< KwabaseKholose 2 >
1 Ngifuna ukuba lazi ukuthi ngilizamela kakhulu okunganani lina labaseLodikheya, kanye labo bonke abangakangiboni mathupha.
Ina so ku san irin famar da nake yi saboda ku da kuma waɗanda suke a Lawodiseya, da kuma saboda dukan waɗanda ba su taɓa ganina ido da ido ba.
2 Injongo yami yikuthi bakhuthazeke ezinhliziyweni njalo bamanyane ethandweni ukuze babe lenotho egcweleyo yokuqedisisa okupheleleyo, ukuze bayazi imfihlakalo kaNkulunkulu kubalisa uKhristu,
Manufata ita ce a ƙarfafa su su kuma zama ɗaya a cikin ƙauna. Ina so su kasance da cikakken ƙarfin hali domin suna da cikakken fahimtar asirin Allah, wato, Kiristi kansa,
3 okufihlwe kuye yonke ingcebo yokuhlakanipha lokwazi.
a cikinsa ne aka ɓoye dukkan dukiya ta hikima da ta sani.
4 Ngilitshela lokhu ukuze kungabikhona olikhohlisayo ngamazwi amnandi.
Ina faɗa muku wannan ne don kada wani yă ruɗe ku da daɗin baki.
5 Ngoba lanxa ngingekho kini ngomzimba ngilani ngomoya njalo ngithokozela ukubona ubuntu benu lokuqina kokholo lwenu kuKhristu.
Gama ko da yake ba na nan tare da ku a cikin jiki, ina tunaninku kullum, ina kuma farin ciki da gani kuna rayuwa yadda ya kamata, kuna kuma dāgewarku a kan bangaskiyarku a cikin Kiristi.
6 Ngakho-ke, njengoba uKhristu Jesu lamamukela njengeNkosi, qhubekani liphila kuye,
To, da yake kun karɓi Kiristi Yesu a matsayin Ubangiji, sai ku ci gaba da rayuwa a cikinsa,
7 ligxile njalo lakhelwe kuye, liqine ekukholweni njengokufundiswa kwenu, liphuphuma ngokubonga.
ku tsaya daram ku kuma ginu a cikinsa, ku sami ƙarfafawa a cikin bangaskiya kamar yadda aka koya muku, kuna kuma cike da godiya.
8 Qaphelani kungabikhona olithumbayo ngenhlakanipho eyize lekhohlisayo, eyeyame emdabukweni wabantu lakuzimiso zemvelo yakulo umhlaba kungesikho kuKhristu.
Ku lura kada wani yă ruɗe ku da ilimin banza da wofi. Wannan koyarwa ta mutane ce kawai. Ta fito daga ikokin wannan duniya ne ba daga Kiristi ba.
9 Ngoba bonke ubuNkulunkulu buhlezi kuKhristu ngesimo somzimba
Gama a cikin Kiristi cikin jiki dukkan cikar Allahntaka take tabbata,
10 njalo lina lilakho lokhu kuphelela kuKhristu oyinhloko yamandla wonke kanye lokubusa konke.
an kuma mai da ku cikakku a cikin Kiristi, wanda yake shi ne kai a kan kowane iko da kuma hukuma.
11 Lasokelwa kuye ngokususwa kwemvelo yenu yesono, kungayisikho ngokusoka okwenziwa ngezandla zabantu kodwa ngokulahla umzimba wenyama, lokhu kuyikusoka okwenziwa nguKhristu
A cikinsa ne kuma aka yi muku kaciya, ba kuwa yin mutum ba, amma wadda Kiristi ya yi muku, ta wurin tuɓe halinku na mutuntaka.
12 ngokungcwatshwa laye ngobhaphathizo labuye lavuswa kanye laye ngokukholwa kwenu emandleni kaNkulunkulu owamvusa kwabafileyo.
Da yake an binne ku tare da shi cikin baftisma haka kuma aka tashe ku tare da shi ta wurin bangaskiyarku a cikin ikon Allah, wanda ya tashe shi daga matattu.
