< U-Isaya 33 >

1 Maye kuwe, wena mchithi, wena ongachithwanga! Maye kuwe, wena mthengisi, wena ongacetshwanga! Lapho uyekela ukuthengisa, lawe uzacetshwa.
Kaitonka, ya kai mai hallakarwa, kai da ba a hallakar da kai ba! Kaitonka, ya maciya amana, kai da ba a ci amanarka ba! Sa’ad da ka daina hallakarwa, za a hallaka ka; sa’ad da ka daina cin amana, za a ci amanarka.
2 Awu Thixo, woba lomusa kithi; siyakulangazelela. Woba ngamandla ethu ekuseni konke, ube yinsindiso yethu esikhathini sosizi.
Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai; muna marmarinka. Ka zama ƙarfinmu kowace safiya, cetonmu a lokacin damuwa.
3 Ekukhwazeni kwelizwi lakho, izizwe ziyabaleka; lapho uphakama izizwe ziyahlakazeka.
Da tsawar muryarka, mutane za su gudu; sa’ad da ka tashi, al’ummai za su watse.
4 Elakuthumbayo, lina zizwe, kubuthwa sengangathi kuqoqwa yisikhongwane, abantu beqela kukho njengomtshitshi wentethe.
Ganimarku, ya al’ummai ƙanana fāri sun girbe; kamar tarin fārin da mutane sun fāɗa wa.
5 UThixo uphakeme ngoba uhlala phezulu, uzagcwalisa iZiyoni ngokufaneleyo langokulunga.
Ubangiji da girma yake, gama yana zaune a bisa; zai cika Sihiyona cikin gaskiya da adalci.
6 Uzakuba yisisekelo esithembekileyo sesikhathi senu, isiphala esigcwele usindiso, ukuhlakanipha lokwazi; ukumesaba uThixo kuyisiqokoqela sokuzuza ingcebo le.
Zai zama tabbataccen harsashi na koyaushe, ma’ajin ceto da hikima da sani a yalwace; tsoron Ubangiji shi ne mabuɗin wannan dukiya.
7 Khangelani, amaqhawe akibo ahlaba umkhosi emigwaqweni! Izithunywa zokuthula ziyakhala kakhulu.
Duba, jarumawansu suna kuka da ƙarfi a tituna; jakadun salama suna kuka mai zafi.
8 Imigwaqo emikhulu ibetha umoya, akulazihambi kuyo. Isivumelwano sephulwe, ofakazi baso beyisiwe, kakho ohlonitshwayo.
An gudu an bar manyan hanyoyi, babu matafiye a kan hanyoyi. Aka keta yarjejjeniya, an rena shaidunsa ba a kuwa ganin girman kowa.
9 Ilizwe liyalila njalo liyachitheka. ILebhanoni iyangekile njalo iyabuna; iSharoni injengenkangala, iBhashani leKhameli akhithizwa amahlamvu awo.
Ƙasa tana kuka an kuma gudu an bar ta, Lebanon ta sha kunya ta kuma yanƙwane; Sharon ta zama kamar Araba, Bashan da Karmel sun kakkaɓe ganyayensu.
10 UThixo uthi, “Khathesi sengizavuka, khathesi sengizadunyiswa, khathesi sengizaphakanyiswa.
“Yanzu zan tashi,” in ji Ubangiji. “Yanzu ne za a ɗaukaka ni; yanzu za a ɗaga ni sama.
11 Liqukethe ngamakhoba, lizale izibi; umoya wenu eliwuphefumulayo ungumlilo oliqedayo.
Kun yi cikin yayi, kuka haifi kara; numfashinku wuta ne da zai cinye ku.
12 Abantu bazatshiswa bafane lekalaga; bazathungelwa ngomlilo njengamahlahla ameva aganyuliweyo.”
Za a ƙone mutane kamar da ƙuna farar ƙasa; kamar ƙayayyuwan da aka sare aka kuma sa musu wuta.”
13 Lina elikhatshana, zwanini engikwenzileyo; lina abaseduze, vumani amandla ami!
Ku da kuke da nesa, ku ji abin da na yi; ku da kuke kusa, ku san ikona!
14 Izoni zaseZiyoni ziyathuthumela; abangamesabiyo uNkulunkulu bayaqhaqhazela: “Ngubani owakithi ongahlala lomlilo oqothulayo na? Ngubani owakithi ongahlala lokutshisa okungapheliyo na?”
