< U-Isaya 14 >
1 UThixo uzakuba lesihawu kuJakhobe; uzamkhetha njalo u-Israyeli, abahlalise elizweni labo. Abezizwe bazahlangana labo bamanyane lendlu kaJakhobe.
Ubangiji zai yi wa Yaƙub jinƙai; zai sāke zaɓi Isra’ila yă kuma zaunar da su a ƙasarsu. Baƙi ma za su zo su zauna tare da su su haɗa kai da gidan Yaƙub.
2 Izizwe zizabathatha zibase endaweni yabo. Indlu ka-Israyeli izathumba izizwe zibe yizisebenzi zesilisa lezesifazane elizweni likaThixo. Bazakwenza abathumbi babo babe yizigqili, babuse abancindezeli babo.
Al’ummai za su ɗauke su su kuma kawo wurin da yake nasu. Gidan Isra’ila kuwa za tă mallaki al’ummai a matsayin bayi maza da mata a ƙasar Ubangiji. Za su mai da waɗanda suka kama su su zama kamammu su kuma yi mulki a kan waɗanda suka taɓa danne su.
3 Ngosuku uThixo azaliphumuza ngalo ekuhluphekeni, ekutshikatshikeni, lasebugqilini obulesihluku,
A ranar da Ubangiji ya hutashe ku daga wahala da azaba da muguwar bauta,
4 lizakutsho la amazwi okukloloda enkosini yaseBhabhiloni lithi: Umncindezeli usefikile ekucineni, ukuthukuthela kwakhe sekuphelile!
za ku yi wa sarkin Babilon wannan ba’a. Mai danniya ya zo ga ƙarshe! Dubi yadda fushinsa ya ƙare!
5 UThixo useyephule intonga yababi, induku yobukhosi eyababusi,
Ubangiji ya karye sandar mugaye, sandan mulkin masu mulki,
6 abatshaya abantu ngokuthukuthela, langokugalela okungapheliyo, banqoba izizwe ngentukuthelo langokuncindezela okungapheliyo.
wanda cikin fushi ya kashe mutane da bugu marar ƙarewa, kuma cikin fushi ya mamaye al’ummai da fushi ba ƙaƙƙautawa.
7 Amazwe wonke alokuphumula lokuthula; aphahluka ahlabelele izingoma.
Dukan ƙasashe suna hutawa suna kuma cikin salama; sun ɓarke da waƙa.
8 Lezihlahla zamaphayini lemisedari yaseLebhanoni ziyathokoza ngawe zithi, “Njengoba khathesi usuwiselwe phansi akula ozakuzasigamula.”
Har itatuwan fir ma da kuma al’ul na Lebanon suna murna a kanka suna cewa, “Yanzu da aka ƙasƙantar da kai, babu wani mai yankan katakon da ya zo yă yanka mu.”
9 Ithuna ngaphansi liyanyakaza ukuba likuhlangabeze ekufikeni kwakho. Livusa imimoya yabafayo ukuba ikubingelele, bonke labo ababengababusi emhlabeni; libenza basukume ezihlalweni zabo zobukhosi, bonke labo ababengamakhosi ezizwe. (Sheol )
Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya don yă sadu da kai a zuwanka; yana tā da ruhohin da suka rasu don su gaishe ka, dukan waɗanda sun taɓa zama shugabanni a duniya; ya sa suka tashi daga kujerun sarauta, dukan waɗanda suke sarakuna a kan al’ummai. (Sheol )
10 Bazaphendula bonke, bazakuthi kuwe, “Lawe usubuthakathaka njengathi, usube njengathi.”
Duk za su amsa, za su ce maka, “Ashe kai ma raunana ne, kamar mu; ka zama kamar mu.”
