< UJobe 22 >
1 U-Elifazi umThemani wasephendula wathi:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 “Umuntu angasiza uNkulunkulu na? Lesihlakaniphi uqobo kambe singamsiza na?
“Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
3 Bekungamupha ntokozo bani uSomandla ukulunga kwakho na? Ubengazuzani ngabe kuthiwa kawulasici na?
Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
4 Yikumesaba kwakho yini akukhuzela khona lakwethesela khona amacala na?
“Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
5 Kabubukhulu ububi bakho na? Lezono zakho angithi kazipheli na?
Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
6 Wawubiza isibambiso kubafowenu kungelasizatho; uhlubula abantu izigqoko zabo basale beze.
Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
7 Abakhatheleyo wawubancitsha amanzi, abalambileyo ungabaphi ukudla,
Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
8 lanxa wena wawuyindoda elamandla, ulepulazi, indoda ehlonitshwayo, uphila kulo.
Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
9 Abafelokazi wabaxotsha ungabaphanga lutho izintandane waziqeda amandla.
Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
10 Kungenxa yalokho usuhanqwe yimijibila, usuhlukuluzwa luhlupho masinyane,
Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
11 yikho kumnyama kangaka ungasaboni, njalo yikho ususibekelwa zimpophoma zamanzi.
An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
12 UNkulunkulu kakho esiqongweni samazulu na? Ake ubone phela ukuthi ziphakeme njani izinkanyezi ezisesiqongweni!
“Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
13 Kodwa wena uthi, ‘UNkulunkulu wazini? Angahlulela phakathi komnyama onje?
Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
14 Usithwe ngamayezi amakhulu, ngakho kasiboni nxa ehambahamba ezulwini eliphezulu.’
Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
15 Wena-ke uzakwalela endleleni endala na eseyahanjwa ngababi?
Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
16 Bedluliswa singakafiki isikhathi sabo, izisekelo zabo zakhukhulwa nguzamcolo.
An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
17 Bathi kuNkulunkulu, ‘Tshiyana lathi! USomandla angasenzani na?’
Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
18 Ikanti kunguye owagcwalisa izindlu zabo ngezinto ezinhle, ngakho kangingeni ezelulekweni zababi.
Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
19 Abalungileyo bayakubona lokho bathokoze; abangelacala bayabahleka bathi,
“Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
20 ‘Ngempela izitha zethu zichithiwe, lokuseleyo kwenotho yazo sekubhuqwe ngumlilo.’
‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
21 Zehlise kuNkulunkulu ukuze uwelelane laye; ngaleyondlela ukuphumelela kuzakuza kuwe.
“Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
22 Yamukela iziqondiso eziphuma emlonyeni wakhe, amazwi akhe uwabeke enhliziyweni yakho.
Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
23 Nxa ubuyela kuSomandla, uzavuselelwa; nxa ususa ububi bube kude lethente lakho
In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
24 lomthuso wakho uwulahlele othulini, igolide lakho lase-Ofiri ulilahlele emadwaleni ezifuleni,
Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
25 lapho-ke uSomandla uzakuba ligolide lakho, lesiliva esikhethekileyo kuwe.
sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
26 Ngempela uzazuza ukuthokoza kuSomandla uphakamisele ubuso bakho kuNkulunkulu.
Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
27 Uzakhuleka kuye, yena akuzwe, njalo uzagcwalisa izifungo zakho.
Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
28 Lokho okumisileyo kuzakwenziwa, lokukhanya kuzazikhanyisa izindlela zakho.
Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
29 Nxa abantu besehliswa ubususithi, ‘Baphakamiseni!’ lapho-ke uzabasiza abahlulukelweyo.
Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
30 Uzabasiza lalabo abonayo, abazakhululwa ngenxa yokubamsulwa kwakho.”
Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”