Masu zunubi a Sihiyona sun firgita; rawar jiki ya kama marasa sanin Allah suna cewa, “Wane ne a cikinmu zai iya zama da wuta mai ci? Wane ne a cikinmu zai iya zama da madawwamiyar ƙonewa?”
15 Ngulowo owenza okulungileyo, ekhuluma okuqotho oyalayo inzuzo yokuncindezelwa, ale ukwamukela isivalamlomo, owalayo ukulalela amaqhinga okubulala, avale amehlo akhe ukuze angaboni okubi,
Shi da yake tafiya cikin adalci yana kuma magana abin da yake daidai, wanda yake ƙin riba daga cuta yana kuma kiyaye hannunsa daga karɓan cin hanci, wanda yake hana kunnuwansa daga ƙulla kisa ya kuma rufe idanunsa a kan tunanin aikata mugunta,
16 lo nguye umuntu ozahlala ekuphakameni, osiphephelo sakhe sizakuba yinqaba yasentabeni. Uzalethelwa isinkwa sakhe, lamanzi kayikuwaswela.
shi ne mutumin da zai zauna a bisa, wanda mafakarsa za tă zama kagarar dutse. Za a tanada abincinsa, kuma ruwa ba zai kāsa masa ba.
17 Amehlo enu azayibona inkosi ebuhleni bayo, abuke lelizwe elibanzi.
Idanunku za su ga sarki a cikin kyansa ku kuma hangi ƙasar da take shimfiɗe can da nisa.
18 Ezingqondweni zenu lizakhumbula ukwesaba kwakuqala lithi: “Ingaphi induna yezikhulu leyana? Ungaphi owayethatha imali yemithelo? Singaphi isikhulu esigcina imiphotshongo na?”
Cikin tunaninku za ku yi tunani firgitar da ta faru tun dā kuna cewa, “Ina hafsan nan? Ina wannan wanda yake karɓar haraji? Ina hafsan da yake lura da hasumiyoyi?”
19 Abantu labayana abaklolodayo kalisayikubabona futhi, abantu labayana abolimi olungazwakaliyo, abolimi olungaziwayo, olungaqondakaliyo.
Ba za ku ƙara ganin waɗannan mutane masu girman kai kuma ba, waɗannan mutane masu magana da harshen da ba ku fahimta ba.
20 Khangelani iZiyoni, idolobho lemikhosi yethu; amehlo enu azabona iJerusalema indawo yokuhlala elokuthula, ithente elingeke lisuswe; izikhonkwane zalo kaziyikusitshunwa lezintambo zalo kaziyikuqamuka.
Ku duba Sihiyona, birnin shagulgulanmu; idanunku za su ga Urushalima, mazauni mai lafiya, tentin da ba za a taɓa gusar ba; wanda ba a taɓa tumɓuke turakunsa ba, ko a tsinke igiyoyinta.
21 Khonapho uThixo uzakuba ngolaMandla wethu. Kuzafana lendawo elemifula ebanzi kanye lezifula. Akukho mkhumbi wempi ozagwedlwa khona, akukho mkhumbi olamandla ozahamba khona.
A can Ubangiji zai zama Mai Iko Duka namu. Zai zama kamar inda manyan koguna da rafuffuka suke. Matuƙan jirgin ruwa ba za su kai wurinsu ba, manyan jiragen ruwa ba za su yi zirga-zirga a kansu ba.
22 Ngoba uThixo ungumahluleli wethu, uThixo usinika imithetho, uThixo yinkosi yethu; nguye ozasikhulula.
Gama Ubangiji ne alƙalinmu, Ubangiji ne mai ba mu dokoki, Ubangiji ne sarkinmu; shi ne wanda zai cece mu.
23 Izintambo zakho zeseyili ziyaxega. Insika kayiqiniswanga; iseyili kayivulekanga. Lapho-ke impango enengi izakwabiwa kuthi labaqhulayo labo bazazuza impango.
Maɗaurinku sun kunce ƙarfafan itacen jirgin ba su da kāriya, fikafikan jirgin ba su buɗu ba. Ta haka za a raba yalwar ganima har ma guragu za su kwashe ganimar.
24 Akulamuntu ohlala eZiyoni ozakuthi, “Mina ngiyagula”; labantu abahlala khona bazathethelelwa izono zabo.
Ba wani mazauna a Sihiyona da zai ce, “Ina ciwo”; za a kuma gafarta zunuban waɗanda suke zama a can.

< U-Isaya 33 >