< UJeremiya 38 >

1 UShefathiya indodana kaMathani, loGedaliya indodana kaPhashuri, uJewukhali indodana kaShelemiya, loPhashuri indodana kaMalikhija bakuzwa uJeremiya ayekutshela abantu bonke esithi,
Shefatiya ɗan Mattan, Gedaliya ɗan Fashhur, Yukal ɗan Shelemiya da Fashhur ɗan Malkiya ya ji abin da Irmiya yana faɗa wa dukan mutane sa’ad da ya ce,
2 “UThixo uthi: ‘Lowo ozasala kulelidolobho uzabulawa yinkemba, yindlala kumbe yisifo; kodwa lowo ozakuya kumaKhaladiya uzasila. Uzaphunyuka lokuphila kwakhe; uzaphila.’
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba, amma duk wanda ya je wurin Babiloniyawa zai rayu. Zai tsira da ransa, ya rayu.’
3 Njalo uThixo uthi: ‘Idolobho leli lizanikelwa impela ebuthweni lenkosi yaseBhabhiloni ezalithumba.’”
Kuma ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Tabbatacce za a ba da wannan birni ga sojojin sarkin Babilon, wanda zai ci shi.’”
4 Izikhulu zasezisithi enkosini, “Umuntu lo kumele abulawe. Wenza amabutho asala kulelidolobho aphelelwe lithemba, kanye labantu bonke, ngenxa yezinto azitshoyo kubo. Umuntu lo kadingi okuhle kwabantu laba, kodwa ukubhujiswa kwabo.”
Sai fadawa suka ce wa sarki, “Ya kamata a kashe wannan mutum. Yana karya zuciyar sojojin da suka ragu a birnin, da zuciyar sauran mutane, ta wurin abubuwan da yake faɗa musu. Wannan mutum ba ya neman jin daɗin zaman wannan sai dai wahala.”
5 UZedekhiya inkosi waphendula wathi, “Usezandleni zenu. Inkosi ingeke yenze lutho ukuba iliphikise.”
“Yana a hannuwanku” Sarki Zedekiya ya amsa. “Sarki ba zai iya yin kome ya hana ku ba.”
6 Ngakho bamthatha uJeremiya bamfaka emgodini kaMalikhija, indodana yenkosi, owawusegumeni labalindi. UJeremiya bamehlisela phansi phakathi komgodi ngemichilo; wawungelamanzi, kuludaka kuphela, ngakho uJeremiya watshona edakeni.
Saboda haka suka kama Irmiya suka sa a rijiyar da ba ruwa a ciki ta Malkiya, ɗan sarki, wadda take a sansanin matsara. Suka saukar da Irmiya cikin rijiyar da ba ruwa da igiya; babu ruwa a cikinta, sai laka, Irmiya ya nutse cikin laka.
7 Kodwa u-Ebhedi-Meleki, umKhushi, isikhulu endlini yobukhosi, wezwa ukuthi basebefake uJeremiya emgodini. Kwathi-ke inkosi ihlezi eSangweni lakoBhenjamini,
Amma Ebed-Melek mutumin Kush, wani hafsa a fada, ya ji cewa sun sa Irmiya a rijiyar da ba ruwa. Yayinda sarki yana zama a Ƙofar Benyamin,
8 u-Ebhedi-Meleki waphuma esigodlweni wathi kuyo,
Ebed-Melek ya fita daga fadar ya ce masa,
9 “Nkosi yami lombusi wami, abantu laba benze ububi kukho konke abakwenze kuJeremiya umphrofethi. Sebemphosele emgodini lapho azalamba khona aze afe kungaselakudla edolobheni.”
“Ranka yă daɗe sarki, waɗannan mutane sun yi mugun abu a duk abin da suka yi wa Irmiya annabi. Sun jefa shi cikin rijiyar da ba ruwa, inda zai mutu da yunwa gama ba sauran wani burodi a birnin.”
10 Ngakho inkosi yalaya u-Ebhedi-Meleki umKhushi yathi, “Thatha amadoda angamatshumi amathathu lapha likhuphe uJeremiya umphrofethi emgodini engakafi.”
