< UJobe 18 >

1 Kwathi lapho uBhilidadi umShuhi waphendula wathi:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 “Koze kube nini ulokhu uphethe emlonyeni? Nakana andubana sikhulume.
“Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
3 Kungani usithatha njengezinkomo kube ingathi siyizithutha kuwe na?
Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
4 Wena ozidabudabulayo ube yiziqa ngokuthukuthela kwakho, uthi sesingawudela umhlaba ngenxa yakho? Loba uthi amadwala agudlulwe ezindaweni zawo na?
Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
5 Isibane somubi siyacima; ilangabi lomlilo wakhe liyaphela ukubhebha.
“An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
6 Ukukhanya ethenteni lakhe kuyafiphala; isibane esiseceleni kwakhe siyacima.
Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
7 Izisinde zakhe zamandla ziyadeda; lamacebo akhe yiwo amlahla phansi.
Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
8 Inyawo zakhe zimbeka emambuleni acine esemthandele.
Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
9 Umjibila umhwiphula ngesithende; isihitshela simuthi nki.
Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
10 Isihitshela usifihlelwe phansi; umjibila uthukuziwe endleleni yakhe.
An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
11 Uyethuka ngokwesaba inxa zonke kumlandelele langaphi aya khona.
Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
12 Umonakalo umlambele; incithakalo imlindele nxa esiwa.
Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
13 Kudla ingxenye yesikhumba sakhe; izibulo lokufa lidla izitho zakhe.
Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
14 Uyasuswa ekuvikelekeni kwethente lakhe aqhutshwe asiwe enkosini yokwesaba.
An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
15 Umlilo uhlala ethenteni lakhe; isolufa evuthayo ichithachithwe emzini wakhe.
Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
16 Impande zakhe ziyabuna ngaphansi lamagatsha akhe abune ngaphezulu.
Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
17 Ukukhunjulwa kwakhe kuyaphela emhlabeni; kalabizo elizweni.
An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
18 Uyasuswa ekukhanyeni aye ebumnyameni njalo axotshwe emhlabeni.
An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
19 Kalabantwana loba isizukulwane ebantwini bakibo, kakho loyedwa owakhe lapho ake ahlala khona.
Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
20 Abantu bentshonalanga bayanengwa yisiphetho sakhe; abantu bempumalanga bayatshaqeka.
Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
21 Ngempela linjalo ikhaya lomuntu omubi; yiyo indawo yalowo ongamaziyo uNkulunkulu.”
Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”

< UJobe 18 >