< UHagayi 1 >

1 Ngomnyaka wesibili wenkosi uDariyu, ngosuku lokuqala lwenyanga yesithupha, ilizwi likaThixo lafika ngomphrofethi uHagayi lisiya kuZerubhabheli, indodana kaSheyalithiyeli, umbusi wakoJuda, lakuJoshuwa, indodana kaJozadaki, umphristi omkhulu:
A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus, a rana ta fari ga watan shida, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai zuwa ga Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, gwamnan Yahuda, da kuma Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
2 Nanku okutshiwo nguThixo uSomandla: “Abantu laba bathi, ‘Isikhathi sokwakha indlu kaThixo kasikafiki.’”
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’”
3 Ngakho ilizwi likaThixo lafika ngomphrofethi uHagayi lisithi:
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
4 “Kuyisikhathi senu lina ngokwenu ukuba lihlale ezindlini zenu ezinhle, kodwa indlu le ilokhu ilunxiwa na?”
“Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
5 Khathesi nanku okutshiwo nguThixo uSomandla: “Cabangani kuhle ngezindlela zenu.
To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
6 Lihlanyele okunengi kodwa livuna okulutshwana. Liyadla, kodwa kalisuthi. Liyanatha, kodwa kalikholwa. Liyagqoka izigqoko, kodwa kalifudumali. Lihola imiholo liyifake esikhwameni esivuzayo.”
Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
7 Nanku okutshiwo nguThixo uSomandla: “Cabangani kuhle ngezindlela zenu.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
8 Khwelani ezintabeni lehlise izigodo lakhe indlu ukuze ngithokoze ngayo njalo ngidunyiswe,” kutsho uThixo.
Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
9 “Kade lilindele okunengi, kodwa khangelani, kusuke kwaba yingcosana. Elikulethe ekhaya, mina ngikuphephulele khatshana. Kungani na?” kutsho uThixo uSomandla. “Kungenxa yendlu yami elokhu ilunxiwa, ngesikhathi lina, omunye lomunye wenu, ebambeke ngendlu yakhe.
“Ga shi, kukan sa rai za ku sami da yawa, amma sai ku ga kun sami kaɗan. Ɗan kaɗan ɗin ma da kukan kawo gida, nakan hura shi yă tafi. Me ya sa yake faruwa haka?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Saboda gidana da yake zaman kango, yayinda kowannenku yana faman gina gidansa.
10 Ngakho-ke, ngenxa yenu amazulu asegodle amazolo lomhlaba amabele.
Shi ya sa, saboda ku sammai sun ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.
11 Ngilethe ukoma emasimini lasezintabeni, emabeleni, ewayinini elitsha, emafutheni lakukho konke okuvela emhlabathini, ebantwini lasenkomeni kanye lasemsebenzini wezandla zenu.”
Na kawo fări a ƙasar, da a kan duwatsu, da a kan hatsi, da a kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da a kan mutane, da a kan dabbobi da kuma a kan wahalar hannuwanku.”
12 Lapho-ke uZerubhabheli, indodana kaSheyalithiyeli, loJoshuwa, indodana kaJozadaki, umphristi omkhulu lensalela yonke yabantu balilalela ilizwi likaThixo uNkulunkulu wabo kanye lombiko kaHagayi umphrofethi ngoba wayethunywe nguThixo uNkulunkulu wabo. Abantu bamesaba uThixo.
Sa’an nan sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, wanda yake babban firist, da kuma dukan raguwar jama’ar suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu da kuma saƙon annabi Haggai, domin Ubangiji Allahnsu ne ya aiko shi. Mutane kuwa suka ji tsoron Ubangiji.
13 Emva kwalokho, uHagayi isithunywa sikaThixo, wanika abantu ilizwi likaThixo leli: “Ngilani,” kutsho uThixo.
Sai Haggai, ɗan saƙon Ubangiji, ya ba da wannan saƙo na Ubangiji ga mutane cewa, “Ina tare da ku” in ji Ubangiji.
14 Ngakho uThixo waqubula umoya kaZerubhabheli indodana kaSheyalithiyeli, umbusi wakoJuda, lomoya kaJoshuwa indodana kaJozadaki, umphristi omkhulu, lomoya wensalela yabantu. Beza baqalisa ukusebenza endlini kaThixo uSomandla uNkulunkulu wabo,
Saboda haka Ubangiji ya motsa zuciyar Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, wanda yake gwamna a Yahuda, da kuma zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma zukatan dukan raguwar jama’ar. Suka zo suka fara aiki a gidan Ubangiji Maɗaukaki, Allahnsu,
15 ngosuku lwamatshumi amabili lane lwenyanga yesithupha ngomnyaka wesibili wenkosi uDariyu.
a ranar ashirin da huɗu ga watan shida. A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus,

< UHagayi 1 >