< 1 Imilando 10 >

1 AmaFilistiya alwa lo-Israyeli; abako-Israyeli babaleka, njalo abanengi bafela eNtabeni yase Gilibhowa.
To, fa, Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra’ilawa; Isra’ilawa kuwa suka gudu a gabansu, da yawa kuma suka mutu a kan Dutsen Gilbowa.
2 AmaFilistiya axotshana kanzima loSawuli kanye lamadodana akhe, abulala amadodana akhe uJonathani, lo-Abhinadabi kanye loMalikhi-Shuwa.
Filistiyawa suka matsa sosai suna bin Shawulu da’ya’yansa maza, suka kuma kashe’ya’yansa maza Yonatan, Abinadab da Malki-Shuwa.
3 Impi yatshisa macele wonke kuSawuli, njalo kwathi abatshoki bemitshoko sebemxhumile, bamlimaza.
Yaƙin ya yi tsanani kewaye da Shawulu, kuma sa’ad da maharba suka rutsa shi, sai suka ji masa rauni.
4 USawuli wathi kumthwali wezikhali zakhe, “Hwatsha inkemba yakho ungigwaze, hlezi abantu laba abangasokanga bafike bangigwaze bangenze ihlazo.” Kodwa umphathi wezikhali zakhe wesaba, akaze akwenza lokho, ngakho uSawuli wathatha inkemba yakhe waziwisela phezu kwayo.
Sai Shawulu ya ce wa mai riƙe masa kayan yaƙi, “Zare takobinka ka soke ni, in ba haka ba waɗannan marasa kaciya za su zo su yi mini ba’a.” Amma mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ji tsoro bai kuwa yi haka ba; saboda haka Shawulu ya zāre takobinsa ya fāɗi a kansa.
5 Kwathi umphathi wezikhali ebona ukuthi uSawuli wayesefile, laye waziwisela phezu kwenkemba yakhe, wafa.
Da mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ga Shawulu ya mutu, sai shi ma ya fāɗi a kan takobinsa ya mutu.
6 Ngakho uSawuli lamadodana akhe amathathu bafa, labo bonke abendlu yakhe bafa ndawonye.
Ta haka Shawulu da’ya’yansa maza uku suka mutu, dukan gidansa kuwa suka mutu tare.
7 Kwathi bonke abako-Israyeli ababesesigodini bebona ukuthi ibutho lalibalekile lokuthi uSawuli kanye lamadodana akhe basebefile, batshiya imizi yabo babaleka. AmaFilistiya afika ahlala kuyo.
Sa’ad da dukan Isra’ilawa a cikin kwari suka ga cewa mayaƙansu suna gudu, kuma cewa Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu, sai suka bar garuruwansu suka gudu. Filistiyawa kuwa suka zo suka zauna a cikinsu.
8 Ngelanga elalandelayo, amaFilistiya esefikile ukuba akhuthuze abafileyo, afica uSawuli lamadodana akhe befile eNtabeni yase Gilibhowa.
Kashegari, da Filistiyawa suka zo don su tuttuɓe waɗanda suka mutu, sai suka sami Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu a Dutsen Gilbowa.
9 Bamkhuthuza baze bamquma ikhanda lakhe balithatha kanye lezikhali zakhe, basebethuma izithunywa kulolonke ilizwe lamaFilistiya ukuthi zimemezele lindaba ezithombeni zabo lebantwini bakibo.
Suka tuttuɓe shi suka yanke kansa suka ɗauka duk da kayan yaƙinsa, suka kuma aika’yan aika ko’ina a ƙasar Filistiyawa, a yi shela labarin a cikin gumakansu da kuma mutanensu.
10 Abeka izikhali zakhe ethempelini labonkulunkulu babo kwathi ikhanda lakhe balibeka ethempelini likaDagoni.
Suka sa kayan yaƙinsa a haikalin allahnsu suka kuma rataye kansa a haikalin Dagon.
11 Abantu bonke baseJabheshi Giliyadi sebezwile ngokwakwenziwe ngamaFilistiya kuSawuli,
Sa’ad da mazaunan Yabesh Gileyad suka ji dukan abin da Filistiyawa suka yi wa Shawulu,
12 wonke amaqhawe alezibindi ahamba ayathatha isidumbu sikaSawuli lezamadodana akhe aya lazo eJabheshi. Basebengcwaba amathambo abo ngaphansi kwesihlahla esikhulu eJabheshi, bazila insuku eziyisikhombisa.
sai dukan jarumawa suka tafi suka ɗauki jikunan Shawulu da na’ya’yansa maza suka kawo Yabesh. Sa’an nan suka binne ƙasusuwan a ƙarƙashin babban itace oak a Yabesh, suka kuma yi azumi kwana bakwai.
13 USawuli wafa ngoba wayengathembekanga kuThixo; kaligcinanga ilizwi likaThixo wakhe waze wayadinga ukuqondiswa yizangoma,
Shawulu ya mutu domin rashin aminci ga Ubangiji; bai kiyaye maganar Ubangiji ba, ya ma nemi shawarar mace mai duba,
14 esikhundleni sokukhuleka kuThixo. Ngakho uThixo wamenza wafa wathatha ubukhosi wabunika uDavida indodana kaJese.
bai kuwa nemi nufin Ubangiji ba. Saboda haka Ubangiji ya kashe shi, ya miƙa mulkin ga Dawuda ɗan Yesse.

< 1 Imilando 10 >