< ULukha 2 >

1 Ngalezonsuku uKhesari Agastasi wakhupha isimemezelo sokuthi abantu babalwe kulolonke ilizwe lombuso wamaRoma.
Ananan cikin kwanakin, sai Kaisar Augustas ya yi shela ya umarta a kidaya dukan mutane da ke zaune a cikin duniya.
2 (Lokhu kwakuyikubalwa kwabantu kokuqala okwenzakala uKhwirinu engumbusi wase-Asiriya.)
Wannan itace kidaya ta farko da aka yi lokacin da Kiriniyus yake mulkin Suriya.
3 Wonke umuntu waya edolobheni lakibo wayabhalisa.
Sabili da haka, kowa ya koma garinsa domin a yi masa rijista domin kidayan.
4 UJosefa laye wahamba esuka edolobheni leNazaretha eseGalile waya eJudiya, eBhethilehema idolobho likaDavida, ngoba wayengowendlu losendo lukaDavida.
Yusufu kuma ya tashi ya bar birnin Nazarat zuwa garin Baitalami da ke Yahudiya, wanda ake kuma kira birnin Dauda, domin shi daga zuriyar iyalin Dauda ne.
5 Waya khona ukuyabhalisa eloMariya, owayesethembise ukwendela kuye, esekhulelwe.
Ya je can ya yi rijista tare da Maryamu, wadda yake tashi tana kuma da juna biyu.
6 Bathi bekhonale safika isikhathi sokubelethwa komntwana,
Ya zama sa'adda suke can, lokaci ya yi da za ta haifi danta.
7 wazibula ngendodana. Wayigoqela ngamalembu, wayilalisa emkolweni wokudlela izifuyo ngoba babengelandawo endlini yezihambi.
Ta haifi da, dan farinta kuwa, ta nade shi da kyau da 'yan tsummoki. Ta sa shi cikin wani kwami na dabbobi, gama babu daki dominsu a masaukin.
8 Kwakulabelusi ababehlala emlageni eduze kwalapho, belinda imihlambi yabo yezimvu ebusuku.
A cikin wannan yankin, akwai makiyaya wadanda suke zama a sarari suna tsaron garken tumakinsu da dare.
9 Ingilosi yeNkosi yabonakala kubo, inkazimulo yeNkosi yakhanya ibazingelezile, ngakho besaba kakhulu.
Nan da nan, sai mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare su, daukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, sai suka figita kwarai.
10 Kodwa ingilosi yathi kubo, “Lingesabi. Ngizolitshela izindaba ezinhle ezizaletha intokozo enkulu ebantwini bonke.
Sai mala'ikan ya ce masu, “Kada ku ji tsoro, domin na kawo maku labari mai dadi da zai kawo murna da yawa ga dukan mutane.
11 Lamuhla lizalelwe uMsindisi emzini kaDavida; unguKhristu iNkosi.
Yau an haifi maku mai ceto a cikin birnin Dauda! Shine Almasihu Ubangiji!
12 Lokhu kuzakuba yisibonakaliso kini: Lizathola umntwana egoqelwe ngamalembu elele emkolweni.”
Wannan itace alama da za a ba ku. Za ku ga dan jariri nade cikin 'yan tsummoki kwance cikin kwamin dabbobi.”
13 Masinyane kwaqhamuka ixuku lebandla lasezulwini lengilosi lidumisa uNkulunkulu lisithi,
Nan take, sai ga babban taro daga sama tare da mala'ikan suna yabon Allah, suna cewa,
14 “Udumo kuNkulunkulu emazulwini aphezulu, lokuthula emhlabeni kulabo abathole umusa kuye.”
“Daukaka ga Allah daga bisa, bari salama ta kasance a duniya tsakanin mutanen da ya ke jin dadinsu.”
15 Kwathi izingilosi sezibatshiyile zabuyela ezulwini, abelusi bakhulumisana bathi, “Kasihambeni siye eBhethilehema siyobona into le esiyenzakele, iNkosi esisitshele ngayo.”
Ya zama sa'adda mala'iku suka bar su zuwa cikin sama, sai makiyayan su ka ce wa junansu, “Bari mu je Baitalami mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya nuna mana.”
16 Bahle basuka ngokuphangisa, bafica uMariya loJosefa losane olwalulele emkolweni wokudlela izifuyo.
Su ka yi hamzari suka tafi can sun iske Maryamu da Yusufu, suka ga jaririn kuwa kwance a cikin kwamin dabbobin.
17 Bathi sebembonile umntwana, batshela abanengi ngalokho ababekutshelwe mayelana lomntwana lo,
Bayan da sun ga wannan, suka gaya wa mutane abinda aka gaya masu game da wannan yaro.
18 kwathi bonke abalizwayo bamangaliswa yilokho abakuzwa ngabelusi.
Dukan wadanda su ka ji, su ka yi mamaki kwarai game da abin da makiyayan su ka gaya masu.
