< Izililo 1 >

1 Kuthule kuthe cwaka! Yeka lelidolobho elalinyakazela abantu! Selinjengomfelokazi, kanti lalilodumo phakathi kwezizwe. Lona elaliyindlovukazi phakathi kwezigodi, khathesi seliyisigqili.
Yanzu birnin ya zama babu kowa a ciki, birnin da a dā yake cike da mutane! Yanzu birnin ya zama kamar gwauruwa, wadda a dā babba ce ita a cikin ƙasashe! Ita da take sarauniya a cikin larduna yanzu ta zama baiwa.
2 Linjengowesifazane okhala kabuhlungu ebusuku, inyembezi zithe hlikilili ezihlathini. Kakho phakathi kwazo zonke izithandwa zakhe ongamduduza. Bonke abangane bakhe bamhlamukele; sebeyizitha zakhe.
Tana yin kuka mai zafi da dare, hawaye na gangara a kan kumatunta. A cikin masoyanta duka babu wanda ya yi mata ta’aziyya. Duk abokanta sun yashe ta; sun zama abokan gābanta.
3 UJuda useye ebugqilini ngemva kokuhlupheka lokudonsa nzima. Usehlala phakathi kwabezizwe; akatholi ndawo yokuphumula. Bonke abamzingelayo bamxhumile ephakathi kokuhlupheka kwakhe.
Bayan wahala da baƙin ciki, Yahuda ta tafi bauta. Ta zauna a cikin ƙasashe, ba tă samu wurin hutawa ba. Duk masu fafararta sun same ta sa’ad da take cikin matuƙar ɓacin rai.
4 Iyalila imigwaqo eya eZiyoni, ngoba kasekho ozayo emikhosini yalo emisiweyo. Wonke amasango alo asekhohlakele, abaphristi balo bayabubula, amantombazana alo ayagomela, lona lidabukile kakhulu.
Hanyoyin zuwa Sihiyona suna makoki, gama ba wanda ya zo bikin da ta shirya. Ba kowa a hanyoyin shiganta. Firistocinta suna gurnani,’yan matana kuma suna wahala, kuma tana cikin shan wahala ƙwarai.
5 Izitha zalo sezingababusi balo; ziyaklamasa. UThixo ulehlisele usizi ngenxa yezono zalo ezinengi. Abantwabalo bathunjiwe, baba yizigqili zezitha.
Maƙiyanta sun zama shugabanninta; Abokan gābanta suna da kwanciyar rai. Ubangiji ya kawo mata ɓacin rai domin yawan zunubanta.’Ya’yanta sun tafi bauta, a ƙarƙashin maƙiyanta.
6 Kuphelile konke ukubenyezela kweNdodakazi yaseZiyoni. Amakhosana ayo asenjengezimpala ezingatholi amadlelo; zibalekile zilambile zingelamandla zibalekela umzingeli.
Diyar Sihiyona ba ta da sauran daraja.’Ya’yan sarakunanta sun zama kamar bareyi waɗanda suka rasa wurin kiwo; cikin rashin ƙarfi suka guje wa masu fafararsu.
7 Ngezinsuku zokuhlupheka lokuntula, iJerusalema iyayikhumbula inotho eyayingeyayo ngensuku zayo. Kuthe abantu bayo sebewela ezandleni zezitha, akubanga khona ongayinceda. Zayikhangela nje izitha zayo zahleka ukuchitheka kwayo.
A cikin kwanakin da take shan wahala take kuma yawo Urushalima ta tuna da dukan dukiyar da take da ita a kwanakin dā can. Sa’ad da mutanenta suka faɗa cikin hannun abokan gābanta, ba wanda ya taimake ta. Maƙiyanta suka dube ta suka yi mata dariya don hallakar da ta auko mata.
8 IJerusalema yonile kakhulu, ngakho isingcolile. Bonke ababeyihlonipha sebeyidelela, ngoba sebebonile ubuze bayo; yona ngokwayo ibubula ize ifulathele.
Urushalima ta yi zunubi ƙwarai saboda haka ta zama marar tsarki. Dukan masu martaba ta sun raina ta, gama sun ga tsiraicinta; ita ma da kanta tana nishi da ƙyar ta kuma juya baya.
9 Ukungcola kwayo kwabhixa izidwaba zayo; kayinakanga ikusasa yayo. Ukuwa kwayo kwesabeka, kungekho oyiduduzayo. “Oh Thixo, ake ukhangele ukuhlupheka kwami, ngoba isitha sesinqobile.”
Ƙazantarta ta manne wa rigunanta; ba tă kula da nan gaba ba, fāɗuwarta kuwa babban abu ne; babu wanda zai yi mata ta’aziyya. “Duba, ya Ubangiji, ka ga wahalata, gama maƙiyi ya yi nasara.”
10 Isitha saphanga yonke inotho yayo; yabona izizwe ezingakholwayo zingena endlini yayo engcwele, bona labo owabanqabela ukungena phakathi kwebandla lakho.
Maƙiya ya kwashe dukiyarta duka; ta ga mutanen da ba su san Allah ba sun shiga wuri mai tsarkinta waɗanda ka hana su shiga taron jama’arka.
11 Bonke abantu bayo bayagomela behamba bedinga ukudla; bathengisa inotho yabo eligugu ngokudla ukuze bangafi. “Oh Thixo, ake ungihawukele ngoba sengidelelwa.”
