< UJobe 14 >

1 “Umuntu ozelwe ngumfazi ulensuku ezilutshwane njalo ezigcwele inhlupho.
“Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
2 Uyaqhakaza njengeluba aphinde abune; njengesithunzi esithi tshazi, akemi.
Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
3 Onjalo ungala ulokhu umkhangele na? Ungamisa phambi kwakho umthonisise na?
Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
4 Ngubani ongaveza okuhlambulukileyo kokungcolileyo na? Kakho!
Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
5 Insuku zomuntu zimisiwe; uzibekile izinyanga zokuphila kwakhe wabeka lemikhawulo angeke ayeqe.
An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
6 Ngakho-ke myekele ungazihluphi ngaye, aze aqede lesosikhathi sakhe njengomuntu oqhatshiweyo.
Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
7 Kungaba lethemba ngesihlahla; singaganyulwa siyahluma njalo, amahlumela aso kawayikwehluleka ukukhula.
“Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
8 Impande zaso zingaguga phansi emhlabathini lesiphunzi saso sife emhlabathini,
Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
9 kodwa singezwa amanzi siyahluma sikhuphe ingatsha njengesihlahla esitsha.
Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
10 Kodwa umuntu uyafa alaliswe phansi; uphefumula okokucina angabe esabakhona.
Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
11 Njengamanzi esitsha olwandle lanjengomfula ucitsha amanzi wome qha,
Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
12 ngokunjalo umuntu ulala phansi angabe esavuka; kuze kutshabalale amazulu abantu kabayikuvuka kumbe baphatshanyiswe ebuthongweni babo.
haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
13 Kube uyangifihla ethuneni ungithukuze ulaka lwakho luze ludlule! Kube ungibekela isikhathi ube usungikhumbula! (Sheol h7585)
“Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
14 Umuntu angafa uphinde aphile na? Zonke insuku zokutshikatshika kwami ngizalindela isikhathi sokuyekelwa kwami.
In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
15 Uzabiza lami ngizasabela; uzasifisa lesosidalwa esenziwa yizandla zakho.
Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
16 Ngeqiniso lapho uzabala izinyathelo zami kodwa kawuyikulandelela izono zami.
Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
17 Iziphambeko zami zizananyekwa emgodleni; uzasigubuzela isono sami.
Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
18 Kodwa njengentaba ikhumuzeka ize ibhidlike, lanjengedwala ligudluka endaweni yalo,
“Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
19 njengamanzi awagubhayo amatshe lezikhukhula zikhukhula umhlabathi, kanjalo uyalibhidliza ithemba lomuntu.
yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
20 Umehlula kanye angaphindi abekhona, adlule; uyabuguqula ubuso bakho umxotshe.
Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
21 Nxa amadodana akhe ezuza udumo, kawakwazi; nxa izizukulwane zakhe zisehliswa, kazikuboni.
Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
22 Bezwa kuphela ubuhlungu bemizimba yabo bazikhalele bona.”
Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”

< UJobe 14 >