13 Ngesikhathi lifile ezonweni zenu lokungasoki kwemvelo yenu yesono, uNkulunkulu walenza laba ngabaphilayo kanye loKhristu. Wasithethelela zonke izono zethu
Kun zama matattu saboda ku masu zunubi ne kuma saboda halin zunubanku aka ware. Sa’an nan Allah ya sa kuka rayu tare da Kiristi. Ya gafarta mana dukan zunubanmu.
14 ngokwesula yonke imithetho elotshiweyo lezimiso zayo eyayimelane lathi njalo isivimbela. Wayisusa, wayibethela esiphambanweni.
Ya soke rubutacciyar doka tare da ƙa’idodinta, wadda take gāba da mu, take kuma hamayya da mu; ya kuma kawar da ta, ya kafe ta a kan gicciye.
15 Kwathi eselahlise imibuso lababusi izikhali, wenza umbukiso oyinhlekisa ngabo, wabanqoba ngesiphambano.
Bayan ya ƙwace makaman ikoki da hukumomi, ya kunyata su a sarari, ya ci nasara a bisansu ta wurin gicciye.
16 Ngakho-ke, lingavumeli umuntu elahlulela ngalokho elikudlayo loba elikunathayo loba ngokuphathelane lomkhosi wokholo, ukuthokozela ukuthwasa kwenyanga loba usuku lweSabatha.
Saboda haka kada ku bar wani yă shari’anta ku a kan abin da kuke ci ko sha, ko bisa ga abin da ya shafi wani bikin addini, ko Bikin Sabon Wata ko na ranar Asabbaci.
17 Lezizinto ziyisithunzi nje sezinto ezazizakuza kodwa ubuqotho butholakala kuKhristu.
Waɗannan su ne hoton abubuwan da za su zo; amma Kiristi ne ainihinsu.
18 Lingavumeli umuntu othokoziswa yikuzithoba kwamanga lokukhonza izingilosi eliphuthisa umvuzo wenu. Umuntu onjalo ubalisa ngokupheleleyo konke akubonileyo, kuthi ingqondo yakhe engayisiyo yomoya imkhukhumeze ngemicabango eyize.
Kada ku yarda wani yă ɓata ku, cewa shi wani abu ne don yă ga wahayi. Irin mutumin nan yakan nuna ƙasƙancin kai na ƙarya, yă kuma ce yana yi wa mala’iku sujada. Irin mutumin nan yana kumbura kansa ba dalili, sai son zuciya irin na halin mutuntaka.
19 Usehlukane lenhloko yomzimba wonke wona ohlanganiswa ndawonye yimisipha lemithambo, okhula ngokuthanda kukaNkulunkulu.
Ya yanke dangantaka da Kiristi wanda yake kai, wanda ta gare shi ne dukan jiki yake a haɗe, yake tsaye ta wurin taimakon gaɓoɓi da jijiyoyi, yana kuma girma kamar yadda Allah yake sa yă yi girma.
20 Njengoba lafa loKhristu ezimisweni zalo umhlaba, kungani liphila sengathi lilokhu lingabawo, lizibeka ngaphansi kwemithetho yawo yokuthi,
Kun mutu tare da Kiristi. Yanzu ƙa’idodin wannan duniya ba su da iko a kanku. Don me kuke zama har yanzu kamar ku nasu ne? Kuna biyayya da umarnansu cewa,
21 “Ungabambi! Unganambithi! Ungathinti!”?
“Kada ka kama! Kada ka ɗanɗana! Kada ka taɓa”?
22 Konke lokhu kumiselwe ukuqedwa yikusetshenziswa ngoba kweyame phezu kwemilayo yabantu lemfundiso yabo.
Irin waɗannan dokoki suna magana a kan abubuwan da ba sa daɗewa. Su ayyukan mutane ne, sun kuma fito daga koyarwar mutane.
23 Impela izimiso ezinje zibonakala njengenhlakanipho, ngenkonzo yazo yokuzenzela, ukuzithoba kwamanga lokuphatha umzimba kabuhlungu kodwa kazilalo usizo lokuzithiba ezinkanukweni zomzimba.
Yin biyayya da irin waɗannan ƙa’idodi za su yi kamar su ne abu mafi kyau da za a yi. Sukan yi kamar suna sa a ƙaunaci Allah sosai a kuma kasance da sauƙinkai a kuma kasance da kamunkai. Amma ba su da wani iko a kan sha’awace-sha’awacenmu.