Dukan mutanenta suna nishi da ƙyar suna neman burodi; sun sayar da dukiyarsu don su samu abinci don kada su mutu da yunwa. “Ubangiji, ka duba ka gani, gama an yashe ni.”
12 “Kakusilutho kini yini lina lonke elidlula lapha? Ake likhangele nje libone. Kambe kukhona ukuhlupheka okulingana lokwami, khona lokhu engakwehliselwayo, nguThixo ngosuku lokuvutha kolaka lwakhe?
“Ko wannan ba wani abu ba ne a wurinku, dukanku masu wucewa? Ku duba ku gani. Ko akwai wata wahala kamar irin wadda nake sha, wadda Ubangiji ya auko mini a cikin zafin fushinsa?
13 Wehlisa umlilo uvela phezulu, wawehlisela phakathi kwamathambo ami. Wangithiya ezinyaweni ngomambule, wangibuyisela emuva. Wangenza ngaba lesizungu, ngaswela amandla ilanga lonke.
“Daga sama ya aiko da wuta, ya aiko ta cikin ƙasusuwana. Ya shimfiɗa raga a ƙafafuna ya juyo da ni. Ya bar ni ni kaɗai, sumamme dukan yini.
14 Izono zami zisongwe zaba lijogwe; ngezandla zakhe wazelukela ndawonye. Zetheswe entanyeni yami, uThixo wangiqeda amandla. Usengifuqele kulabo engingeke ngimelane labo.
“Ya ɗaura zunubaina a wuyana; aka naɗe su a hannuwansa. Aka rataye su a wuyana Ubangiji ya kwashe ƙarfina. Ya bashe ni ga waɗanda suka fi ni ƙarfi.
15 UThixo kabemukelanga bonke abangabebutho lami; usebize impi ukuthi ingihlasele, ichoboze zonke izinsizwa zami. Esihluzweni sakhe sewayini, uThixo unyathelele phansi iNdodakazi yakoJuda eGcweleyo.
“Ubangiji ya ƙi duk mayaƙan da suke tare da ni; ya sa wata runduna ta tayar mini ta kuma tattake samarina. Ubangiji ya tattake budurwa Diyar Yahuda kamar’ya’yan inabi a wurin matsewa.
16 Yikho ngilila, amehlo ami empompoza inyembezi. Kakho oseduze ongangiduduza, kakho ongavusa umphefumulo wami. Abantwabami sebeswela ngoba isitha sinqobile.”
“Dalilin da ya sa nake kuka ke nan idanuna kuma suna ta zubar da hawaye. Babu wani a kusa da zai yi mini ta’aziyya, ba wanda zai sabunta ruhuna.’Ya’yana sun zama fakirai domin maƙiyina ya yi nasara.”
17 IZiyoni yelulile isandla sayo kodwa kakho oyiduduzayo. UThixo usekumisile ngoJakhobe ukuthi abakhelene laye babe yizitha zakhe; iJerusalema isiphenduke yaba yinto engcolileyo kubo.
Sihiyona ta miƙa hannunta, amma ba wani da zai yi mata ta’aziyya. Ubangiji ya umarta cewa maƙwabtansa za su zama maƙiyansa; Urushalima ta zama abar ƙyama a cikinsu.
18 “UThixo ulungile, kodwa ngaphikisana lomlayo wakhe. Lalelani bantu lonke; khangelani ukuhawula kwami. Izinsizwa lezintombi zami zonke sezaya ekuthunjweni.
“Ubangiji mai adalci ne, duk da haka na yi tawaye da umarninsa. Ku saurara, jama’a duka; ku dubi wahalar da nake sha. Samarina da’yan matana duka sun tafi bauta.
19 Ngakhala kulabo engidlelana labo, kodwa banginina. Abaphristi bami labadala bami babhubhela phakathi kwedolobho besadinga ukudla, ukuze baziphilise.
“Na kira abokaina amma sun yashe ni. Firistocina da dattawana sun hallaka a cikin birnin yayinda suke neman abinci don kada su mutu da yunwa.
20 Ake ubone, Oh Thixo, ukuthi ngihlupheka njani! Ngiyatsha ngaphakathi kwami, ngidungekile enhliziyweni yami, ngoba bengilihlongandlebe. Ngaphandle, inkemba iyadabukisa; ngaphakathi, yikufa kodwa.
“Duba, Ubangiji, ka ga ƙuncin da nake ciki! Ina shan azaba a raina, ba ni da kwanciyar rai a cikin zuciyata, domin na yi tawaye sosai. A waje takobi na kisa; a ciki kuma akwai mutuwa.
21 Abantu bakuzwile ukububula kwami, kodwa kakho ongangiduduza. Zonke izitha zami zikuzwile ukuhlupheka kwami; ziyathokoza ngalokhu okwenzileyo. Sengathi ungalufikisa lolusuku owalumisayo, ukuze labo babe njengami.
“Mutane suna ji ina nishi da ƙyar, amma ba wanda zai yi mini ta’aziyya. Dukan maƙiyana sun ji wahalar da nake ciki; suna farin ciki da abin da ka yi. Ka kawo ranan nan da ka sanar domin su ma su zama kamar ni.
22 Abuvele kuwe bonke ububi babo; yenza kubo konke okwenzileyo kimi ngenxa yezono zami zonke. Kunengi ukububula kwami, lenhliziyo yami iphela amandla.”
“Bari ka ga muguntarsu duka; ka yi musu yadda ka yi mini domin dukan zunubansu. Nishina da yawa kuma zuciyata ta gaji.”

< Izililo 1 >