< UmTshumayeli 11 >
1 Phosela isinkwa sakho phezu kwamanzi, ngoba ngemva kwensuku ezinengi uzasifumana futhi.
Ka jefa burodinka a bisa ruwaye, gama bayan kwanaki masu yawa, za ka sāke samunsa.
2 Yabela abayisikhombisa, yebo abayisificaminwembili, ngoba kawuwazi umonakalo ongehlela elizweni.
Ka raba abin hannunka ga mutum bakwai, I, har ma takwas, gama ba ka san bala’in da zai auko wa ƙasar ba.
3 Nxa amayezi ethwele, anisa izulu emhlabathini. Aluba isihlahla singawela eningizimu loba enhla, silala khonapho esiwele khona.
In gizagizai sun cika da ruwa, sukan zub da ruwan sama bisa duniya. Itace ya fāɗi, ko wajen kudu ne, ko wajen arewa, inda ya fāɗi a nan zai kwanta.
4 Lowo onanzelela umoya kayikuhlanyela; lowo okhangela amayezi akazukuvuna.
Duk mai la’akari da iska, ba zai yi shuka ba, mai la’akari da gizagizai kuma, ba zai yi girbi ba.
5 Njengoba ungayazi indlela yomoya, loba ukubunjwa komzimba esiswini sikanina, yikho ungeke uzwisise umsebenzi kaNkulunkulu, uMenzi wezinto zonke.
Kamar yadda ba ka san hanyar iska ba, ko yadda aka siffanta jiki a cikin mahaifiya, haka ba za ka fahimci aikin Allah Mahaliccin dukan abubuwa ba.
6 Hlanyela inhlanyelo yakho ekuseni, kuthi ntambama uphumuze izandla zakho, ngoba kawukwazi okuzaphumelela, kumbe yilokhu loba yilokhuyana, langabe kokubili kuzalunga ngokufananayo.
Ka shuka irinka da safe, da yamma kuma kada ka janye hannunka, gama ba ka san wanda zai yi albarka ba, ko wannan ko wancan, ko kuma duka biyunsu su yi albarka.
7 Ukukhanya kumnandi, njalo kuhle emehlweni ukubona ilanga.
Haske da yana da kyau, abu mai kyau ne kuma idanu su dubi rana.
8 Umuntu angaze aphile iminyaka emingaki, kayikholise yonke. Kodwa makakhumbule insuku zobumnyama, ngoba zizabe zizinengi. Konke okuzakuza kuyize.
Kome tsawon rayuwar mutum, bari yă more su duka. Amma bari kuma yă tuna da kwanakin duhu, gama su ma za su yi yawa. Duk abin da zai faru ba shi da amfani.
9 Jabula nsizwa usesemutsha, uvumele inhliziyo yakho ikuthokozise ensukwini zobutsha bakho. Landela izindlela zenhliziyo yakho lakho konke amehlo akho akubonayo, kodwa yazi ukuthi ngenxa yazo zonke lezizinto uNkulunkulu uzakumisa ekwahlulelweni.
Ka yi murna, kai matashi, a ƙuruciyarka, bari zuciyarka kuma tă yi farin ciki a kwanakin ƙuruciyarka. Ka bi shawarar zuciyarka da kuma duk abin da idanunka suka gani, amma ka sani fa, cikin dukan al’amuran nan Allah zai shari’anta ka.
10 Ngakho-ke, susa ukukhathazeka enhliziyweni yakho ulahlele kude inhlupheko zomzimba wakho, ngoba ubutsha lamadlabuzane kuyize.
Saboda haka, ka fid da tsoro daga zuciyarka ka kakkaɓe duk wani abin da ya dami rayuwarka, gama ƙuruciya da ƙarfi ba su da amfani.