< UDanyeli 1 >

1 Ngomnyaka wesithathu wokubusa kukaJehoyakhimi inkosi yakwaJuda, uNebhukhadineza inkosi yaseBhabhiloni wafika eJerusalema walihanqa.
A Shekara ta uku ta mulki Yehohiyakim sarkin Yahuda, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zo Urushalima ya kuma yi mata ƙawanya.
2 UThixo wanikela uJehoyakhimi inkosi yakwaJuda ezandleni zakhe, kanye lezinye impahla zethempeli likaNkulunkulu. Konke wakuthwala wakusa ethempelini likankulunkulu wakhe eBhabhiloniya wakufaka endlini yenotho kankulunkulu wakhe.
Sai Ubangiji ya bashe Yehohiyakim sarkin Yahuda a hannunsa, tare da waɗansu kayayyakin haikalin Allah. Ya ɗauki waɗannan kayan zuwa cikin haikalin allahnsa a Babilon cikin ma’ajin gidan allahnsa.
3 Kwathi-ke inkosi yasilaya u-Ashiphenazi, induna yezikhulu zesigodlo sayo ukuthi alethe abanye bama-Israyeli besikhosini lasezikhulwini,
Sa’an nan sarkin ya umarci Ashfenaz, shugaban fadarsa yă kawo waɗansu daga cikin Isra’ilawan da suka fito daga gidan sarauta da kuma na fitattun mutane.
4 amajaha amizimba ingelasici, amahle, atshengisa ukufundiseka ezintweni zonke, azi okunengi, aphangisayo ukuzwisisa njalo abonakala efanele ukukhonza esigodlweni senkosi. Ayemele awafundise ulimi lezincwadi zamaBhabhiloni.
Matasa maza waɗanda ba su da wata naƙasa kuma kyawawa, hazikai ta kowace hanyar koyo, sanannu, masu saurin fahimtar abu, da kuma waɗanda suka cancanci su yi aiki a fadar sarki. Zai koya musu harshen Babiloniyawa da kuma littattafansu.
5 Inkosi yababela ukudla okukhethiweyo okwansuku zonke kanye lewayini kuthathwa kokwakulungiselwe inkosi. Babezafundiswa okweminyaka emithathu, kuthi ngemva kwalokho baqalise ukusebenza esigodlweni.
Sarki kuma ya sa a ba su abinci da ruwan inabi kowace rana daga cikin abincin sarki. Za a koyar da su har shekaru uku, bayan haka kuma su shiga yin wa sarki hidima.
6 Phakathi kwalabo babekhona ababephuma koJuda: uDanyeli, loHananiya, loMishayeli kanye lo-Azariya.
Daga cikin waɗannan da aka zaɓa akwai waɗansu daga Yahuda, Daniyel, Hananiya, Mishayel da kuma Azariya.
7 Indunankulu yabanika amabizo amatsha: uDanyeli kwathiwa nguBhelitheshazari; uHananiya waba nguShadreki, uMishayeli waba nguMeshaki; u-Azariya waba ngu-Abhediniko.
Sai sarkin fada ya raɗa musu sababbin sunaye, ga Daniyel ya raɗa masa Belteshazar; ga Hananiya ya raɗa masa Shadrak; ga Mishayel ya raɗa masa Meshak; ga Azariya kuma ya raɗa masa Abednego.
8 Kodwa uDanyeli wazimisela ukuthi angazingcolisi ngokudla kwesikhosini lewayini lakhona, yikho wasecela kundunankulu imvumo yokuthi angazingcolisi kanjalo.
Amma Daniyel ya ƙudura a zuciyarsa ba zai ƙazantar da kansa da abinci da ruwan inabin sarki ba, sai ya tambayi sarkin fada don a ba shi izinin kada yă ƙazantar da kansa ta wannan hanya.
