< Abahluleli 18 >
1 Ngalezonsuku u-Israyeli wayengelankosi. Njalo ngalezonsuku abosendo lukaDani babedinga indawo engeyabo, lapho ababengahlala khona, ngoba babengakabi sendaweni eyilifa labo phakathi kwezizwana zako-Israyeli.
To, a kwanakin nan Isra’ila ba ta da sarki. A kwanakin kuwa zuriyar Dan tana neman wurinsu na zama, gama ba su riga sun sami gādo tare da kabilan Isra’ila ba.
2 Ngakho abakoDani bathuma amabutho amahlanu avela eZora lase-Eshithawoli ukuyahlola ilizwe lokulibona. Amadoda la ayemele zonke insendo zakibo. Zathi kubo, “Hambani liyehlola ilizwe.” Amadoda lawo angena elizweni lezintaba elako-Efrayimi ayafika endlini kaMikha, lapho alala khona.
Saboda haka mutanen Dan suka aika jarumawa guda biyar daga Zora da Eshtawol don su leƙi asirin ƙasar su kuma bincike ta. Waɗannan mutanen sun wakilci dukan kabilar. Suka ce musu, “Ku je, ku bincike ƙasar.” Mutanen suka shiga ƙasar tudu ta Efraim suka zo gidan Mika, inda suka kwana.
3 Kwathi eseseduze lendlu kaMikha alazi ilizwi lejaha elingumLevi; ngakho aphendukela khona alibuza athi, “Ngubani owakuletha lapha? Wenzani kule indawo? Ufunani lapha?”
Sa’ad da suka yi kusa da gidan Mika, sai suka gane muryar saurayin nan Balawe; saboda haka suka shiga wurin suka tambaye shi, “Wa ya kawo ka nan? Me kake yi a nan? Me ya sa kake a nan?”
4 Lawatshela elalikwenziwe nguMikha, laselisithi, “Ungiqatshile njalo ngingumphristi wakhe.”
Ya gaya musu abin da Mika ya faɗa masa ya ce, “Ya ɗauke ni aiki ya kuma sa in zama masa firist.”
5 Asesithi kulo, “Ake usibuzele kuNkulunkulu ukuthi uhambo lwethu luzaphumelela na.”
Sa’an nan suka ce masa, “Muna roƙonka ka nemi mana nufin Allah don mu sani ko tafiyarmu tana da nasara.”
6 Umphristi wawaphendula wathi, “Hambani ngokuthula. Uhambo lwenu luvunyelwe nguThixo.”
Firist ya amsa ya ce, “Ku sauka lafiya, gama tafiyarku tana da yardan Ubangiji.”
7 Ngakho amadoda amahlanu lawo asuka aya eLayishi, lapho abona ukuthi abantu bakhona babezihlalele bevikelekile njengamaSidoni, belokuthula njalo bevikelekile. Njalo babehlezi khatshana lamaSidoni njalo bengelabuhlobo lomunye umuntu.
Saboda haka mutum biyar ɗin suka tashi suka iso Layish, inda suka ga mutane suna zamansu a huce, kamar Sidoniyawa, ba sa zato ga tsaro. Kuma da yake ƙasarsu ba ta bukata kome, suna da wadata. Suna kuma nesa da Sidoniyawa, ba sa kuma hulɗa da kowa.
8 Esebuyele eZora lase-Eshithawoli, abafowabo bawabuza bathi, “Libone kunjani?”
Da suka komo Zora da Eshtawol,’yan’uwansu suka tambaye su, “Me kuka gano?”
9 Aphendula athi, “Phangisani, kasibahlaseleni! Sibonile ukuthi ilizwe lelo lihle kakhulu. Kaliyikwenza lutho na? Lingazilazili ukuya khonale lilithathe.
Suka ce, “Ku zo mu yaƙe su! Mun ga ƙasar tana da kyau sosai. Ba za ku yi wani abu ba? Kada ku yi wata-wata, ku je kun mallaki ƙasar.
10 Ekufikeni khonale lizathola abantu abanganqinekeli lutho lelizwe elibanzi uNkulunkulu aselifake ezandleni zenu, ilizwe elingasweli lutho.”
