< U-Isaya 2 >

1 Lokhu yikho okwabonwa ngu-Isaya indodana ka-Amozi mayelana loJuda leJerusalema:
Ga abin da Ishaya ɗan Amoz ya gani game da Yahuda da Urushalima.
2 Ngezinsuku zokucina intaba yethempeli likaThixo izamiswa njengenhloko phakathi kwezintaba; izaphakanyiselwa phezu kwezintaba njalo izizwe zonke zizabekelela zisiya kuyo.
A kwanaki masu zuwa za a kafa dutsen haikalin Ubangiji a matsayin babba cikin duwatsu; za a daga shi bisa tuddai, kuma dukan al’ummai za su bumbunto zuwa gare shi.
3 Abantu abanengi bazakuza bathi, “Wozani siye phezu kwentaba kaThixo, siye ethempelini likaNkulunkulu kaJakhobe. Uzasifundisa izindlela zakhe, ukuze sihambe emikhondweni yakhe.” Umthetho uzavela eZiyoni, ilizwi likaThixo livele eJerusalema.
Mutane da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, domin mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Dokar za tă fito daga Sihiyona, maganar Ubangiji daga Urushalima.
4 Uzakwahlulela phakathi kwezizwe, alamule ingxabano zabantu abanengi. Bazakhanda izinkemba zabo zibe yimihlathi yamakhuba, lemikhonto yabo ibe ngamahloka okuthena izihlahla. Isizwe asiyikuhlomela isizwe ngenkemba loba sifundele ukulwa impi futhi.
Zai shari’anta tsakanin al’ummai zai kuma sulhunta faɗar mutane masu yawa. Za su mai da takubansu su zama garemani māsunsu su zama wuƙaƙen askin itatuwa. Al’umma ba za tă ƙara ɗauki takobi a kan al’umma ba, ba kuwa za su ƙara yin horarwar yaƙi.
5 Woza, ndlu kaJakhobe, kasihambe ekukhanyeni kukaThixo.
Ki zo, ya gidan Yaƙub, bari mu yi tafiya a hasken Ubangiji.
6 Wena, Thixo, usubalahlile abantu bakho, isizukulwane sikaJakhobe. Bagcwele ukholo oluyize lwaseMpumalanga benza lemisebenzi yobungoma njengamaFilisti, njalo babambana izandla labangakholwayo.
Ka rabu da mutanenka, gidan Yaƙub. Sun cika da ayyukan sihiri da aka kawo daga Gabas; suna yin duba kamar Filistiyawa suna tafa hannuwa tare da marasa sanin Allah.
7 Ilizwe labo ligcwele isiliva legolide; inotho yabo ayilakuphela. Ilizwe labo ligcwele amabhiza; izinqola zabo zempi kazipheli.
Ƙasarsu ta cika da azurfa da zinariya; dukiyarsu kuma ba iyaka. Ƙasarsu ta cika da dawakai; kekunan yaƙinsu kuma ba iyaka.
8 Ilizwe labo ligcwele izithombe; bakhothamela umsebenzi wezandla zabo, lakulokho okwenziwa yiminwe yabo.
Ƙasarsu ta cika da gumaka; sukan rusuna ga aikin hannuwansu, ga abin da yatsotsinsu suka yi.
9 Ngakho abantu bazakwehliselwa phansi bonke bazehliswa ungabathetheleli.
Saboda an jawo mutum ƙasa aka kuma ƙasƙantar da ɗan adam, kada ku gafarta musu.
10 Ngenani ezimbalwini zamatshe lasemhlabathini, licatshele ukwesabeka kukaThixo lenkazimulo yobukhosi bakhe!
Ku tafi cikin duwatsu, ku ɓuya cikin ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa!
11 Amehlo omuntu oziphakamisayo azathotshiswa, lokuziphakamisa kwabantu kwehliselwe phansi; uThixo kuphela nguye ozaphakanyiswa ngalolosuku.
Za a ƙasƙantar da mai girman kai za a kuma lalatar da fariyar masu ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana.
12 UThixo uSomandla ulosuku alubekele bonke abazazigqajayo labazikhukhumezayo; lakho konke okuphakemeyo (kuzathotshiswa),
Ubangiji Maɗaukaki yana da rana ajiye domin dukan masu girman kai da masu fariya domin dukan waɗanda aka ɗaukaka (zai kuwa ƙasƙantar da su),
13 olwazo zonke izihlahla zemisedari zaseLebhanoni ezinde leziphakemeyo, lazozonke izihlahla zomʼOkhi zaseBhashani,
domin dukan al’ul na Lebanon, masu tsayi da masu fariya, da kuma dukan itatuwan oak na Bashan,
14 olwazo zonke izintaba ezindekazi lamaqaqa wonke aphakemeyo,
domin dukan dogayen duwatsu da kuma tuddai masu tsayi,
15 olwayo yonke imiphotshongo ephakemeyo layo yonke imiduli eyinqaba,
domin kowace doguwar hasumiya da kowace katanga mai ƙarfi,
16 olwemikhumbi yonke yaseThashishi layo yonke imikolo emihle.
domin kowane jirgin ruwan kasuwanci da kuma jirgi mafi girma mafi kyau.
17 Ukuziphakamisa kwabantu kuzakwehliselwa phansi, ukuzazisa kwabantu kuthobekiswe; uThixo kuphela nguye ozadunyiswa ngalolosuku,
Za a jawo mai girman kai ƙasa a kuma ƙasƙantar da mai ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana,
18 izithombe zizanyamalala zithi nya.
za a kuma kawar da gumaka ƙaƙaf.
19 Abantu bazabalekela ezimbalwini zamatshe lasemilindini emhlabathini bebalekela ukwesabeka kukaThixo lenkazimulo yobukhosi bakhe lapho ephakama ukuba anyikinye umhlaba.
Mutane za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
20 Ngalolosuku abantu bazazilahlela emvukuzaneni lakubomalulwane izithombe zabo zesiliva lezegolide abazenzela ukuba bazikhonze.
A wannan rana mutane za su zubar wa jaba da jamage gumakansu na azurfa da gumakansu na zinariya da suka yi don su bauta musu.
21 Bazabalekela ezimbalwini zamatshe lasezingoxweni zamawa bebalekela ukwesabeka kukaThixo lenkazimulo yobukhosi bakhe, lapho ephakama ukuba anyikinye umhlaba.
Za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma zuwa tsagaggun duwatsu daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
22 Yekelani ukwethemba umuntu olomphefumulo nje kuphela emakhaleni akhe. Ngoba uyini yena na?
Ku daina dogara ga mutum, wanda numfashi ne kawai yake da shi a hancinsa. Wace daraja gare shi?

< U-Isaya 2 >