19 Kodwa uMariya wazenza igugu zonke lezizinto wazishicilela enhliziyweni yakhe.
Amma ita Maryamu ta ci gaba da tunani akan wadanan abubuwa da ta ji, tana tunani mai zurfi a cikin zuciyarta.
20 Abelusi babuyela, bedumisa njalo bebabaza uNkulunkulu ngezinto zonke ababezizwile njalo bazibona, zaba yikho kanye ababekutsheliwe.
Makiyayan suka koma suna ta daukaka da yabon Allah domin dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, dadai da yadda aka gaya masu.
21 Ngosuku lwesificaminwembili, sekuyisikhathi sokuthi asokwe, wethiwa ibizo elithi nguJesu, ibizo ayelithiwe yingilosi engakabunjwa esiswini.
Da ya kai kwana takwas, lokacin da za a yi wa jaririn kaciya, sai aka rada masa suna Yesu, sunan da mala'ikan ya bashi kamin a yi cikinsa.
22 Kwathi lapho sesiphelile isikhathi sabo sokuhlanjululwa ngokomthetho kaMosi, uJosefa loMariya bamusa eJerusalema ukuyamnikela eNkosini
Da kwanakin tsarkakewar su ya wuce bisa ga shari'ar Musa, Yusufu da Maryamu suka kawo shi cikin haikali a Urushalima dominsu mika shi ga Ubangiji.
23 (njengokulotshiweyo eMthethweni weNkosi ukuthi, “Lonke izibulo lesilisa kumele linikelwe eNkosini”),
Kamar yadda aka rubuta a dokokin Ubangiji, “Za a kira duk da na fari kebabbe ga Ubangiji.”
24 njalo kwenziwe umhlatshelo kulandelwa lokho okutshiwo nguMthetho weNkosi othi: “amajuba amabili loba inkwilimba ezisesezincane ezimbili.”
Suka kuma zo su mika hadaya bisa ga yadda aka fada a shari'ar Ubangiji, “Kurciyoyi biyu ko 'yan tantabaru biyu.”
25 Kwakukhona eJerusalema indoda eyayithiwa nguSimiyoni, yayilungile njalo ikholwa. Yayilindele ukududuzwa kuka-Israyeli, njalo uMoya oNgcwele wawuphezu kwayo.
Ga shi akwai wani mutum a Ushalima mai suna Siman. Wannan mutum adali ne kuma mai ibada. Yana jiran mai ta'aziyar Isra'ila, kuma Ruhu Mai-sarki na bisansa.
26 Kwakwambuliwe kuye nguMoya oNgcwele ukuthi wayengayikufa engakaboni uKhristu weNkosi.
An kuma bayyana masa ta wurin Ruhu Mai-tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kristi na Ubangiji.
27 Waholwa nguMoya wangena emagumeni ethempeli. Kwathi abazali sebemlethile umntwana uJesu ukumenzela lokho okwakufunwa ngumkhuba woMthetho,
Wata rana Siman ya zo cikin haikali ta wurin jagorar Ruhu Mai-tsarki. Da iyayen suka kawo yaron ciki, wato Yesu, domin su cika sharudan da shari'ar ke bukata,
28 uSimiyoni wamgona ngezingalo zakhe wadumisa uNkulunkulu esithi:
sai Siman ya karbe shi cikin hanuwansa, ya yabi Allah ya ce,
29 “Thixo, Nkosi, njengoba wavele wathembisa, manje-ke iyekele ihambe ngokuthula inceku yakho.
“Yanzu bari bawanka ya tafi da salama, Ubangiji, bisa ga kalmarka.
30 Ngoba amehlo ami aseyibonile insindiso yakho,
Domin idanuna sun ga cetonka,
31 oyilungisileyo phambi kwezizwe zonke,
wanda ka shirya a gaban dukan mutane:
32 ukukhanya kokwambulela abeZizwe lokwenkazimulo yabantu bakho bako-Israyeli.”
Haske ne na wahayi ga al'ummai, kuma daukakar mutanenka Isra'ila.”
33 Oyise lonina womntwana bamangala kakhulu ngalokho okwakukhulunywa ngaye.
Mahaifin yaron da Mahaifiyarsa, sun yi mamaki kwarai domin abubuwan da aka fada akansa.
34 USimiyoni wasebabusisa, wathi kuMariya unina: “Umntwana lo umiselwe ukuwa lokuvuka kwabanengi ko-Israyeli, lokuba yisibonakaliso esizagconwa,
Sai Siman ya albarkace su ya ce wa uwatasa Maryamu, “Ki ji da kyau, wannan yaro zai zama sanadiyar faduwa da tashin mutane dayawa a Isra'ila, kuma alama wadda ake kushen ta.
35 ukwenzela ukuthi imicabango yabanengi ivele obala. Njalo inkemba izawugwaza umphefumulo wakho lawe.”
Kuma takobi zai tsaga zuciyar ki yadda tunanin mutane za ya bayyana.”
