< UHoseya 4 >
1 Zwanini ilizwi likaThixo, lina bako-Israyeli ngoba kulecala uThixo alethesa lina elihlala elizweni: “Akulakwethembeka, akulathando, akukho ukumamukela uNkulunkulu elizweni.
Ku ji maganar Ubangiji, ku Isra’ilawa, gama Ubangiji yana da tuhumar da zai kawo a kan ku waɗanda suke zama a ƙasar. “Babu aminci, babu ƙauna, babu yarda da Allah a cikin ƙasar.
2 Kulokuthuka kuphela, lokuqamba amanga lokubulala, lokuntshontsha kanye lobufebe; benza ububi bonke, njalo ukuchithwa kwegazi kulandela ukuchithwa kwegazi.
Akwai la’ana ce kawai, yin ƙarya da kisa, yin sata da zina; sun wuce gona da iri, kisankai a kan kisankai.
3 Ilizwe liyalila ngenxa yalokhu, njalo bonke abahlala kulo bayacikizeka; izinyamazana zeganga lezinyoni zasemoyeni kanye lenhlanzi zasolwandle kuyafa.
Saboda wannan ƙasar tana makoki, kuma dukan waɗanda suke zama a cikinta sun lalace; namun jeji da tsuntsayen sararin sama da kuma kifin teku suna mutuwa.
4 Kodwa akungabi lamuntu omangalayo, akungabi lomuntu owethesa omunye icala ngoba abantu bakho bafana lalabo abamangalela umphristi.
“Amma kada wani mutum yă kawo tuhuma, kada wani mutum yă zargi wani, gama mutanenka suna kama da waɗanda suke kawo tuhume-tuhume a kan firist ne.
5 Liyakhubeka emini lebusuku, labaphrofethi bakhubeka kanye lani. Ngakho unyoko ngizamchitha,
Kuna tuntuɓe dare da rana, annabawa ma suna tuntuɓe tare da ku. Saboda haka zan hallaka mahaifiyarku,
6 abantu bami bachithwa yikungabi lolwazi. Njengoba likwalile ukwazi, lami ngiyalala njengabaphristi bami; ngoba kaliwunakanga umthetho kaNkulunkulu wenu, lami angiyikubanaka abantwana benu.
mutanena suna hallaka saboda jahilci. “Domin kun ƙi neman sani, ni ma na ƙi ku a matsayin firistocina; domin kun ƙyale dokar Allahnku, ni ma zan ƙyale’ya’yanku.
7 Ngokwanda kwabaphristi, kwanda kanjalo lokona kwabo kimi, benanisa uDumo lwabo ngento elihlazo.
Yawan ƙaruwar firistoci, haka suke yawan zunubi a kaina; sun yi musaya Ɗaukakarsu da wani abin kunya.
8 Badla izono zabantu bami bajabuliswe yikuxhwala kwabo.
Suna ciyar da kansu a kan zunuban mutanena suna kuma haɗamar muguntarsu.
9 Njalo kuzakuba kanje: Njengabantu, njengabaphristi. Bonke ngizabajezisela izindlela zabo, ngiphindisele kubo lezenzo zabo.
Zai kuwa zama, kamar yadda mutane suke, haka firistoci suke. Zan hukunta dukansu saboda al’amuransu in kuma sāka musu saboda ayyukansu.
10 Bazakudla kodwa bangasuthi; bazakwenza ubufebe kodwa bangandi, ngoba bamdelile uThixo ukuba bazinikele
“Za su ci amma ba za su ƙoshi ba; za su shiga karuwanci amma ba za su ƙaru ba, gama sun rabu da Ubangiji don su ba da kansu
11 ebufebeni, lewayini elidala kanye lelitsha elisusa ukuqedisisa kwabantu bami.
ga karuwanci, ga tsoho da kuma sabon ruwan inabi, waɗanda suka ɗauke ganewar mutanena.
12 Badinga izeluleko esithombeni sesigodo baphendulwe yiluthi lwesigodo. Umoya wobufebe uyabedukisa; kabathembekanga kuNkulunkulu wabo.
Sun nemi shawarar gunkin da aka yi da itace suka kuwa sami amsa daga sanda. Halin karuwanci yakan ɓad da su; sun yi rashin aminci ga Allahnsu.
13 Banikela imihlatshelo ezingqongweni zezintaba batshise iminikelo phezu kwamaqaqa, ngaphansi komʼokhi, lomphophila kanye lomtherebhinti, lapho okulomthunzi omnandi. Ngakho amadodakazi enu enza ubuwule, labomalukazana benu benze ubufebe.
Suna miƙa hadaya a kan ƙwanƙolin duwatsu suna kuma ƙone hadayu a kan tuddai, a ƙarƙashin itatuwa oak, aduruku da katambiri, inda inuwa take da daɗi. Saboda haka’ya’yanku mata suka juya wa karuwanci surukanku mata kuma suka shiga yin zina.
14 Angiyikuwajezisa amadodakazi enu lapho esenza ubuwule loba omalukazana benu lapho besenza ubufebe, ngoba amadoda uqobo azwana lezifebe anikele imihlatshelo lezifebe ezisezindaweni zokukhonzela abantu abangelakuqedisisa bazabhubha.
“Ba zan hukunta’ya’yanku mata sa’ad da suka juya ga yin karuwanci ba, balle surukanku mata, sa’ad da suka yi zina, gama mazan da kansu suna ma’amala da karuwai suna kuma miƙa hadaya tare da karuwai na masujada, mutane marasa ganewa za su lalace!
15 Lanxa ufeba, we Israyeli, uJuda kangabi lecala. Lingayi eGiligali; lingayi eBhethi-Aveni. Njalo lingafungi lisithi, ‘Ngeqiniso njengoba uThixo ekhona!’
“Ko da yake kun yi zina, ya Isra’ila, kada Yahuda ya yi laifi. “Kada ku tafi Gilgal; kada ku haura zuwa Bet-Awen. Kuma kada ku rantse cewa, ‘Muddin Ubangiji yana a raye!’
16 Abako-Israyeli bayiziqholo, njengethokazi eliyisiqholo. Pho uThixo angabelusela njani emadlelweni njengezimvu na?
Isra’ilawa masu taurinkai ne, kamar karsana mai taurinkai. Yaya Ubangiji zai iya kiwonsu kamar tumaki a makiyaya mai ɗanyar ciyawa?
17 U-Efrayimi uhlangene lezithombe; myekeleni enjalo!
Efraim ya haɗa kai da gumaka; ku ƙyale shi kurum!
18 Lalapho okunathwayo kwabo sekuphelile, bayaqhubeka ngobufebe babo; ababusi babo bazithanda kakhulu izindlela ezilihlazo.
Ko ma sa’ad da abin shansu ya ƙare, sai suka ci gaba da karuwancinsu; masu mulkinsu suna ƙaunar abin kunya.
19 Isavunguzane sizabakhukhula, lemihlatshelo yabo izabalethela ihlazo.”
Guguwa za tă share su, hadayunsu kuma za su jawo musu abin kunya.