11 Bonke ubukhosi bakho sebehliselwe phansi ethuneni, kanye lomsindo wamachacho akho. Impethu zendlaliwe ngaphansi kwakho, inhlavane zikwembesile. (Sheol )
An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari, tare da surutan garayunka; tsutsotsi sun bazu a ƙarƙashinka tsutsotsi kuma suka rufe ka. (Sheol )
12 Yeka ukuwa kwakho uvela ezulwini, wena nkanyezi yekuseni, ndodana yokusa! Uphoselwe phansi emhlabeni, wena owake wehlisela izizwe phansi!
Yaya aka yi ka fāɗo daga sama Ya tauraron safiya, ɗan hasken asuba! An fyaɗa ka da ƙasa, kai da ka taɓa ƙasƙantar da al’ummai!
13 Wathi enhliziyweni yakho, “Ngizakwenyukela ezulwini, ngizaphakamisela isihlalo sami sobukhosi ngaphezu kwezinkanyezi zikaNkulunkulu; ngizahlala ebukhosini phezu kwentaba yombuthano, ezingqongweni zentaba engcwele.
Ka yi tunani a ranka ka ce, “Zan hau zuwa sama; zan ɗaga kursiyina sama da taurarin Allah; zan zauna a kursiyi a kan dutsen taro, a can ƙurewar saman dutse mai tsarki.
14 Ngizakwenyukela phezu kwezindawo eziphakemeyo emayezini; ngizazenza ngibe njengoPhezukonke.”
Zan haura can bisa gizagizai; zan mai da kaina kamar Mafi Ɗaukaka.”
15 Kodwa ulethwe phansi ethuneni, ekuzikeni kwegodi. (Sheol )
Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari, zuwa zurfafan rami. (Sheol )
16 Labo abakubonayo bakudonsela amehlo, bayacabanga ngowakudalelwayo bathi: “Nguye lo na umuntu owanyikinya umhlaba wenza imibuso yaqhaqhazela,
Waɗanda suka gan ka sun zura maka ido, suna tunani abin da zai same ka. “Wannan mutumin ne ya girgiza duniya ya kuma sa mulkoki suka razana,
17 umuntu owenza umhlaba waba lugwadule, owadiliza amadolobho awo, kazavumela abathunjwayo bakhe ukubuyela ekhaya na?”
mutumin da ya mai da duniya ta zama hamada, wanda ya tumɓuke biranenta bai kuma bar kamammunsa suka tafi ba?”
18 Wonke amakhosi ezizwe alele ebukhosini, enye lenye ethuneni layo.
Dukan sarakunan duniya suna kwance a mace, kowa a kabarinsa.
19 Kodwa wena uphoselwe ngaphandle kwethuna lakho njengogatsha olulahliweyo; welekwe ngababulawayo, lalabo abagwazwa ngenkemba, labo abehlela ematsheni egodi. Njengesidumbu esinyathelwe ngezinyawo,
Amma an jefar da kabarinka kamar reshen da aka ƙi; an rufe ka da waɗanda aka kashe, tare da waɗanda aka soke da takobi, waɗanda suka gangara zuwa duwatsun rami. Kamar gawar da aka tattake da ƙafa,
20 kawuyikuhlangana labo ekungcwatshweni; ngoba usulichithile ilizwe lakho wabulala labantu bakini. Inzalo yababi kakungakhulunywa ngayo futhi.
ba za a haɗa ka tare da su a jana’iza ba, gama ka hallaka ƙasarka ka kuma kashe mutanenka. Ba za a ƙara ambaci zuriyarka masu aikata mugunta ba.
21 Lungisa indawo yokubulalela abantwabakhe ngenxa yezono zabokhokho babo. Kabamelanga bavuke ukuba bathathe ilizwe bagcwalise umhlaba ngamadolobho abo.
A shirya wuri don a yayyanka’ya’yansa maza saboda zunuban kakanninsu; kada a reno su su gāji ƙasar su cika duniya da biranensu.
22 “Ngizabavukela,” kutsho uThixo uSomandla. “Ngizakwesula iBhabhiloni labasindayo abantwabakhe lezizukulwane,” kutsho uThixo.
