMariya, owazala uJesu obizwa ngokuthi nguKhristu.
Yakubu shine mahaifin Yusufu maigidan Maryamu, wadda ta wurin ta ne aka haifi Yesu, wanda ake ce da shi Almasihu.
17 Ngokunjalo-ke, kwakulezizukulwane ezilitshumi lane sezizonke kusukela ku-Abhrahama kusiya kuDavida, ezilitshumi lane kusukela kuDavida kusiya ekuthunjweni yiBhabhiloni njalo ezilitshumi lane kusukela ekuthunjweni kusiya kuKhristu.
Tun daga Ibrahim zuwa Dauda, an yi tsara goma sha hudu ne, daga Dauda zuwa lokacin da aka kwashe su zuwa Babila, tsara goma sha hudu ne, sannan daga lokacin da aka kwashe su zuwa Babila zuwa Almasihu tsara goma sha hudu ne
18 UJesu Khristu wazalwa kanje: Unina uMariya wayethembise ukuthi uzakwendela kuJosefa kodwa kwathi bengakahlangani wabonakala esezithwele kwenziwe ngoMoya oNgcwele.
Ga yadda haihuwar Yesu Almasihu ta kasance. Mahaifiyarsa, Maryamu, tana tashi da Yusufu, amma kafin su yi aure, sai aka same ta da juna biyu ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
19 Ngoba umkakhe uJosefa wayeyindoda elungileyo emthethweni, njalo engafuni ukumyangisa ebantwini, wacabanga ukumala ngasese.
Mijinta, Yusufu, adalin mutum ne, amma ba ya so ya kunyatar da ita a sarari. Sai ya yi shawara ya sake ta a asirce.
20 Uthe esekucabangile lokhu, kwafika kuye ingilosi yeNkosi ephutsheni yathi, “Josefa ndodana kaDavida, ungesabi ukuthatha uMariya ukuba abe ngumkakho ngoba lokhu akhulelwe ngakho kuvela kuMoya oNgcwele.
Yana cikin tunanin wadannan al'amura, sai mala'ikan Ubangiji ya bayyana gareshi a mafarki, ya ce masa, “Yusufu, dan Dauda, kada ka ji tsoron daukar Maryamu a matsayin matarka. Gama abinda ke cikinta, ta wurin Ruhu Mai Tsarki aka same shi.
21 Uzabeletha indodana ozayetha ibizo uthi nguJesu ngoba uzasindisa abantu bakhe ezonweni zabo.”
Za ta haifi Da, za ka kira sunansa Yesu, domin za ya ceci mutanensa daga zunubansu.”
22 Konke lokhu kwenzakala ukuze kugcwaliseke okwatshiwo yiNkosi ngomphrofethi ukuthi:
Duk wannan ya faru ne domin a cika abinda aka fada ta bakin annabin, cewa,
23 “Intombi egcweleyo izakhulelwa izale indodana, bayibize ngokuthi ngu-Emanuweli” (okutsho ukuthi, “uNkulunkulu ulathi”).
“Duba, budurwa za ta sami juna biyu sannan za ta haifi da, za su kira sunansa Immanuel”-ma'ana, “Allah tare da mu.”
24 UJosefa esevukile ebuthongweni wenza lokho ingilosi yeNkosi eyayimlaye khona, wamthatha uMariya waba ngumkakhe.
Yusufu ya farka daga barci, ya yi kamar yadda mala'ikan Ubangiji ya umarce shi, sai ya dauke ta a matsayin matarsa.
25 Kodwa kazange embathe laye waze wabeletha indodana. Wayetha ibizo wathi nguJesu.
Amma Yusufu bai sadu da ita ba sai bayan da ta haifi da. Ya kira sunansa Yesu.