Sai sarki ya umarce Ebed-Melek mutumin Kush, “Ka ɗauko mutane talatin daga nan ku fid da Irmiya annabi daga rijiyar kafin ya mutu.”
11 Ngakho u-Ebhedi-Meleki wathatha amadoda lawo waya lawo endlini engaphansi kwendlu yengcebo esigodlweni. Wathatha amanikiniki amadala lezigqoko ezigugileyo khonapho wakwehlisela phansi kuJeremiya emgodini ngemichilo.
Saboda haka Ebed-Melek ya ɗauki mutane tare da shi suka shiga ɗaki a ƙarƙashin baitulmali a cikin fada. Ya ɗauko waɗansu tsofaffin tsummoki da tsofaffi riguna daga can ya kuma zurara su da igiya wa Irmiya a cikin rijiyar.
12 U-Ebhedi-Meleki umKhushi wathi kuJeremiya, “Faka amanikiniki la amadala lezigqoko lezi ezigugileyo emakhwapheni akho ukuze imichilo ingakulimazi.” UJeremiya wenza njalo,
Ebed-Melek mutumin Kush ya ce wa Irmiya, “Ka sa waɗannan tsummoki da tsofaffin rigunan a hammatarka, ya zarga igiya.” Irmiya ya yi haka,
13 basebemdonsela phezulu ngemichilo, bamkhupha emgodini. UJeremiya wahlala egumeni labalindi.
suka kuma ja shi sama da igiya suka fid da shi daga rijiyar. Irmiya kuwa ya zauna a sansanin matsara.
14 Inkosi uZedekhiya wabiza uJeremiya umphrofethi wasiwa entubeni yesithathu yethempeli likaThixo. Inkosi yasisithi kuJeremiya, “Ngizakubuza okuthize. Ungangifihleli lutho.”
Sai Sarki Zedekiya ya aika a kawo Irmiya annabi, ya sa aka kawo shi a ƙofa ta uku ta haikalin Ubangiji. Sai sarki ya ce wa Irmiya, “Zan tambaye ka wani abu, kada ka ɓoye mini wani abu.”
15 UJeremiya wathi kuZedekhiya, “Ngingakuphendula kawuyikungibulala na? Loba ngingakweluleka, kawuyikungilalela.”
Irmiya ya ce wa Zedekiya, “In na ba ka amsa, ba za ka kashe ni ba? Ko da na ba ka shawara, ba za ka saurare ni ba.”
16 Kodwa inkosi uZedekhiya wafunga isifungo lesi ngasese kuJeremiya, wathi, “Ngeqiniso elinjengoba uThixo ekhona, yena owasinika ukuphefumula, angiyikukubulala loba ngikunikele kulabo abafuna ukukubulala.”
Amma Sarki Zedekiya ya yi wannan rantsuwa a kaɗaice ga Irmiya cewa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya ba mu numfashi, ba zan kashe ka ko in ba da kai ga waɗanda suke neman ranka ba.”
17 Lapho-ke uJeremiya wathi kuZedekhiya, “UThixo uNkulunkulu uSomandla, uNkulunkulu ka-Israyeli, uthi: ‘Ungazinikela ezikhulwini zenkosi yaseBhabhiloni, impilo yakho izaphepha njalo ledolobho leli kaliyikutshiswa ngomlilo; wena labendlu yakho lizasila.
Sa’an nan Irmiya ya ce wa Zedekiya, “Ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon, za a bar ka da rai ba za a kuma ƙone wannan birni ba; da kai da iyalinka za ku rayu.
18 Kodwa nxa ungazinikeli ezikhulwini zenkosi yaseBhabhiloni, idolobho leli lizanikelwa kumaKhaladiya azalitshisa ngomlilo; njalo wena uqobo kawuyikuphunyuka ezandleni zawo.’”
Amma in ba ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon ba, za a ba da wannan birni ga Babiloniyawa za su kuma cinna mata wuta; kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba.’”