9 UNkulunkulu wayekwenzile ukuthi Indunankulu imthande njalo imhawukele uDanyeli,
Sai Allah ya sa sarkin fada ya nuna masa tagomashi ya kuma ƙaunaci Daniyel,
10 kodwa wathi kuDanyeli, “Ngiyamesaba umhlekazi wami inkosi, onguye okumisileyo ukudla kwenu lokokunatha. Kambe akayikulibona yini selikhangeleka kubi kulamanye amajaha angontanga benu? Inkosi ingahle ingiqume ikhanda ngenxa yenu.”
amma sai sarkin fada ya ce wa Daniyel, “Ina jin tsoron ranka yă daɗe, sarkina wanda ya sa a ba ku abinci da ruwan inabi. Me zai sa yă ga kuna ramewa fiye da sauran samari, tsaranku? Sarki zai sa a fille mini kai saboda ku.”
11 UDanyeli wasesithi enxuseni elalibekwe yindunankulu phezu kwaboDanyeli, loHananiya, loMishayeli lo-Azariya,
Sai Daniyel ya ce wa mai gadi wanda sarkin fada ya sa yă kula da Daniyel, Hananiya, Mishayel da Azariya,
12 “Ake uzilinge izinceku zakho okwensuku ezilitshumi nje: Ungasiphi lutho ngaphandle kwemibhida ukuba sidle yona lamanzi okunatha.
“Ina roƙonka ka gwada bayinka kwana goma. Kada ka ba mu kome sai kayan lambu mu ci da kuma baƙin ruwa mu sha.
13 Lapho-ke ubusufananisa imizimba yethu laleyo eyamajaha adla ukudla kwesikhosini, ubususenza njengokubona kwakho ezincekwini zakho.”
Sa’an nan sai ka dubi fuskokinmu da na sauran samarin da suke ci daga abincin sarki; sa’an nan ka yi da bayinka bisa ga abin da ka gani.”
14 Lakanye inxusa lakuvuma lokho labalinga okwensuku ezilitshumi.
Sai ya amince da haka ya kuma gwada su har kwana goma.
15 Ekupheleni kwensuku ezilitshumi bakhangeleka bephila ngcono njalo bezimukile kulamajaha ayesidla ukudla kwesikhosini.
A ƙarshen kwana goma sai aka ga fuskokinsu suna sheƙi, sun kuma yi ƙiba fiye da samarin da suke cin abinci irin na sarki.
16 Yikho inxusa laselisusa ukudla kwabo kwekhethelo kanye lewayini ababelinatha labapha imibhida.
Sai mai gadinsu ya janye abinci da ruwan inabi irin na sarki, ya ci gaba da ba su kayan lambu.
17 La amajaha amane uNkulunkulu wawanika ulwazi lokuzwisisa zonke izibhalo lemfundo. Njalo uDanyeli wayezwisisa imibono lamaphupho wonke ehlukeneyo.
Ga samarin nan guda huɗu Allah ya ba su sani da ganewar dukan irin littattafai da kuma koyarwa. Daniyel kuma ya iya gane wahayi da kowane irin mafarki.
18 Ekupheleni kwesikhathi esasibekwe yinkosi ukuthi balethwe, indunankulu yabethula kuNebhukhadineza.
A ƙarshen lokacin da sarki ya sa da za a kawo su ciki, sai sarkin fada ya gabatar da su ga Nebukadnezzar.
19 Inkosi yakhuluma labo yafumana engekho olingana loDanyeli, loHananiya, loMishayeli kanye lo-Azariya; ngakho bangeniswa ukusebenzela inkosi.
Sarki kuwa ya yi magana da su, sai ya gano cewa babu wani kamar Daniyel, Hananiya, Mishayel da kuma Azariya; don haka sai suka shiga yi wa sarki hidima.
20 Kuzozonke izindaba zokuhlakanipha lokuzwisisa inkosi eyababuza ngazo yabafumana bebedlula bonke omasalamusi lezangoma ngokuphindwe katshumi kuwo wonke umbuso wayo.
A dukan al’amuran hikima da na fahimta wanda sarki ya tambaye su, ya tarar sun fi dukan masu sihiri da bokaye waɗanda suke cikin mulkinsa sau goma.
21 UDanyeli wahlala khona kwaze kwaba ngumnyaka wokuqala weNkosi uKhurosi.
Daniyel kuwa ya kasance a nan har shekara ta farko ta mulkin sarki Sairus.

< UDanyeli 1 >