Sa’ad da kun kai can, za ku iske mutanen suna zama a sake, ƙasar kuwa mai faɗi ce wadda Allah ya sa a hannuwanku, ƙasar da ba tă rasa kome ba.”
11 Lapho-ke amadoda osendo lwakoDani angamakhulu ayisithupha ahlomela ukulwa, asesuka eZora kanye le-Eshithawoli.
Sai mutane ɗari shida daga kabilar Dan suka yi ɗamarar yaƙi, suka tashi daga Zora da Eshtawol.
12 Ekuhambeni kwawo amisa izihonqo eduze leKhiriyathi-Jeyarimi koJuda. Yikho-nje indawo esentshonalanga kweKhiriyathi-Jeyarimi ithiwa yiMahane Dani kuze kube lamhla.
A kan hanyarsu suka kafa sansani kusa da Kiriyat Yeyarim a Yahuda. Shi ya sa a ana kira wurin nan yamma da Kiriyat Yeyarim Mahane Dan har wa yau.
13 Esuka lapho aya elizweni lezintaba elako-Efrayimi afika endlini kaMikha.
Daga can suka tafi ƙasar tudu ta Efraim suka zo gidan Mika.
14 Amadoda amahlanu ayehambe ukuyahlola ilizwe leLayishi athi kubafowabo bakoDani, “Liyakwazi yini ukuthi enye yalezizindlu ilesembatho semahlombe, labanye onkulunkulu basendlini, lesithombe esihuqwe ngesiliva? Khathesi selikwazi okumele likwenze.”
Sa’an nan mutum biyar ɗin nan da suka leƙi asirin ƙasar Layish suka ce wa’yan’uwansu, “Kun san cewa ɗaya daga cikin gidajen nan yana da efod, waɗansu allolin iyali, siffar da aka sassaƙa da kuma gunki na zubi? To, kun san abin da za ku yi.”
15 Ngakho-ke aphambukela khona aya endlini yejaha elingumLevi koMikha, alibingelela.
Saboda haka suka juya a wurin suka shiga gidan saurayin nan Balawe a wajen Mika suka gaishe shi.
16 AbakoDani abangamakhulu ayisithupha, ababehlomele ukulwa, bema entubeni yesango.
Mutanen Dan ɗari shida da suka sha ɗamarar yaƙi suka tsaya a bakin ƙofa.
17 Abahlanu ababeyehlola ilizwe bangena phakathi bathatha isithombe esibaziweyo, lesembatho semahlombe, labanye onkulunkulu basendlini, umphristi lamadoda ahlomileyo angamakhulu ayisithupha bemi entubeni yesango.
Sai mutum biyar da suka leƙi asirin ƙasar suka shiga ciki suka ɗauke gunkin da aka sassaƙa, efod, sauran allolin gida da kuma gunki na zubi yayinda firist ɗin tare da mutane ɗari shida da suka yi ɗamarar yaƙi suna tsaye a bakin ƙofa.
18 Kwathi amadoda la esengene endlini kaMikha athatha isithombe esibaziweyo, lesembatho semahlombe, labanye onkulunkulu basendlini kanye lesithombe esibunjiweyo, umphristi wathi kubo, “Lenzani na?”
Sa’ad da waɗannan mutane suka shiga gidan Mika suka ɗauke gunkin da aka sassaƙa, efod, sauran allolin gida da kuma gunki na zubi, sai firist ya ce musu, “Me kuke yi?”
19 Amphendula athi, “Thula! Ungatsho lutho. Woza uhambe lathi, ube ngubaba lomphristi wethu. Akungcono yini ukuthi usebenzele isizwana losendo lwako-Israyeli njengomphristi kulabendlu yomuntu oyedwa?”
Suka ce, “Ka yi shiru! Kada ka ce wani abu. Zo tare da mu, ka zama mahaifinmu da kuma firist. Bai fi maka ka yi wa kabila da kuma zuriya a Isra’ila aikin firist ba, da ka bauta wa iyali guda kawai?”
20 Umphristi wathokoza. Wathatha isembatho semahlombe, labanye onkulunkulu basendlini kanye lesithombe esibaziweyo wahamba labantu.
Sai firist ya yi farin ciki. Ya ɗauki efod, sauran allolin gida da siffar da aka sassaƙa ya tafi tare da mutanen.