19 INkosi uZedekhiya wasesithi kuJeremiya, “Ngiyabesaba abakoJuda asebe kumaKhaladiya, ngoba amaKhaladiya anganginikela kubo bangiphathe kubi.”
Sarki Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Ina jin tsoron Yahudawan da suka tafi wurin Babiloniyawa, gama Babiloniyawa mai yiwuwa su ba da ni gare su su kuma wulaƙanta ni.”
20 UJeremiya wathi, “Kabayikukunikela. Lalela uThixo ngokwenza lokhu engikutshela khona. Lapho-ke kuzakulungela, njalo lempilo yakho izaphepha.
Irmiya ya ce, “Ba za su ba da kai ba, ka yi biyayya ga Ubangiji ta wurin yin abin da na faɗa maka. Ta haka zai zama maka da amfani, za ka kuwa rayu.
21 Kodwa ungala ukuzinikela, nanku okuvezwe nguThixo kimi:
Amma in ka ƙi miƙa wuya, ga abin da Ubangiji ya bayyana mini.
22 Bonke abesifazane abasele endlini yobukhosi yenkosi yakoJuda bazakhutshelwa phandle ezikhulwini zenkosi yaseBhabhiloni bathi kuwe: ‘Bakukhohlisile bakwehlula abangane bakho abathenjiweyo. Inyawo zakho zitshonile edakeni; abangane bakho bakudelile.’
Za a fitar da dukan matan da suka ragu a fadan sarkin Yahuda wa hafsoshin sarkin Babilon. Waɗannan mata za su ce maka, “‘Sun ruɗe ka suka kuma rinjaye ka, waɗannan abokanka. Ƙafafunka sun nutse a cikin laka; abokanka sun yashe ka.’
23 Abafazi bakho kanye labantwana bazakhutshelwa phandle kumaKhaladiya. Lawe uqobo kawuyikuphunyuka ezandleni zawo, kodwa uzathunjwa yinkosi yaseBhabhiloni; njalo idolobho leli lizatshiswa ngomlilo.”
“Za a kawo dukan matanka da’ya’yanka wa Babiloniyawa. Kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba amma za su sa sarkin Babilon zai kama ka; za a kuma ƙone wannan birni.”
24 UZedekhiya wasesithi kuJeremiya, “Akungabi lomuntu omazisa inkulumo le, hlezi ufe.
Sai Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Kada ka bar wani ya san wannan zance, in ba haka ba za ka mutu.
25 Izikhulu zingezwa ukuthi ngike ngakhuluma lawe, besezisiza kuwe zithi, ‘Sitshele lokho okutshiloyo enkosini kanye lokutshiwo yinkosi kuwe; ungasifihleli funa sikubulale,’
In fadawa suka ji cewa na yi magana da kai, suka kuma zo wurinka suka ce, ‘Faɗa mana abin da ka faɗa wa sarki da kuma abin da sarki ya faɗa maka; kada ka ɓoye mana, in ba haka za mu kashe ka,’
26 wena zitshele uthi, ‘Kade ngincenga inkosi ukuthi ingangibuyiseli endlini kaJonathani ukuyafela khona.’”
sai ka ce musu cewa, ‘Na roƙi sarki kada yă mai da ni gidan Yonatan in mutu a can.’”
27 Lakanye izikhulu zonke zaya kuJeremiya zambuza, yena wazitshela konke inkosi eyayimlaye ukuthi akutsho. Ngakho kazisatshongo lutho kuye futhi, ngoba kakho owayeyizwile inkulumo yakhe lenkosi.
Dukan fadawa kuwa suka zo wurin Irmiya suka tambaye shi, ya kuma faɗa musu dukan abin da sarki ya umarce shi ya faɗa. Saboda haka ba su ƙara ce masa kome ba, gama ba wanda ya ji zance da suka yi da sarki.
28 UJeremiya wahlala egumeni labalindi kwaze kwaba lusuku lokuthunjwa kweJerusalema. IJerusalema lathunjwa kanje:
Irmiya kuwa ya zauna a sansanin masu gadi har ranar da aka ci Urushalima da yaƙi. Ga yadda aka ci Urushalima,

< UJeremiya 38 >