“Zan yi gāba da su,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kau da sunan Babilon da waɗanda suka rage da rai a cikinta,’ya’yanta da zuriyarta,” in ji Ubangiji.
23 “Ngizalenza libe yindawo yezikhova lelizwe elilixhaphozi. Ngizalithanyela ngomthanyelo wencithakalo,” kutsho uThixo uSomandla.
“Zan mai da ita wuri domin mujiyoyi da kuma fadama; zan share ta da tsintsiyar hallaka,” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
24 UThixo uSomandla ufungile wathi, “Ngeqiniso, njengoba sengilungisile, kuzakuba njalo, njalo njengoba ngikumisile kuzakuma kanjalo.
Ubangiji Maɗaukaki ya rantse, “Tabbatacce, kamar yadda na riga na shirya, haka zai kasance, kuma kamar yadda na nufa, haka zai zama.
25 Ngizamchoboza umʼAsiriya elizweni lami; ezintabeni zami ngizamnyathelela phansi. Ijogwe lakhe lizasuswa ebantwini bami, umthwalo wakhe ususwe emahlombe abo.”
Zan ragargazar da Assuriya a cikin ƙasata; a kan duwatsuna zan tattake shi. Za a ɗauke nauyin da ya sa wa mutanena, a kuma ɗauke nauyinsa daga kafaɗunsu.”
26 Lokhu yikho okumiselwe umhlaba wonke, lesi yisandla eselulelwe phezu kwezizwe zonke.
Wannan shi ne shirin da na yi domin dukan duniya; wannan shi ne hannun da aka miƙa a bisa dukan al’ummai ke nan.
27 Ngoba uThixo uSomandla usenze isimiso, ngubani ongamvimbela na? Isandla sakhe siphakanyisiwe, ngubani ongasibuyisela emuva na?
Gama Ubangiji Maɗaukaki ya ƙudura ya yi wannan, wa kuwa zai hana shi? Ya riga ya miƙa hannunsa, wa zai komar da shi?
28 Ilizwi leli lafika nyakana kusifa inkosi u-Ahazi:
Wannan abin da Allah ya yi magana ya zo ne a shekarar da Sarki Ahaz ya mutu.
29 Lingathokozi, lonke lina maFilistiya, lisithi intonga eyalitshayayo yephukile; ngoba empandeni yenyoka leyana kuzavela inhlangwana, inzalo yayo izakuba yinyoka elobuthi obutshokayo.
Kada ku yi farin ciki, dukanku Filistiyawa, cewa sandar da ta buge ku ta karye; daga saiwar wannan maciji wani mugun maciji mai dafi zai taso,’ya’yansa za su zama wani maciji masu dafi mai tashi sama.
30 Abangabayanga kubayanga bazathola amadlelo, abaswelayo bazalala phansi bevikelekile. Kodwa impande yakho ngizayitshabalalisa ngendlala; izabulala abaseleyo bakho.
Mafi talauci na matalauta zai sami wurin kiwo, mabukata kuma za su kwana lafiya. Amma zan hallakar da saiwarka da matsananciyar yunwa; za tă kashe naka da suka rage da rai.
31 Lila wena sango! Bubula wena dolobho! Chithekani lonke lina maFilistiya! Iyezi lentuthu livela enyakatho; njalo akulamatshida eviyweni lalo.
Ki yi ihu, ya ke ƙofa! Yi kururuwa, ya ke birni! Ku razana, dukanku Filistiyawa! Ƙunshin hayaƙi yana tasowa daga arewa, kuma babu matsorata a cikin sojojinsa.
32 Yimpendulo bani ezanikwa izithunywa zalesosizwe na? “UThixo useyakhile iZiyoni, abantu bakhe abahluphekileyo bazaphephela kuye.”
Wace amsa ce za a bayar wa jakadun wannan al’umma? “Ubangiji ya kafa Sihiyona, kuma a cikinta mutanensa masu shan azaba za su sami mafaka.”