36 Kwakukhona njalo umphrofethikazi, u-Ana, indodakazi kaFanuweli, owesizwana sika-Asheri. Wayesemdala kakhulu: wayephile lomkakhe okweminyaka eyisikhombisa ngemva kokwenda kwakhe,
Wata annabiya mai suna Annatu ta na nan wurin. Ita diyar Fanuyila ce daga kabilar Ashiru. Ta riga ta manyanta a shekaru sosai. Ta kasance da maigidanta shekaru bakwai bayan auren ta,
37 wasesiba ngumfelokazi waze waba leminyaka engamatshumi ayisificaminwembili lane. Kazange lanini asuke ethempelini kodwa wayekhonza ubusuku lemini, ezila njalo ekhuleka.
sannan ta yi zama gwambranci na shekaru tamanin da hudu. Ba ta taba barin haikali ba, tana ci gaba da yi wa Ubangiji sujada, dare da rana.
38 Wabuya kubo ngalesosikhathi wabonga kuNkulunkulu, wakhuluma ngomntwana kubo bonke ababelindele ukuhlengwa kweJerusalema.
A dadai lokacin nan, ta hau zuwa wurinsu ta fara yi wa Allah godiya. Ta gaya wa dukan wadanda ke jiran fansar Urushalima.
39 Kwathi lapho uJosefa loMariya sebekwenzile konke okwakufuneka ngoMthetho weNkosi babuyela eGalile, edolobheni lakibo elaseNazaretha.
Da su ka gama komai da aka bukace su suyi bisa ga tafarkin shari'ar Ubangiji, sai suka koma Galili, zuwa birninsu, Nazarat.
40 Umntwana wakhula, waqina; wagcwala inhlakanipho, njalo umusa kaNkulunkulu waba phezu kwakhe.
Yaron kuma ya yi girma ya zama da karfi, yana karuwa da hikima, alherin Ubangiji kuma yana kansa.
41 Iminyaka yonke abazali bakhe baya eJerusalema belanda uMkhosi wePhasika.
Iyayensa sukan tafi Urushalima kowacce shekara domin idin ketarewa.
42 Kwathi eseleminyaka elitshumi lambili baya emkhosini njengenjayelo.
Da yana shekara goma sha biyu, suka sake haurawa daidai lokacin idin a al'adance.
43 Kwathi uMkhosi usuphelile, abazali bakhe sebebuyela ekhaya, umfana uJesu wasala eJerusalema, kodwa bona belibele.
Bayan da sun cika dukan kwanakin idin, sun fara dawowa gida. Amma dan yaron Yesu ya jinkirta ya zauna a Urushalima, kuma iyayensa basu sani ba.
44 Bazihambela ilanga lonke bona becabanga ukuthi ukhona edwendweni lwabo. Basebeqalisa ukumdinga phakathi kwezihlobo zabo labangane.
Suna tsammani yana tare da sauran mutane da suke tafiya tare, sai suka yi tafiya na kwana daya. Suka fara neman sa a cikin danginsu da abokansu.
45 Bathi sebemswele babuyela eJerusalema bayamdinga.
Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima suna cigiyar sa a can.
46 Ngemva kwensuku ezintathu bamfumana emagumeni ethempeli ehlezi phakathi kwabafundisi elalele njalo ebabuza imibuzo.
Ya zama bayan kwanaki uku, su ka same shi a cikin haikali, yana zama a tsakiyar malamai, yana sauraron su yana kuma yi masu tambayoyi.
47 Wonke umuntu owamuzwayo wamangala ngokuzwisisa kwakhe kanye lempendulo zakhe.
Dukan wadanda suka ji shi suna ta mamakin fahimtar sa da amsoshin sa.
48 Abazali bakhe bathi bembona bamangala kakhulu. Unina wathi kuye, “Ndodana, kungani usinqinekisa kangaka? Uyihlo lami besesikhathazekile sikudinga.”
Da suka gan shi, suka yi mamaki kwarai. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Da na, don me ka yi mana haka? Ka ji, mahaifinka da ni muna ta neman ka rai a bace.”
49 Yena wabuza wathi, “Belivele lingidingelani kanti? Belingazi yini ukuthi bekumele ngibe sendlini kaBaba?”
Ya ce masu, “Don me kuke nema na? Ba ku sani cewa dole in kasance a gidan Ubana ba?”
50 Kodwa kabazwisisanga lokho ayekutsho kubo.
Amma ba su gane abin da yake nufi da kalmomin nan ba.
51 Wasehamba labo eNazaretha wahlala ebalalela. Kodwa unina wazenza igugu zonke lezi izinto enhliziyweni yakhe.
Sa'annan ya koma gida tare da su zuwa Nazarat yana kuma masu biyayya. Mahaifiayarsa kuma ta ajiye dukan wadannan abubuwa a zuciyarta tana yin tunani akansu.
52 UJesu wakhula ngenhlakanipho, langomzimba langokuthandwa nguNkulunkulu labantu.
Amma Yesu ya ci gaba da hikima da girma, ya kuma karu da tagomashi wurin Allah da mutane.

< ULukha 2 >