21 Sebefake abantwababo abancane, lezifuyo zabo kanye lempahla zabo phambi kwabo, baphenduka bahamba.
Suka sa’ya’yansu ƙanana a gaba, dabbobinsu da mallakansu a gabansu, suka juya suka tafi.
22 Sebehambe isibanga esithize besuka endlini kaMikha, abantu ababehlala eduzane lendlu kaMikha babizelwa ndawonye baxhuma abakoDani.
Sa’ad da suka yi ɗan nisa daga gidan Mika, sai aka kira mutanen da suke maƙwabtakar da Mika suka taru suka bi mutanen Dan suka cim musu.
23 Kwathi bebamemeza, abakoDani baphendula bathi kuMikha, “Kungani ubize abantu bakho ukuba balwe?”
Da suna ihu suna binsu, sai mutanen Dan suka waiga suka cewa Mika, “Mece ce damuwarka da ka kira mutanenka su zo su fāɗa mana?”
24 Yena waphendula wathi, “Lithethe onkulunkulu engabenzayo lomphristi wami, lahamba. Kuyini okunye engilakho? Lingangibuza kanjani lisithi, ‘Uhlutshwa yini na?’”
Ya amsa ya ce, “Kun kwashe allolin da na yi, da kuma firist nawa, kuka tafi. Me kuma nake da shi? Yaya za ku ce, ‘Mece ce damuwata?’”
25 AbakoDani baphendula bathi, “Ungaphikisani lathi, hlezi abanye abantu abalolaka bakuhlasele, kuthi wena labendlu yakho lilahlekelwe yikuphila kwenu.”
Mutanen Dan suka ce, “Kada ka kuskura ka ce kome, in ba haka ba mutanen nan za su harzuƙa, da kai da iyalinka duka ku rasa rayukanku.”
26 Ngakho abakoDani bazihambela, kwathi uMikha ebona ukuthi babelamandla kakhulu kulaye, waphenduka wabuyela emzini wakhe.
Saboda haka mutanen Dan suka kama hanyarsu, Mika kuwa da ya ga an fi ƙarfinsa, sai ya juya ya koma gida.
27 Bathatha okwakwenziwe nguMikha, lomphristi wakhe, baya eLayishi, ebantwini ababelokuthula njalo bengethuki lutho. Babahlasela ngenkemba batshisa ledolobho labo.
Sa’an nan suka ɗauko abin da Mika ya yi, da firist nasa, suka tafi Layish, suka fāɗa wa mutanen da suke zaman lafiya, ransu kuma a kwance. Suka fāɗa musu suka kuma ƙone birninsu.
28 Kakho owayengabahlenga ngoba babehlezi khatshana kakhulu leSidoni bengelabuhlobo lamuntu. Idolobho lalisesigodini eduze leBhethi-Rehobhi. AbakoDani balakha kutsha idolobho lelo bahlala kulo.
Ba wanda zai cece su domin suna nesa da Bet-Sidon kuma ba sa hulɗa da kowa. Birnin yana a kwari kusa da Bet-Rekob. Mutanen Dan suka sāke gina birnin suka zauna a can.
29 Balibiza ngokuthi yiDani ibizo likakhokho wabo uDani, owayezalwa ngu-Israyeli, lanxa idolobho lalikade lithiwa yiLayishi.
Suka sa wa birnin suna Dan, wato, sunan kakansu Dan, wanda aka haifa wa Isra’ila, ko da yake a dā ana kira birnin Layish.
30 AbakoDani bazimisela izithombe khona, njalo uJonathani indodana kaGeshomu, indodana kaMosi, lamadodana akhe babengabaphristi besizwana sikaDani kwaze kwaba yisikhathi sokuthunjwa kwelizwe.
A can mutanen Dan suka kafa wa kansu gumaka, Yonatan ɗan Gershom, ɗan Musa, da’ya’yansa maza firistoci ne na kabilar Dan har lokacin da aka kwashe mutane zuwa bauta.
31 Baqhubeka basebenzisa izithombe ezazenziwe nguMikha, ngasosonke isikhathi indlu kaNkulunkulu iseShilo.
Suka ci gaba da amfani da gumakan da Mika ya yi, a duk wannan lokacin gidan Allah yana a Shilo.